HAUSA NOVELMUSADDAM NE ZABINA Complete Hausa Novel

MUSADDAM NE ZABINA Complete Hausa Novel

Inna Salma ba ta tsaya ko ina ba sai gurin bokan ta inda ta zayyana masa abinda yake tafe da ita.

Kusan mintuna goma ya dauka yana bincikensa na iska kafin yace, ” Salma na faɗa miki tun wannan yaron yana cikin cikin mahaifiyar sa cewa, “ba fa za ki taɓa samun nasarar raba shi da rayuwar sa ba, saboda haka ki koma gida ki zubda makaman yaƙin ki kawai shi ne mafita”.

Hararar sa tayi tace, “kawai kace min ba zaka iya ba, sai na kwana da sanin cewa yanzu lokaci ba ya tsaginka mtsssss aikin banza kawai”.

Murmushi bokan yayi yace, “ba ki tambaye ni dalili ba kin hau masifa Salma”.

Hararar sa tayi a karo na biyu tace, “faɗa min dalilan naka ina sauraro”.

Murmushin takaici bokan yayi yace, “saboda ya riƙe ALLAH da Manzon sa, mutumin nan yana cikin azkar ɗin safe da yamma ba sa wuce shi, sannan ba ya ga haka shi ne yake jiran lokaci sallah ba ita ke jiran sa ba domin yana yinta cikin lokaci. Shin wa ya faɗa miki cewa akwai wanda lokaci yake tsagin shi a rayuwar nan bayan shi kan shi rai da muke kuri da shi watarana zai bar gangar jikinmu m, ya koma ga mahaliccinsa. Ina mai sake gargaɗin ki da ki koma ki zubda makaman yaƙin ki don kuwa nima daga yau na bar harkar bokanci daga nan har zuwa ranar da ALLAH zai raba rai na da gangar jikina”.

Tashi yayi ya fara ciccire kayan jikinsa yana watsarwa sai dai kash, ya mance cewa lokaci baya jiran kowa wani irin giftawar farin haske ya gani ta gaban goshin sa, aikuwa nan da na ya zuɓe a ƙasa duk yadda boka yayi don ya samu yayi kalmar shahada ko kuma neman tuba ina abu yaci tura banda tattauna harshe babu abinda yake ,har rai yayi halin sa.

Ganin abinda ya faru da boka yasa Inna Salma fallawa a guje ta bar gurin jiki na rawa….

Koda inna Salma ta isa gida samun guri tayi ta zauna tana tunanin wannan al’amari.

ALLAH cikin ikon sa kuwa Muhammad da iyalan sa, suka lula ƙasa mai tsarki.

Tun daga wannan lokaci ALLAH ya buɗewa Muhammad hanyar arziki, kullum ƙofofin alhairai sake buɗe masa suke domin kuwa shi ma kullum cikin kyautatawa na ƙasa da shi yake ba tare da gajiyawa ba.

Kamar yadda Inna Salma ba ta huta da zuwa gun bokaye ba, haka shi ma Muhammad da iyalansa kullum cikin neman tsari suke gurin ALLAH mahaliccin kowa da komai.

Hakan yasa ko da sau ɗaya ba ta taɓa samun nasara akan su ba.

Sai da *MUSADDAM* ya kai shakara tara kafin suka sake samun wani cikin, sai dai kuma izuwa wannan lokacin kaf faɗin garin babu lungu da saƙo da sunan Alhaji Muhammad mai shinkafa bai kewaya ba.

ALLAH cikin ikon sa kuwa Ni’ima ta haifo ɗiyarta kyakkyawa mai kama da ita tsaf kamar an tsara kara, ranar suna yarinya ta ci suna *SAFNAH*.

Bayan wata ɗaya da haihuwar Safnah, Ni’ima ta matsa lalle fa tana son zuwa ƙauyen su Muhammad duk yadda Muhammad yaso fahimtar da ita tarin hidimar dake gaban sa amma sam Ni’ima taƙi saurara sosai abin ya ba wa Muhammad mamaki dan kuwa a tsayin rayuwar su a tare ba ta taɓa masa musu ko kuma jayya ba.

Hakan yasa ya aminci suka shirya. A ranar washegarin tafiyar ta su a can kasuwa ya rinƙa yiwa mutane kyauta da alherai iri-iri. Duk wanda Muhammad ya san akwai wata ƴar tsama a tsakanin su sai da ya ya roƙesu gafara duk kuwa da cewa da yawansu din ma shi ne yake da gaskiya.

Daga nan Alhaji Muhammad bai tsaya ko’ina ba sai gidan marayu kamar yadda ya saba zuwa. Nan ma sosai yayi musu abin arziki, a ranar sai da ya basu kyautar sama da miliyan ɗaya wanda adadi ne da a baya bai taba ba wa gidan kamar hakan ba.

