MAKAUNIYAR KADDARA 46

bakin ɗorawar kan hanya na jira Hajja Lanti zamuje anguwa. Ban musa 

mataba naje na canja kayana na fito, saita sake korani da cewar naje na 

saka kayan sallata. Zuwa nai na sake canjo kayan na fito, a gabansu na 

tafi inda tace naje na jira hajja Lanti ɗin. Na jima a bakin ɗorawa 

zaune sannan hajja lanti tazo ita da wasu yara da ban sansu ba. Batare 

da itama tamin bayaniba ta bani hijjabi da nikab wai na saka. Nidai ban 

musa mataba na saka. bayan na sakane ta kira masu mashin su uku suka 

daukemu zuwa Gozarki. A Gozarki muka kwana dan maraice ya rufa lokacin. 

Washe gari tunda farar safiya muka tafi inda ake hawa mota muka shiga 

motar Katsina da naji ana faɗi a wajen. Nasha mamaki amma a raina ina 

ɗoki zanje katsina da nakeji a labari. Koda muka isa Katsina an saukemu 

a wani waje mai tarin jama’a, mudai muka shiɗa a motar kamar yanda tace 

mana. Daga nan an ɗibemu a napep zuwa wani waje da naji hajja Lanti ta 

kira da suna anguwar yari.

          Kamar yanda ƴan uwan tafiyata basa gane komai a wannan tafiya 

nima dai ba ganewa nakeba. Sai dai ina lure da komai da akeyi. Kamar 

sunayen wajajen da muka sauka da inda muke tafiya. Mun isa anguwar yari 

da tace a kaimu. Inda aka saukemu a wani gida mai matsakaicin ƙyau da 

girma. 

        Koda muka shiga cikin gidan mun samu kusan mutane goma a 

cikinsa, Sai wata dattijuwar mata da tafi hajja Lanti shekaru dajin 

daɗi. Yanda ta tarbemu ne yasa naji ɗan dadi ga raina. Sai dai yanda 

maza da mata ke shiga da fita gidan baiminba a rai. Mun jima zaune suna 

hira kafin a kawo mana abinci muci, bayan mun koshi aka haɗamu da wata a 

gidan mai suna Sadiya. Itace ta kaimu wani ɗaki wai anan zamu zauna. 

Nidai kallon kowa nake da mamaki da tunanin mi mukazoyi nan? Miyasa Inna 

tace na biyo wannan matar nan batare da Baba ma ya sani ba?. Banda mai 

bani amsa, shiyyasa naja bakina na tsuke. Daga wannan lokaci ban sake 

ganin hajja Lanti ba a gidan, ban kawo komai a rainaba sai tunanin ko 

taje wani wajene ta dawo tazo mu dawo gida. Amma sai naji shiru har 

tsayin kwana biyu. Duk da ana bamu abinci muci mu ƙoshi, ga television 

muna kallo hakan baisa hankalina ya kwantaba, sai dai inajin tsoron na 

tambayi wani ina hajja Lanti take?. A randa muka cika kwanaki uku a 

gidan naga an kwashi abokan tafiyata su uku aka fita dasu a gidan, daga 

haka ban sake ganinsuba suma. Hankalina ya tashi na shiga yi musu kuka 

akan nidai su maidani garinmu, danni na ɗauka kodai ƴan yankan kai ne 

ma. Ranar naga ruwan masifa wajen matar nan, dan kamar zata dakani a 

turmi saboda masufar data dinga min. Dolena shanye kukana saboda 

tsoronta. Da maraice aka sake kwashe sauran abokan tafiyata su biyu da 

suka rage aka barni ni kaɗai sai waɗanda na samu a gidan. Ranarma nayi 

kuka har takaini gayin masassara. 

          Magani kawai suka bani nasha, daga haka babu wanda ya sake bi 

takaina, sai ma da daddare kusan ƙarfe takwas hajiyar tace a tasoni zamu 

fita. Ina jinta daga ɗaki danba barci nakeba, tunanin asibiti zata kaini 

yasa ban kawo komai a rainaba na tashi na fito bayan na saka hijjab 

ɗina. Tsaye na sameta a tsakar gida cikin gayu, na gaisheta jikina duk a 

sanyaye saboda zazzaɓi dake cina. Gaba tai na bita baya batare damin 

maganaba. Muna fitowa ƙofar gida muka iske mota mai ƙyau.

