MADADI Page 41 to 50

Yana fita daga dakin nata ta dauki wayarta cike da tsantsar farin ciki ta kira Ramlatu ta fada mata cewar aiki yayi! tafada mata kyautar kudin da yayi mata da kuma maganar zuwa umarar da zasuyi.
Yaya Ramlatu tace”To alhamdullihi haka muke sai dai kuma baki fada min tsakaninsa da tsinanniyar yarinyar nan ba.
Halisa tace”Ai tunda naga sun kwana tare da ita washe gari yana min rawar jiki na gane bai samu biyan bukata ba a gurinta amma dai duk da haka zansa musu ido sosai na gani domin na gane halin da suke ciki.
Ya Ramltu tace”To shikkenan sai naga tukwicina ko.” Halisa tayi dariya da fadin”Ba ke kadai ba ma har *Yar shagamu* zan muku kyauta ta mussaman dama ni babban burina na mallaki zuciyarsa ya zama sai abinda nace masa alhmdullhi kwalliya ta soma biyan kudin sabulu.”
Halisa yini tayi cikin walwala da farin ciki yayin da ita kuma Naja’atu ta yini cikin damuwa da fargaba daga ta tuno abubuwan da suka faru tsakaninta da Abbah Abbas a daran jiya sai gabanta ya fadi gabadaya ta rasa samun nutsuwa a gidan, dan zaman daki ma gagararta yayi ta fito palo ta zauna cikinsu Saddiqa tayi zugum! sa’i da lokaci tsigar jikinta na tashi
Walwalar da Halisa take a gidan itace take bata mamaki sai wani ji take dasu har da tambayarsu me zata dafa musu na abincin rana..Kowa ya fadi abinda yake so banda Naja’atu dan cewa tayi bata bukatar cin komai..Halisa murmushin mugunta tayi ta wuce kicin cikin zuciyarta tace”Shegiya Idan kikaji wuya da kafarki zaki bar min gidana.”
Naja’atu kuwa na ganin yamma tayi lokacin dawowar maigidan daga kasuwa tashi tayi bar palon ta shiga dakinsu saddiqa ta zauna tana tunanin abinda zai fisheta. Waya take so ta samu ta kira Munira tana ganin gobe dole ta shiga gidan anty Maryam ta dauki wayarta a boye ta kira Kawar tata, wannan itace shawarar data yankewa kanta…….Mussadiq ne ya shigo yake fada mata Abbansu ya dawo, tace”To jeka naji.” Yaron ya kama hanya ya fita daga dakin, a maimakon taje tayi masa sannu da zuwa sai ta sake gyara zamanta dan bata tunanin zata je yi masa barka da zuwa taje taga abinda zai b’ata mata rai wani lokacin har mamakin kanta takeyi a duk sanda taga Abbahn da Halisa suna zaman lafiya gami da nuna kulawa a kan junansu take jin haushin hakan ta kasa gane me yasa hakan ke faruwa da ita.tunda ita dai tasan ba sonsa take ba to me yasa take jin haushi idan taga yana mu’amular arzki da matarsa.
Har suka zauna gurin cin abinci Naja’atu bata fito ba, ya kalli Mussadiq cikin nutsuwa yace.”Jeka kira Yaya Naja’atu tazo taci abinci.” Halisa tayi saurin cewa”Wallahi tun dazu ta shiga daki ta kulle kanta ni kam na rasa abinda ke damun Naja’atu wallahi gabadaya yini mukayi cikin walwala amma banda ita, gabad’aya kafin na shiga kicin sai da na tambayesu abinda suke so na dafa musu da rana kowa ya fada amma banda ita a takaice dai haka ta yini da yunwa gashi abincin daran ma taki fitowa taci.”
Takaici ne ya kama shi, shi kansa halin yarinyar ya soma bashi haushi duk abinda za’ayi mata ba’a burgeta, ya fahimci halisa na kokari a kanta kuma tana kokarin so su zauna lafiya da juna amma ita kullum cikin so ta tayar masa da hankali gida take.
Yace.”Ki kara hakuri da halinta Akwai kuruciya a tare da ita idan ta kara shekaru zata daina abinda take.” Halisa mirmushin munafurci tayi ta cigaba da had’a masa abincin, shi kuma Mussadiq ya shiga dakin nasu domin kiran Naja’atun
Fitowa yayi yana kumbura fuska yaron shima ya soma jin haushin abinda takeyi zama yayi gurin zamansa ba tare da yace komai ba.
Halisa tace”Ina naja’atun.”? Yaron yace.”Cewa tayi na fita na bata guri wai takoshi.” Abbah Abbas ransa ya sake baci abincinsa ya cigaba daci sai da ya kammala tukkuna ya mike ya nufi dakin.
Kan dadduma ya tarar da ita a takure tunda ta idar da sallahr ishai ta kasa barin gurin, Allah Allah take gari ya waye taje gidan anty maryam.