Su kansu duk da ya saba musu kyauta,amma abin sai yake basu mamaki yanmdda yayi ta jan yara da wasa, wata yarinya daga cikin su wacce ba ta da ido, ma’ana makauniya ce har Alhaji Muhammad zai shiga motar sa cikin sauri ta laluɓa ta rike masa ƙafa da mamaki ya juya yake kallon ta tare da dafa kanta yace, “Nuriya kina lafiya?”

“Lafiya kalau Baba,”

Alhaji Muhammad gabakiɗaya jin sunan da ta kira shi da shi yasa ya ji tsigar jikin sa duk sun mimmiƙe, fashewa da kuka yarinyar tayi tana ƙara ja masa ƙafa, kwantar da muryar sa Alhaji Muhammad yayi yace, “kina buƙatar wani abu ne?”

Girgiza kai wacce ake kira Nuriya tayi tace, “a’a Baba ai ka gama bani komai tunda ka ba ni abincin da zan ci, kuma ka gina min gurin da zan kwana, sannan ka gina min makarantar da zan yi karatu duk da kuwa bana gani. Baba kar kayi tafiyar nan dan ALLAH”.

Cikin sauri Alhaji Muhammad ya kalle ta fuskar sa cike da tsantsar mamaki yace, “wa ya faɗa miki cewa zan yi tafiya?”

Murmushi Nuriya tayi tace, “baba duk da ba na gani amma ina iya ganin abinda ku masu idanuwa sam ba za ku taɓa gani ba, don ALLAH Baba karka tafi”.

Wani irin kuka Nuriya take wanda kallo ɗaya zaka mata ka fahimci daga zuciya kukan yake fita…..
????????????????????
*MUSADDAM NE ZAƁINA*
????????????????????

*PERFECT WRITER’S ASSOCIATION*????

( WE AIN’T PERFECT BUT WE’RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*STORY & WRITING*

*BY*

*SAFNAH ALIYU JAWABI*

*Reviewed by Musaddam Idiriss Musa*

_jama’a ku shaida na sadaukar da wannan littafin ga Musaddam Idiriss Musa_

1️⃣5️⃣

*Sometimes even those with good intentions can lead you down the wrong path. Tread carefully. Watch where you’re heading. Learn to listen to the Almighty more than you listen to people. Trust Him more than you trust people. People are fallible. He isn’t!*

 

 

 

__________Yayan Halima shi yayi kudumbala ya ba shi kudin sadakin. Sosai Muhammad ya yi farinciki da samuwar kuɗin sadakin ba tare da bata lokaci ba kuwa ya kai gidan su Ni’ima inda aka sanya lokacin aure nan da wata ɗaya.

A nan ne kuma zuciyar Muhammad ta sake cika da jin kewar iyayensa. Rintse idanuwan sa yayi yace, “ina ma a ce kina tare da ni a yanzu Umma!? Na san ko ba komai zan samu sassaucin kuncin da nake ji a raina. Ina ma zan wai ga na ganka a tare da ni Abba na, wallàhi na san da duk wannan kuncin ba zan gan shi ba. Yaya Suwaiba ina miki fatan shiriya daga ALLAH mahaliccin kowa da komai, haka kai ma yaya Sale. Inna Salma ke ma ina miki fatan ki gane gaskiya tun kafin lokaci ya kure miki.

Haka dai Muhammad ya zauna yayi ta addu’ar shiriya ga ƴan uwan sa idanuwansa na ta zubar da hawaye.

Yau da gobe kayan ALLAH. Haka aka ɗaura auren Muhammad da Ni’ima cikin kwanciyar hankali aka kai ta makeken gidan su mai kyau da tsari, ganin wannan gida sai da Muhammad ya zubda hawaye saboda a cikin rayuwarsa ko da wasa bai taɓa kawowa a ransa cewa zai mallaki wannan gida a matsayin nasa ba.

Cikin tsafta da aminci suke gabatar da rayuwar auren su, wata rana Ni’ima ta buƙaci su tafi garin su don ta saba da ƴan uwan sa. Babu musu kuwa ya amince suka tafi don kuwa shi ma abin yana ransa da ma lokaci kawai yake jira.

Ko da suka tafi garin sosai abubuwa suka ba shi mamaki ganin yadda Inna Salma ta ƙara lalacewa da son kuɗi. Suwaiba kuwa ta ƙanjame ta rame saboda fama da take da matsananciyar jinya, ga shi Sale yana magarƙama sanadiyar satan da yayi duk dauriyar da Muhammad yake da shi sai da ya zubda hawaye ganin yadda uwa tayi burus da rayuwar ƴaƴan ta.

Ni’ima kuwa tsabar tausayi sai da ta yi kuka har idanuwanta suka kumbura, ranar suka juya suka koma tare da Suwaiba suna zuwa ba su tsaya a ko’ina ba sai asibiti taimakon gaggawa aka shiga ba ta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button