MAKAUNIYAR KADDARA 46

     Ɗaki guda aka bani a gidan, wanda yaji duka kayan more rayuwa, ni 

harma abin ya ban mamaki amma sai ban tambayaba tunda dai ance aiki 

nazoyi. Komai na nema ina samu a gidan, amma sai dai a tsorace nake, dan 

haka kawai na kasa yarda da sakin jiki da baba harirah, sai dai kullum 

sai ta shigo ɗakina ita ta sakani shan magungunana na asibiti da aka 

bani. Hajiyar kuma ban sake ganintaba sai bayan kwanaki sai gata. 

Cataimin na shirya muje asibiti likita ya sake dubani, ban kawo komai a 

raiba na shirya na bita zuciyata fal fargaba. Munje likita ya sakemin 

gwaje-gwaje, sai yace wai akwai wani ciwo dake damuna zasu ban magani. 

Daga wannan maganar aka kaini wani ɗaki, tunda akaimin wata allura ban 

sake sanin inda nakeba sai a gida. Ni kuma tunda na farka sai tsoro ya 

kamani ganin ko baba harirah ɗinma yanzu babu, sai wani gardi abin tsoro 

dake a waje. Hankalina ya tashi, da ƙyar na samu nai wanka nayi salla. 

ina idarwa na saka kayan danazo dasu daga gidan hajiyar farko da aka 

kaini, ALLAH ya taimakeni na silalo na fito daga gidan, ɗari biyar ɗin 

da hajiyar ta bani da zata tafi lokacin data kaini can gidan itace ta 

taimaka mani na koma Danya. Koda na koma kuma saina kasa bama kowa 

labarin abinda ya faru har Babana, duk da inason na faɗa masa kodan 

kalmar iskanci da Inna ke dangantani da shi sai dai inajin tsorone”.

           Shiru hajiya iya kawai tai tana kallon Zinneerah kamar mai 

karanto komai akan fuskarta, sai dai wani irin tausayin yarinyar da 

ƙaunarta na sake shigarta. Dan yanda take bata labarin a nutse sai take 

ƙara godema ALLAH da samunta matsayin matar jikanta mafi soyuwa a ranta. 

Ta ɗan murmusa cike da basarwa tana faɗin, “Uhmm lallai dole ki kasa 

mantawa da birnin katsina. To amma ita hajiyar data kaiki gidan baki 

koma gidantaba bayan kin baro can?”.

     “Wai Granny sokike na koma ta sake maidani, nifa wlhy haka kawai 

naji banason hajiyarnan data kaini asibiti, ta cika tsare gida da mulkin 

tsiya kamar sarki”.

      A karon farko Hajiya iya tai dariya da juyawa tana kallon AK datun 

fara maganarta da Zinneerah ya shigo ɗakin, sai dai jin labarin da 

Zinneerah ta fara badawa ya sakashi dakatawa batare daya shigoba. Yanda 

ya kafe Zinneerah da idanu yana ma labarin nata fashin baƙi da 

nazartarsa yasa hajiya iya faɗin, “Amma baki taɓa gamo da maikama da 

wancan mutumin a katsina ɗinba?”.

     Sai a lokacin Zinneerah ta farga da AK, duk da ta jima tanajin 

ƙamshinsa a hancinta bata kawo shi baneba. Kallo ɗaya tai masa tai 

saurin maida kanta ƙasa saboda yanda kwarjininsa ke cika mata idanu da 

zuciya. Cikin girgiza kai tace, “A’a Granny, anan na fara ganinsa 

nikam”.

     “Inno bafa wasa nakeba”.

Da iya gaskiyarta tace, “Wlhy kuwa Granny”.

     Hajiya iya zata sake magana AK ya katseta da faɗin, “Kin shirya ne 

na kaiki gidan Gwaggon?”. (mmn sadiq).

      Tsaf hajiya iya ta fahimci dalilinsa na katseta, dan haka tai 

guntun murmushi da cewa, “Eh bara na kimtsa, ai hada Inno ma zamuje 

saimu barta acan dan da safe idan ALLAH ya kaimu zata dawo akwai inda 

zan turata”.

    Baice komaiba sai duban Zinneerah ɗin datai ƙasa da kanta yaɗanyi, 

ya ɗauke idanunsa ya juya ya fice. 

    Binsa da kallo Zinneerah tayi, tana ganin ya fice ta sauke ɓoyayyar 

ajiyar zuciya da har sai da hajiya iya tai murmushi………….✍

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button