Ganinsa a tsaye a kanta yasa da sauri ta dago kanta tana rawar baki tace”Abbah sannu da zuwa.” Cikin tsare gira babu alamun wasa a tare dashi yace.”Tashi ki wuce kici abinci.” Mikewa tayi da sauri ta kama hanyar fita yabi bayanta yana masifar jin takaicin abinda yarinyar take masa gabadaya ta mayar dashi sakarai kamar yarinya ‘kan’kanuwa kullum sai yayi ya’ki da ita kafin taci abinci…Halisa kuwa ganin sun fito tare sai ta daure ranta ta shiga tsokanar Naja’atu wai ta daure ta dinga cin abinci ko ta samu tayi ki’ba idan ba haka ba sai Saddiqa ta fita kumari! Naja’atu ko kallonta ba tayi ba sabida tsabar haushinta da takeji ta nemi guri ta zauna tana cika da batsewa.
Zama yayi yana fuskantar ta yasa halisa ta hada mata abincin ya tura gabanta tare da fad’in “Maza ki cinye shi tas!
Kamar za tayi kuka tace”Abbah ina zan kai wannan uban abinci ai yayi min yawa.” Yace.”Kici ki koshi jiya ai haka kika kwana da yunwa yau da rana ma baki ci abinci ba duk ba zai rasa gurbi a cikin ki ba.
Tace”Gaskiya ba zan iya cinye wannan abincin ba kwata kwata ma bana cin pride rice ni.” Yace.”Yau zaki koyi ci dan wallahi kinji na rantse ba zaki mayar dani d’an wahala ba ni kenan zuwa siyo miki abinci kina ‘kin ci.” Halisa tasa dariya tace”To kai in banda abinka ai amarya bata laifi meye dan kayi mata hidima.” Kai tsaye yace”Na gaji da hidimar wannan yarinyar Halisa hidimar akeyi mata amma bata gani saboda haka ni ba zan zama sakarai ba.”
Halisa tana dariya ta bar gurin.
Naja’atu cin abincin kawai takeyi zuciyarta na tashi dan gabadaya bata jin dadin sa a bakinta, da kyar taci rabi! ya ajiye cokalin zuciyarta na tashi.
Tilasta ta yayi kan lallai sai ta cinye sauran, kuka ta dinga yi masa tana bashi hakuri da fadin”Idan ya tsananta mata za tayi amai yayi hakuri ya kyaleta, rabuwa yayi da ita ya mike ya bar gurin.
Itama barin gurin tayi ta nufi daki tana kuka gabadaya zuciyarta tashi take tana jin yanda abincin ke taso mata kwanciya tayi tana share hawaye.
Halisa kam shigar banza taje tayo ta baza tururruka masu kamshi da tayar da sha’awa ta fito palo ta sameshi yana duba loptop kamar dai koda yaushe….Tunda ya ganta yaji ‘kososhin kansa sun kwance, ya rasa wane irin turare ne wannan da halisa take amfani dashi a duk sanda zai sha’ki kamshinsa yakan rasa nutsuwarsa gabadaya….Loptop din dake cinyarsa ta dauke ta a jiye gefe ta hau cinyarsa tare da sakalo wuyansa da hannuwanta…Fuskarsa ya dora a kirjinta yana shanshanawa tare dasa hannayensa a kan mazaunanta yana matsawa, ajiyar zuciya suka sauke a tare….Naja’atu ta fito daukar lemo domin cikin firjin dake dakin babu kawai taga abinda sukayi saboda da akwai haske sosai a palo..Tsigar jikinta ne ya tashi ganin Abban Abbas din na tsotsar saman breast din halisa, gabadaya idanunta ne suka rufe ta juya da saurin gaske ta koma dakin ta rufe kofa jingina tayi da jikin kofar ta dafe kirjinta jikinta duk yayi sanyi kasala duk ta baibayeta! lokaci guda wata irin masifaffiyar sha’awa ta taso mata abinda Abbah Abbas keyiwa Halisa ya d’aga mata hankali sosai, zamewa tayi ta zauna bakin kofar tana takure jikinta.
Halisa kam sai da ta gama tayar masa da hankalinsa sannan ta cire jikinta daga nasa ta matsa gefe guda, yasa hannunsa cikin fitar hayyaci ya janyota tare da matseta a jikinsa yana cigaba da shashshafa ta….Tace”Abban mufida ina ganin fa abinda muke kamar bai dace ba muna shiga hakkin yarinyar nan a cikin kwanakin ta saboda haka yau fa sai dai kayi hakuri dan ba zan iya bari kayi komai dani ba kaje gurin matarka dan itama macece kuma tana da dik abinda kake bukata….Da yake baya cikin hayyacinsa sai yace.”Halisa bana jin yarinyar nan zata iya daukata a yanda nake jin kaina sannan kuma bata da juriya irin taki ki barni na biya bukatata.” Tace”Gaskiya na gaji da kwasar zunubi, sai dai kayi hakuri sai gobe tunda dama goben zaka dawo dakina amma bana tunanin zan iya amincewa da bukatarka a yanzu.