MADADI Page 41 to 50

Yace.”Haba baby nifa jikina yayi sanyi wallahi bana tsammanin za’a samu budurci a tare dake nafi kowa sanin waye Kawu Abbas a fagen son mata kullum a gabana shida abokansa na kasuwa suke siyan magungunan karfi domin saduwa da iyali na tabbatar da ba zai zuba miki ido yana kallonki ba.
Naja’atu gabanta na faduwa tace”Wallahi ka daina wannan maganar ni har yanzu budurwa ce to har yaushe ma akayi auran da wata mu’alama zata faru a tsakanimu na fada maka fa kai zan mallakawa komai nawa to me zai sanya ka dinga wannan maganar.” …murmushi yayi yana sake sosa sajensa cikin shakiyanci yace. Amma dai nasan ko baiyi mai gabad’aya ba yana rungumeki ko.”? Da sauri ta sunkuyar da kanta tace”Dan Allah ka daina wannan maganar bana so.” Salim yace.”Shikkenan tunda bakya so na daina ina nan ina jira ki cika min al’kawarina ki fito ni kuma nayi miki al’kawarin auranki.”
Naja’atu siyayya tayi sosai kaya na manyan mata na kece raini manyan atampopi da lesuka da abaya gami da mayafai masu tsada da takalma da kayan make up duk abinda take bukata sai da ta dauka akwatina hud’u ta cika da kayanta sukeje gurin biya Salim ya tura musu kudin kayansu ta banki, yaran dake aiki a gurin ne suka kwashe akwatin nan suka kai mota, daf da zasu fita daga get din Sahad din Abbah Abbas din ya kira wayar Salim din, cikin girmamawa Salim ya daga wayar da fad’in “Kawu gamu nan zamu koma gida alhmdullhi na kaita ta za’bi duk wani abu da take bukata kamar yanda ka umarce ni.” Tana jin muryarsa yana cewa”To ya tabbatar da cewar ka shigar mata da kyan cikin gida.” Cike da ladabi yace.”Insha Allahu Kawu..Sunayin sallama Salim ya juyo yana kallonta yana d’an ‘bata fuska yace.”Kinji mutuminki ko sai kace wani yaronsa wai yana cewa na shigar miki da kaya cikin gida nifa wallahi mugun haushinsa nakeji ina bala’in kishinsa…..Dariya tasa tace”Kaji ka da wata magana to da meye kai idan ba yaron nasa ba, kawai kabi umarnin ubangidanka.” Yace.”Daga ranar da kika zama matata zan daina yi masa hidima yanzu inaso na cimma munufata ne a kansa shiyasa nake zama a karkashinsa.” Kallonsa ta shigayi tana mamakin wace irin munufa ce a zuciyarsa dangane da Abbah Abbas din, jikinta ne yayi sanyi cikin zuciyarta tana adduar Allah yasa munufar alkairi ce a zuciyar Salim din..Cike da hirar Abba Abbas din suka isa gidan..Salim ya shigar mata da akwatinan kayanta cikin gidan kamar yanda aka umarce shi, Halisa na ganin iyayen akwatina masu masifar tsada da daukar ido sai hankalinta ya tashi ‘kyashi da ba’kin ciki gami da kishi ya cika mata zuciyarta…………
*Littafin na kudi ne!*
Koda zaki ganshi a group na sata ne idan kina bukatar biyan kudin karatu ga yanda abin yake
Vip Gruop#600
Normal#300
Account.. 0542382124….Binta Umar gtbank…Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
*MANZIL ALWAFIR ABUJA????????????*
_*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci, magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu kowace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye akwai groups na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rigistar dasu kukanki ya kar’e idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_
Mddbhrmbn40
Naja’atu ganin yanda Halisa tayi kici kici da fuska yasa ta fasa shiga daki ta tsaya suna magana da Baba Larai inda take cewa da ita tazo taga kayan data siyo..Baba Larai na washe baki taje kusa da naja’atun suka shiga kici kicin bude kayan, Halisa kasa barin gurin tayi tana ta satar kallon kayan ta gefan idonta…Ganin irin manya manyan lesukan da Naja’atu take ta fito dasu daga akwatin ne yasa hankalinta ya tashi cikin lesukan dik babu na kasa da dubu ashirin daga na talatin sai na hamsin sun kai guda biyar ga iyayen atampopi masu kyau da tsada! Naja’atu na dariya tace”Baba wai dani za’a rainawa hankali aje a had’o min wasu banzayen kaya ace sune lefena an dauka nima ‘yar kauye ce.” Ta’karasa maganar tana dariya kana ganinta kasan tana cikin nishadi.
