Noor Albi

NOOR ALBI 13

Kallon Fattu Anne Tayi Kai tsaye tace”

A qarasa dashi daga ciki gama su Sa’adah anan,a shigo dashi.

Juyawa Fattu tayi ta koma can harabar gidan tayi Masa iso yabiyota daga baya har zuwa cikin palon
Ya Dan durqusa Yana gaidata cikin mutuntawa sbd ta girmesa sosai gata Kuma tamkar uwa.

A mutunce cikin kulawa tace”

Malam saidu Kaine da kanka kazo baka Bari Turakin yaje gurinka da kansa ba.

Murmushi yayi Yana zaunawa Kan kujerar one seater dake nesa da Annen Yana cewa”

Aa bakomai ai
Nima ai bama maganar komaiceba takawoni ke nazo yiwa barka da zuwa tunda Anjima sosai ba’a haduba,
Allah dai yaqara nisan kwana da lafiya da kwanciyar hankali,
Anata dawainiya sosai da kashe dukiya, ubangiji Allah yasaka muku da mafificin alkhairinsa yabar zumuncin da akaiwa,
Dan kuwa duk ranarda Allah ya tashi kafadun Mahmoud saiyayi qwallar farin ciki da wannan al’amari sbd kun rufa asiri tako Ina tareda dawainiya da iyalinsa.

Katsesa Anne Tayi da cewa”

Wannan duk yiwa Kaine bakomai bane,Allah dai yabasa lafiya
Yakuma Sanya alkhairi acikin wannan lamarin.

Amin Amin ya Allah” Kawu Yafada da hanzari Yana Dan kallon Sa’adah data gaishesa cikin girmamawa
Ya kalleta dakyau cikin Dan mamaki yace”

Wannan Sa’adah ce kokuwa?

A sanyaye tace”

Nice Kawu.

Kasa shiru yayi da mamaki da ‘dan takaici duk da yana kokarin boyewa agaban Anne yace”

Ke dawa Kika zo?
Me kikazo Yi keda zasu tafi Dake jibi Kuma meyene na zuwa yanzu?

Sunkuyar dakai tayi cikin tsananin kunyar kanta da baqin cikin halin dangin mahaifiyarta.

Anne ce tayi murmushin manyanci tace”

Zuwa sukayi gaidani
Bakuma illa bane hakan, tare suke da Yar gurin Zainab wato zainab.

Gyada Kai yayi Yana jinjina al’amarin dangin Zainab da basuda lissafi ko daya.

Dan dagowa Sa’adah tayi cikin zurfafa kalami da nutsuwa ta kalli Kawun tace”

Kawu inada maganar fada akan….cikin wani Irin sauri da waskewa Kawun ya katseta da cewa”

To Ina suka tafi da bazasu taho ku koma Haka ba tunda Kun Mata barka da zuwan.

Kallon mamaki Sa’adah takewa Kawun ganin ya da yayi saurin katseta kamar yasan abunda zata fada,
Kokuwa shima su umma Jamila sun siyesa an shafa Masa kudi?

Shikuwa Kawun sanin rashin Arziki irin na dangin Zainab yasashi katse Sa’adah din Dan baisan mezata fadaba agaban sirikar da ba’a ringa andaura aurenba taje ta zubarwa da kanta dashi da Dan uwansa mutunci tunda su dangin uwarta Akan kwadayi yaga alamar ba kalar mutuncin da bazasu zubarba.

Sake yunqurin magana tayi ya banko Mata wata irin mugun kallo yna kokarin miqewa Yana yiwa Anne sai anjima shi zai tafi.

Kallon Sa’adah da idanuwanta suka sauya tayi dakyau taga alamar da akawai damuwa saita kalli Kawun a natse tace”

Kaga malam saidu koma ka zauna
Yarinyar Nan magana zatai dakai
Da alama Kuma akan auren Nan
ALLAH yasa ba Dole acikin al’amarin??

Ajiyar zuciya ya sauke yana komawa ya zauna zuciyarsa fal da takaici Dan kuwa idan har yarinyar Nan ta bude Baki gaban Anne tace batason auren Turaki wlh saiya Mata dukan mutuwa tabi sahun mahaifinta asibiti
Dan iyakar zubarda girma da mutunci ta zubar masa idan hakan tafaru
Kuma agaban Anne yarinyar Nan zata shimfida wannan rashin da’ar.

Kallon Sa’adah Anne Tayi hankali kwance a natse tace”

Menene Damuwar Sa’adah?
Auren ne bakyaso zasuyi Miki Dole kokuwa?

