Noor Albi

NOOR ALBI 12

Wannan ‘yar Zainab ce ko?

Eh itace” Sa’adah tafada kanta a qasa
Haj Karima kuwa kasa hakuri tayi ta miqe tana cewa”

Bari muje mukai wani sakon sainmu dawo mu dauki Sa’adah din daga baya Idan tagama gaidaki.

Cikin kulawa Anne tace”

Ba damuwa kuje tunda zaku dawo saina sake gaisawa da Laylah ko? Tafada tana kallon Laylan Wanda har lokacin itadai bayan gaisuwa batace komaiba kanta na qasa Wanda yasa Anne fahimtar Kamar Laylan nada matsala ko damuwa sbd sanyinta da rashin kuzarin yayi yawa.

Sa’adah datafi kowa farin cikin tafiyar Haj Karima da Laylah
Tana ganin Haj Karima taja Laylah suntafi sbd karsu bada damar da Anne zata qaunaci Laylah
Shi Turaki basama maganarsa Dan sunsan bazai taba ganin laylan ba saidai idan yaganta wata Rana a gidansa acikin Yan aiki.

Ajiyar zuciya Mai sanyi anty Sa’adah ta sauke tareda Dan dagowa kadan tanason magana Amma tanajin nauyi da fargaba saiga sakon zuwan Kawu saidu ya isowa Anne Ana neman ison shigowa dashi.
Wata irin Ajiyar zuciya anty Sa’adah ta sauke sbd tabbas wannan zuwan nasa wani aike ne daga ubangiji.

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button