To kowa dai yayi zagi a kasuwa yasan da wanda yake..Halisa uffan ba tace ba ganin kayan lefen na’ja’atu yayi masifar daga mata hankali a ‘kiyasin da tayi da akwatin nan da kayan dake ciki sun kusa tassama miliyan guda..lallai ba zata yarda da wannan rashin adalcin ba tana ganin idan ya dawo itama dole ya ‘kara mata kudi akan abinda ya bata.
Baba Larai da bata san abinda ke faruwa ba tace”Aikuwa dai kaya sunyi kyau ubangiji Allah yasa ki kashe lafiya Allah kuma ya baku zaman lafiya dake da mijinki.” Domin ta sake cuzgunawa Halisa ta amsa da “ameen Baba larai nagode.” Halisa ta kalli Larai fuskarta a murtuke tace”Ya kamata ki tashi haka ki shiga kicin yamma tanayi.” Baba Larai na ‘yar dariya ta mike da fad’in “Na tsaya kallon kaya ne Hajiya to bari na shiga kicin din.”
Halisa ta bita da kallon banza tana jan tsaki haushin matar take ji ganin kamar tasu tazo daya da naja’atu ita duk wanda zaiyi muamular arziki da yarinyar ba kaunarsa take ba.
Naja’atu tana gyara kayanta cikin akwatin tana wa’kokinta tanayi tana satar kallon halisan dan duk abinda takeyi a tsorace take tana jin tsoron kada aljanunta su tashi ta maketa a gurin amma saboda neman fitina bata fasa sakar mata da habaici ba….Halisa ta kalleta tana murmushin mugunta tace”Duk wannan rawar kan da kikeyi zaki daina ne a tafin hannuna kike wallahi ni naso ki zauna a gidan nan da banso zamanki a cikinsa ba da tuni kin dade a gidanku amma kinyi da ‘yar halak wallahi sai na nuna miki ke ‘karamar mara kunya ce.”
A nutse ta kalleta kamar babu wani ‘kulli a zuciyarta tace”Ikon Allah to me nayi miki da kike wannan maganar naga tunda na shigo ban ambaci sunanki ba ballantana nayi miki rashin kunyar da kike magana a kanta, kinga aunty Halisa bana son neman rigima dan Allah ki zauna a matsayinki na zauna a nawa.”
Halisa tace”Sharrina yafi kala dubu kuma wallahi sai bukatata ta biya a kanki.” Wannan magana ta fad’e ta ne a lokacin da baba larai ta fito daga kicin kuma taji da kunanta…Tace”Subahanallahi duk me ya jawo wannan maganar Hajiya.”
Naja’atu tayi saurin fadin “Baba kin daiji da kunanki ko? gashinan da bakinta tana fad’in cewar sai ta cutar dani to ni ban dogara da kowa ba sai da Allah na dogara kuma babu abinda mutum ya isa yayi min komai tsafinsa da asirinsa.
Baba Tace” Haba naja’atu ki daina fad’ar wannan maganar kinji ko itama hajiyan bacin rai ne yasa ta fadi haka, Yau kwanana hudu a gidan nan amma na fahimci babu jituwa a tsakaninku dan Allah kuyi hakuri ku zauna lafiya da junanku ku daina ikirarin zaku cutar da junanku…Halisa ba tace komai ba ta bar gurin…Naja’atu ta kalli Baba Larai da fadin”Baba wannan matar bata da kirki ga hassadar tsiya wai fa ganin wad’an nan kayan ne yasa ta take wannan maganar kina dai kallo tunda na shigo gidan banyi mata magana ba.”
Larai tace”Ina kallo wallahi itace babba amma kuma wani sa’in itace ke tada husuma a tsakaninku ke kuma baki da hakuri ki dinga biye mata kuna tada hankalin maigidanku dan Allah ku daina abinda kukeyi ku zauna lafiya.