       Motarnan muka shiga, gabana nata faɗuwa nidai inata tunanin 

lokacin yanke nawa kan yayi. Dan haka naita addu’a kala-kala ina sharar 

hawaye a ɓoye da roƙon gafarar babana a zuciya, a haka muka iso wata 

babbar anguwa dabansan sunantaba, sai dai yanda ko’ina ke ƙwanyar da 

hasken lantarki zai tabbatar maka da anguwar masu kuɗice. Katafaren gida 

mai blue gate aka buɗe mana muka shiga, kasancewar darene bazan iya 

banbance tsarin gidanba, sai dai lallai ya haɗu matuƙa. Koda muka fito a 

motar hajiya ce ta kama hannuna muka shiga ciki. Anan ne na sake 

tabbatar da gidan ya haɗu, masu shi kuma sunada kuɗi. 

     Waɗanda muka samu a falon ne sukai mana iso zuwa ciki bayan mun 

gaisa, an sake kaimu wani falon, inda muka zauna zaman jiran matar 

gidan. Munfi ƙarfin awa ɗaya zaune kafin ta fito, ƙyaƙyƙyawa ce sosai 

baƙa, daka ganta kaga bafulatanar bakatsiniya, dan ƙyawun nata ya fita 

sosai masha ALLAH. Sai da ta gama mana kallon tsaf kafin ta amsa mana 

gaisuwa tana sake ƙaremin kallo, cikin maganar daban ganeba hajiya tace, 

“Ranki ya daɗe ga wata ki duba ko zata iya, yau kwana uku da kawomin su 

daga wani ƙauye”.

      Kallona ta sakeyi sama da ƙasa tana ɗan yamutsa fusaka. Ta ɗage 

kafaɗunta cike da isa tana faɗin, “Uhm babu laifi kam, dan tafi waccan 

komai, girma kawai waccan zata fita. Amma ina zuwa”. Tai maganar tana 

miƙewa, fita tai, babu jimawa sai gata ta dawo ɗauke da waya, batare da 

tayimana maganaba ta shiga haskani da hasken wayarta daban fahimci 

ma’anarsaba a wancan karon, sai dai a yanzu inaji a raina camara ne. 

Bayan ta gama kuma ta fara waya, da turanci take magana shiyyasa banji 

komaiba, bansan dai ga hajiya ba. Ta ɗauki lokaci mai tsaho tanayi kafin 

ta ajiye ta dubi hajiyar, “Ba damuwa zamu gwada mu gani, bara na ɗakko 

miki sauran saƙonki ko, idan akwai wani matsala zan nemiki daga baya 

kafin ki wuce, namafison sai mun kammala komai mun fara wucewa kafin 

taki tafiya”.

     Baki a washe Hajiya tace, “Ato babu damuwa ranki ya daɗe, ni bani 

da matsala duk yanda kukeso sai ayi, fatana dai ALLAH yasa a dace 

akumayi nasara”.

     Cike da yanga ta amsa da amin. Daga haka taje ta kawo mata saƙon da 

tace. Inaji ina gani hajiya ta miƙe tana faɗamin aini nan zata barni, 

nanne zanyi nawa aikin, dan haka sai nayi biyayya, yi nayi bari na bari.

      Sosai na fara hawayen fili saɓanin na zuci, yanda zuciyata kemin 

zugi da zafi ya hanani yin magana harta fice ta tafi bayan ta bani ɗari 

biyar a kuɗin danaga an bata masu yawa, itama haijiyar gidan ta shige 

batare damin maganaba. Da wannan damar nai zaman kuka na kusan awa ɗaya 

kafin wata tazo cikin wanda muka fara tararwa a falon farko ta kama 

hannuna muka fice.

        In taƙaita miki Granny tun daga ranar zazzaɓina ya ƙaru, inaga 

ganin yanda nake galabaita yasa Hajiyarnan ɗaukata a washe gari takaini 

wani asibiti mai ƙyau da alama na kuɗine. Anan aka bani gado. Sosai 

likitan yaytamin tambayoyi harnaji nama ƙosa dashi, amma na daure dan 

lafiyata nake nema ai. Kwanana shidda a asibitin nan na warke sarai aka 

sallamoni, sai dai kuma hajiya ta kaini wani gida ba nata da aka fara 

kainiba, naji tsoro sosai, dan can babu kowa sai wata dattijiwar mata 

mai suna Harirah. 

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button