Zazzaro idanuwa Kawu saidu yayi Yana kallon Sa’adah Dan ta kallosa yasamu damar Mata gargadi Kota idone Amma taqi kallonsa Kai tsaye ta gyada Kai tareda sauke Kai daga kallon da Anne ke Mata tace”

Bani Abba yaceba
Laylah yace….
Dan shiru tayi na minti daya kafin ta hadiye hawayen dasuka ciko idanuwanta tana qara bawa kanta qwarin gwiwar magana tace”

Su umma Jamila ne sukeson sauyawa Dani Amma Abba Laylah yakes…..kasa qarasawa tayi sbd siririn kukan dayazo Mata na karyewar zuciya Dan kuwa harga Allah da ita din aka bada datayi farin ciki Amma Kuma bazata iya auren Wanda ba ita din aka basa aurenba Kamar haramci take kallon kanta a auren shiyasa ta Kori shedan ta danne komai ta fada gskia.

Wasu manya manyan Ajiyar zuciya Kawu saidu ya ringa jerowa a boye Yana Dan goge zufan daya tsatsafo Masa a goshi cikin dubara
Dan duk yagama katsewa da bijrewa auren Sa’adah zatai ta wulaqanta zumuncin da mutunci da Anne ke gani
Shi Turakin ba’a maganarsa sbd yasan ko ahaka Matar da auren ba lallai suna gabansaba.

Anne kuwa wani irin kyakkwan murmushi Mai sanyi tasaki tana kallon Sa’adah din cikin tsananin burgewa da yabawa da hankalinta datai saima taji Sa’adah din tashiga ranta itama Dan Haka ta kalli Sa’adah din a natse tace”

Meyasa zasu sauya Laylah bayan da ita din Dake duk Abu dayane?

Shiru Sa’adah tayi Bata iya cewa komaiba sbd a bayyane yake basai anfadaba ansan Laylah batada gata batada Wanda ya tsaya Mata sai Allah.

Wani murmushin Anne takuma saki kafin ta kalli Kawu saidu tace”

Malam saidu kaji abindayake faruwa.

Cikin takaici da baqin cikin Hali irin na zuriarsu umma Jamila yace”

Tabbas dama Zainab da danginta bazasu taba Bari Laylah tayi rayuwarda kowane ‘da mai yanci zaiyiba,
So suke yanda ta taso a wahala ta qare a wahala shiyasa gashinan masifarsu da rashin imaninsu ya haukatar da ita kwakwalwarta Bata cikakkiyar lafiya
Yarinya Takoma Kamar mutum mutumi
To gwara danaji wannan zancen Dan kuwa wallahi ita Zan daurawa aure dukkaninsu sun Dade kwadayi Bai Gama kashesuba Dan nasan manufarsu ta auren
Kema nafasa tafiyar bazan tafiba saina aurar Dake ga duk Wanda nasamu zanga uban dayafini iko akanku cikinsu.

Daga fada da maganganun Kawun Anne tafahimci abindayake faruwa a rayuwar iyalin Mahmoud din take taji wani irin rashin Jin Dadi da tsananin qauna da tausayin Laylah
Yarinyar data taso cikin maraicin uwa da uba duk da Yana Raye,
Tabbas kuwa Kamar yanda Kawun Yafada aure Kam da Laylah Kamar ba fashi saidai Kuma fushinsa na aurarda Sa’adah din daketa kuka Mai tsima Rai bataga DACEWA da adalci a hakan ba Dan kuwa itama Sa’adah ta cancanta rayuwa Mai kyau tunda har tanada kyakkwan zuciya Dan Haka Kai tsaye tace”

Malam saidu kayi hkr karka yanke hukunci cikin fushi akan Sa’adah da Babu ruwanta a wanna al’amarin
Idan har batada wani tsayayyan mijin Zan tafi da ita kodan Yanayi na rayuwar Laylah daba lafiya isashiyaba
Tunda harkace ta mental health Dole zaaje da Wanda tasaba dashi harta warware tafito daga depression din datake ciki kafin ma ayi maganar sanar da ita auren Dake kanta daga
Kuma best solution anan shine tafiya da Sa’adah,
Dan karatu da komai na rayuwar Sa’adah na dauka Inshallah Dan dama tuni yakamata muyi hakan mu dauki ‘yayan Mahmoud Dan inganta rayuwarsu da ilimi Mai kyau da tarbiya
Amma tunda yanzu komai yazo da hakan Inshallah idan ka amince Zan daukesu duka su biyun
Laylah Amatsayin Matar Turaki Sa’adah Amatsayin Amanata Inshallah.

Sosai ran Kawu yake quna da Daci sbd har kunyar kansa yaringa ji daya biyewasu Alhaji Atiku Ashe yaudararsa akeyi Dan ya cutatar da ‘yar marainiyar ‘yar Dan uwansa duk da Sa’adah dinma daya suke agunsa Amma ita tanada gata tako Ina tunda gashi sunso cin amanarsa su tura tasu Yar gurin arzki,
To kuwa zasusan yanda asalin mugunta da yaudara take Dan yanda sukai Masa Haka zai musu bazai fada musu gskiyarba shima shiru zaiyi sai ranarda Allah ya nufa susani.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button