Hausa Novels

Lu’u Lu’u 38

Jiki na kakkarwa Juman ta kalleshi tace” Ba wannan ba, maganar aure… Ayam da Umad…me hakan yake nufi?”

Gyara zama ya kuma yi wanda Ayam ta kalli Umad ba ko k’yabtawa tana jira ta ji me mahifinta zai fad’a, cikin nutsuwa Musail yace” Tun daga sanda ya fara shigowa rayuwarki na samu labari daga gurin masu bibiyarki ba dare ba rana, da kallon fuskarshi a allon wayata da aka turo min na san ko wanene saboda kama da yake da sarauniyar Giobarh da kuma yayanshi Urab wanda na kasa yayin neman auren mahaifiyarki, bayanan da suka biyo bayan hoton su suka tabbatar min da kokonto na, bincike na sa aka min sosai a kan ka har saida na san abubuwa uku game da kai masu mahimmancin da ba kowa ya sani a ge da kai ba, na farko shi ne musulunta da ka yi iyayenka basu sani ba, na biyu kuma shi ne aikin sirri da kake da hukunmar binciken miyagun laifuka, na uku kuma shi ne k’udirinka akan Ayam, da haka nasan ranar da ka je gidan su Habbee ka kuma nemi aurenta a wajensu.”

Da sauri Ayam tace” Pah ban gane ba? Ya nemi aurena kamar ya?”

Jinjina mata kai yayi yace” Hakane, ya nemi aurenki a wajensu, duk da ba amincewarki a ciki, amma ni na yarda da shi saboda mutumin kirki ne, zai kula da ke Ayam.”

Kallon Umad tayi d kanshi ke sadde yana wasa da yatsun hannunshi, a sanyaye ta furta” Ta ya haka ma zata faru? Bayan babu soyayya a tsakaninmu.”

Murmusawa Musail yayi yace” Zaku saba Ayam, da sannu za ki so shi, amma dai ba zan miki dole ki zauna da shi ba, dan na fi kowa sanin illar haka, akwai zuciyar da kyautatawa bata sa ta tausasa.”

Had’a ido sukayi da Juman da sauri tayi k’asa da na ta tana mai jin kunyarshi, muryar Zafreen suka ji dake tsaye tace” Duk wannan ba shi zai sa na saurara ba, ka rabani da wacce ta haife ni, sannan ita ma ta rabani da wanda na ke so.”

Ta k’arashe tana duban Ayam da ita ma ta kalleta a lokacin haka a Juman, da mamaki Juman tace” Wa ye kike sl da ta rabaki da shi haka?”

Nuna Umad tayi tace” Wannan ne.”

Kallon Umad sukayi da yayi kamar bai san suna yi ba, Juman ce tace” Amma ai ita ma bata sani ba, ki bi komai a hankali mana Zaf…”

D’aga mata hannu tayi tace” Kinga ni ba da ke nake ba, hak’uri na hak’ura da shi dole, tunda na ji ya rabata da budurcinta daren shekaran jiya, amma ku sani wallahi ba zan rasa abunda nake so ba ni kad’ai, dole dukkanmu mu rasa wani abu da muke so.”

Mik’ewa Juman tayi tana kallonta tace” Kamar ya? Me kike nufi?”

Tab’e baki tayi tace” Ina nufin dole na kashe yarinyar nan sannan na kashe shi shi ma..”

Ta k’arashe da nuna Musail, da sauri Ayam ta mik’e tsaye tana fad’in” Idan ina raye ba zaki kashe mahaifina ba, idan kuma ni zaki kasheni saboda Umad ne, to ki d’aukeshi na bar miki, ni ba wani damuna yayi ba…”

Ta k’arashe maganar da kallon gefen da Umad yake, duk da kansa a k’asa yake amma saida ya dakata da matsa hannayenshi da yake yana taune leb’ensa yana nanata kalmar *ba damuna yayi ba*.

A hankali Musail ya mik’e tsaye ya tako zuwa gaban Zafreen ya kalleta yace “…

 

*Ki garzayo ki biya na ki.*

 

*Alhamdulillah.*

The post Lu’u Lu’u 38 first appeared on 2gNovels.com.ng.

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button