Na Baki Rayuwa Ta, Complete Hausa Novel.

Har suka k’araso Afnan tana kuka, haka suka tasa k’eyarta suka shige cikin asibitin, koda suka bud’e k’ofar d’akin hankalinsu ya tashi matuk’a ganin Affan yana aman jini.
Muje zuwa
Page 40 to 45
Suna shiga d’akin suka tarar da Affan yana aman jini, hannunshi na dafe da saitin zuciyarshi.
Adnan ya kalli Afnan wadda ta mak’ale bakin k’ofa ta kasa k’arasowa ciki, kanta na k’asa tunda ta d’ago sau d’aya taga halinda Affan yake ciki ta duk’ar dashi, bata sake d’agowa ba, Adnan ya daka mata tsawa yace “wuce ki shige ciki ko in tattakaki, muguwa shed’aniya mara tausayi da imani kawai.”
Suf suf suf ta shige ciki, kuma ya dage sai taje bakin gadon taga halinda ta jefa Affan aciki, yanda ta iya kanta yana duk’e ta k’arasa bakin gadon, ta tsaya a tsaye k’ik’am.
Affan kuwa tarin da yake ya lafa mishi, d’agowa yayi ya k’ura mata idanu, sannan cikin murya ta jinya yace “ga kujera nan ki zauna. ”
Ba musu ta samu waje ta zauna, idon Affan yana kanta, yace “Afnan kiyi hak’uri da d’aukoki da d’an uwana yaje yayi, wallahi banda masaniya akan haka, har abada ina k’aunarki kuma bazan tab’a bari aci zarafinki ba, duk abinda kikaimin wallahi na yafe miki, Afnan *na baki rayuwata* dan Allah ki yarda nima ki bani taki rayuwar dan Allah Afnan. kuma auren da zakiy in har an riga da an d’aura to ina muku fatan alkhairi Allah ya sanya alkhairi, idan kuma ba’a d’aura ba to ina rok’onki da ki dubi girman Allah, ki kalli halinda nake ciki ki hak’ura da auren wancan mutumin kizo ki aureni, Afnan k’aunar da nake miki ta rigada taimin tabo me girma wanda in har ba mallakarki nayi a matsayin matar aureba to tabbas zan rasa rayuwata, baki fad’amin ba dagaske kike sona ba da tun farko na hak’ura, amma yanzu lokaci ya k’ure, domin kuwa k’aunarki itace ke sarrafa tunanina ban isa na gujewa faruwar hakan ba, saboda sonda nake miki ya rigada yai miki har ya zama gyambon da be tab’a warkewa, amma kije kiyi tunani, tashi ki tafi abinki,” duk wad’annan maganganun cikin zubarda hawaye yake yinsu.
Afnan batace komai ba, amma ga dukkan alamu jikinta yai matuk’ar sanyi, haka ta tashi ta doshi hanyar fita, Adnan ya tare k’ofa tare da fad’in babu inda zataje.
Affan ya kalli Adnan yace “Adnan,” Adnan yace “na’am,” Affan yace “kaf duniya babu abinda na tsana irin naga ana cin zarafin Afnan, dan Allah in kana k’aunar farin cikina ka k’yaleta ta tafi, bana k’aunar duk wani abu da za’ayi domin tirsasa mata ko yi mata barazana, ka k’yaleta ta tafi in baka bartaba zan iya shiga wani mawuyacin hali sanadin haka, kaga fa hawaye takeyi saboda takurawarku, wallahi in ka bari ta cigaba da kuka sanadinka bazan tab’a yafe maka ba. ”
Adnan ya matsa Afnan ta wuce ta fita daga d’akin.
Abinda Affan be saniba shine tana fita D. P. O yaiwa jami’an dake waje message akan da ta fito su kamata su wuce da ita station su kulleta zaizo daga baya.
Sun shafe wajen sati biyu a garin, duk kiran da Inna tayi da irin k’aryar da Adnan ke shirga mata.
Yau lahadi, kuma yau aka basu sallama sakamakon sauk’i da Affan ya samu sosai, sun shirya tsaf domin tafiya, D. P. O kawai suke jira yazo suyi sallama.
Suna cikin jiranshi kuwa sai gashi ya shigo, bayan sun gaisa suka yi mishi godiya akan irin taimakon da yai musu da kuma irin dukkanin kulawar da ya basu, har bakin mota ya rakasu inda sukai sallama Adnan yaja suka d’auki hanyar zaria.
Haka suka taho hanya suna hira jefi jefi, duk da hirarma Adnan ne yaketa janshi da ita, saboda sam baya k’aunar yaga Affan d’in yai shiru yana tunani yanzu sai kamanninshi su canza, kuma an gargad’esu da hanashi shiga damuwa da tunanin.
