Lu’u Lu’u 40

Juyawa yayi ya fice a wurin duk da yanda take k’wala masa kira tana ya yafe mata kar su d’aureta, ba za ta iya rayuwa a d’aure ba wa ye wa ye, haka yana fitowa jami’an dake nan wanda duk suka ji tattaunawarsu suka dinga sara masa wasu kuma na bashi hannu, shugabar hukumar kan shi hannu ya bashi suka gaisa bayan ya share k’walarshi yace “Nagode Umad, yau ta dalilinka na gano wanda suka kashe min mahaifina, atisayen *lu’u lu’u* ya zo k’arshe.”
Murmusawa yayi yana mai danne k’unar dake cikin zuciyarshi na rasa yayanshi yace “Nagode yallab’ai, ina neman wata alfarma?”
Da fara’a dattijon yace “Ba komai, fad’i buk’atarka.”
Kan shi tsaye yace “Ina so zan d’auki hutu.”
Dariya yayi ya bubbuga kafad’arshi yace “Ai ko baka nema ba, abu ne da muka tanada maka tun kafin zuwan ranar nan.”
Jinjina kai yayi yace “Nagode yallab’ai.”
Girgiza kai yayi yace “Ba komai Umad….am…yarima Umad, zuwa dare zaga ka takardar izinin hutunka a e-mail d’inka.”
Jinjina kai yayi sannan ya ciro bindigarshi ya aje akan d’an teburin dake kusa, da mamaki dattijon yace “Baka buk’atarta daga yanzu kenan?”
Murmushi yayi yace “Hutu zan yi yallab’ai, da kuma cin…amarci, ba karan batta ba.”
Bushewa duk wurin sukayi da dariya har wasu na tsokanarsa dama yana da aure ne, abu d’aya ya fad’a musu shi ne “Ina gayyatarku dukanku wajen shagalin biki na a fadar Khazira.”
Daga haka ya juya ya fita a gaba d’aya headquarters duk da yana jin tsiyar da wasu ke masa wai hala yar sarki ya kwashe? Wasu kuma suna fad’in ko dai ma *lu’u lu’un* atisayen na su ya d’auke kacokam.
馃グ *Mu sha kodumo, In Shaa Allah gobe za ku ji ni shiru saboda zamu yi tafiya amma ta wuni d’aya zuwa Katsina, ina baran addu’arku guy’s.*
*Alhamdulillah.*
[ad_2]