Noor Albi

NOOR ALBI 1

Rayuwar Laylah rayuwace Mai cikeda zallan kadaici da maraici,
Tunda tafara wayo taga yanda Momy Bata taba kallontaba bare amsa ko gaisuwarta Amma Kuma Bata taba hantarartaba saita taso cikin juriya da rungumar rayuwar ahakan tareda yarda da cewa tabbas itace sakamakon cin Amana da haincin da akaiwa Momy Wanda ya rusa rayuwarta da kwanciyar hankalinta na gidan aurenta Dan kuwa tun lokacin Momy ta Rasa miji tunda yakoma baida wani amfani agareta da yarta tun daga kan auratayya har Kan sauran haqqoqin.,

Da wannan zuciyarta take kasa Jin ‘dacin Momy sbd takowane sashe tabbas itace mummanar qaddarar data Bata rayuwarsu shiyasa ta sadaukar da kanta da rayuwarta gurin bautawa Momy da anty Sa’adah ko zata iya biyansu ta wani sashen da abinda abbanta da mahaifiyarta da Bata Raye sukai musu,
A rayuwarta cinta da Shanta tareda karatunta momynce ta dauka nauyi abisaga aikin wahalar datake musu tun bayan data girma aka sallami Mai aikin data raineta harta girma ragamar aikin gidan tadawo hannunta tun daga kan girki da tsaftar gidan,

Sam rayuwar Momy a baude take wanzuwar laylah a rayuwarta sbd tuni ta Rasa annashuwa da dariyarta harma da murmushinta,
Rayuwarta Takoma ta wata irin cunkusashiya kasancewarta cikin mutane masu tsananin riqo a zuciya shiyasa duk tsawon shekarun Bata tabajin sassaucin abunda takejiba akan al’amarin.

Babban abunda yake tattareda rayuwar Layla na nutsuwa da kwanciyar hankali shine tsananin kauna da soyayyar da mahaifinta ke Mata Mai tsanani da wadda ‘yar uwarta Anty Sa’adah ke Mata Dan kuwa anty Sa’adah itace gatanta a fili da boye sbd itace ta tsaya Kai da qafa agurin mahaifiyarta ta roqu alfarmar bawa laylan damar karatu bisaga neman alfarmar zata karba ragamar aikin gidan,
Da wannan Laylah tasamu tayi karatu a makarantar gwamnati Mai dama dama harta samu ilimin bokon datake dashi sabanin ita Sa’adah datai karatun private school Mai kyau,

Anty Sa’adah ce gatanta a duk abinda ya danganci haqqin dake rataye akan iyayenta na kula da ita shiyasa koyaushe Abba ya bude idanuwansa akan Sa’adah yake Mata godiya cikin ganin qimarta itada momyn sbd koma yayane da dukiyar momyn Sa’adah ke yiwa Laylah hidima Wanda itama momyn rufin asirine kawai na ‘yar kasuwancin buga buga datake Dan tallatawa rayuwar yarta da abban da yarsa dasuka zamar Mata wani babban jarabawan rayuwa.

Mahaifiyarta ta rasu tabarta a ranarda ta haifeta Dan Haka batasan wani shaquwaba ko sake tayi Wasa tareda wani,
Mahaifintane Kuma kwance ta bude ido tagansa,
Anty Sa’adah Kuma kallon wadda ke tallafe da rayuwarta take Mata duk da a zuciyarta matsayi da girman kaunar datakewa anty Sa’adahn daban ne.

MAMUH

NOOR ALBI
Rabo sai Mai shi…Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!
Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon ‘da amatsayin nata mijin?
Qaddararsu wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?
NOOR ALBI Hasken rayuwata
Littafina dayazo muku da wani salon na dabam Wanda soyayyarsa ta kere sauran labaraina,salonsa ya bambanta da sauran,nishadinsa da shauqinsa na musamman ne
Fata dai ku kasance taredamu kuji zafi zafin damuka dawo muku dashi
NoorAlbi#MAMUH

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button