Tun suna hanya Adnan yaiwa Inna albishir cewa suna hanya shida Affan, har tana fad’in ho d’an nema ashe can ka tafi kaketa yimin hanya hanya a waya, hakan yasa ita da k’annen Affan wato su Yasmeen aka shiga shiryawa babban yaya da Adnan girki me rai da lafiya, sedai kash
Suna shigowa cikin unguwarsu ciwo ya dawo sabo, Adnan duk ya rud’e, sam baya k’aunar Inna taga Affan a irin wannan yanayin, yana k’ok’arin juya motar suje asibiti ne kawai ya gansu sun fito daga gida cikin sauri kowannensu fuskarshi d’auke da murmushi suna jiran fitowarsu domin suga yayansu.
Sedai ganin Adnan ya fito shi kad’ai ga tari matsananci suna ji a cikin motar yasa sukayi saurin k’arasowa inda motar take.
Halinda suka tarar da Affan a ciki shi ya tsayar da dukkanin fara’ar fuskarsu, a yayinda cikin k’ank’anin lokaci kuka ya maye gurbin dukkanin walwalarsu.
Inna ce cikin kuka take fad’in “Innalillahi wa inna ilaihir raji’un me zan gani haka!!! Affan menene ya sameka haka, juyawa tayi b’angaren da Adnan yake wanda yaketa kuka yama kasa cewa komai, saboda a yanzu bayan ciwon Affan d’in dake damunshi harda tausayin mahaifiyarshi da kuma k’annenshi.
Inna tace “Adnan me ya sami Affan d’ina ka sanar dani dan Allah, aman jini fa yake, yanzu halinda yake ciki kenan dama shiyasa kaketa b’oyemin Adnan, ” duk ta rikice ta cukuikuye Affan d’in tana kuka, a yayinda suma k’annenshi suke kusa da Innar tasu suna kallon halinda d’an uwan nasu yake ciki suna kuka.
Adnan ne cikin k’arfin hali da wata irin muryar kuka yace “Inna ku shiga mota mu kaishi asibiti, daga baya na sanar dake komai. ”
Cikin sauri Adnan da Inna suka maidashi baya Inna ta zauna kusa dashi, kanshi yana Kafad’arta, ‘yan uwanshi ma dukkansu suka shiga, Adnan yaja motar cikin sauri suka tafi asibitin kud’i saboda Adnan bayaso a b’ata lokaci wajen dubashi, yana tuk’i yana kuka tare da waigowa yana kallon halinda Affan d’in ke ciki, gudu yake sosai amma duk rashin son gudu da inna take a mota a yau gani take kamar baya wani gudu, ji take kamar ta karb’i motar taja.
Allah ne kawai ya kaisu bakin asibitin lafiya, cikin sauri ba b’ata lokaci aka shiga dashi emergency likitoci suka duk’ufa a kanshi.
A wannan lokacin ne Adnan ya sanar da Inna komai, kuka Inna take kamar zata shid’e, tana fad’in “meyasa baka fad’amin ba Adnan, meyasa Affan zai mana haka, akan mace zai salwantar mana da rayuwarshi, bayan yana sane da cewa tafi komai muhimmanci a garemu, ” Adnan ya kasa cewa komai domin kuka yake shima.
Likitoci suna kanshi har wajen awa shida da rabi sannan suka fito, d’aya daga cikinsu ya nufo su Inna, suma su Inna kanshi sukayo cikin sauri suna tambayarshi lafiyar Affan d’in.
Doctor yace “to munyi iya yinmu sauran sai mu barwa Allah, amma kun rigada kun bari jikinshi yai tsananin da har zuciyarshi tayi mugun ciwo, zamu cigaba da dubashi mu ga abinda Allah zaiyi, wasu kayan aiki zan d’auko mu cigaba da dubashi, ” yana gama fad’in haka ya wuce, a yayin da jin haka ya k’ara tayar da hankalin su Inna sosai.
A tak’aice saida yai kwana biyu rak yana kwance besan ma inda kanshi yake ba, a kwana na uku ne Allah yasa ya farfad’o, yana farfadowa ikon Allah kuma sai jikin yai sauk’i, su Inna sukaji dad’i sosai, abinci yakeci, yana ci yana kallon Inna da taketa kuka har yanzu.
Affan ya kalli Inna yace “haba Inna menene kike kuka kuma bayan gashi na warke? ”
Inna tace “meyasa ka b’oyemin abinda ke faruwa Affan, dama duk halinda ka shiga a baya saboda watace wadda bata damu da ka rayu ko ka mutu ba, wallahi abinda tai maka da kuma halinda ta jefaka a ciki insha Allah sai……..” Affan yai wuf ya rufe bakin Inna yana kuka yace “Inna dan girman Allah kar kiywa Afnan baki, ki yafe mata, karki manta yafiya sifface daga cikin siffofin ‘yan aljanna, duk da abinda taimin har yanzu ina k’aunarta Inna, kuma bazanji dad’i ba idan naji kinyi mummunan kalami a kanta, ki yafe mata, nima ina rok’on afuwarki akan irin k’aryar da naita yi miki Inna. ”