Noor Albi

NOOR ALBI 5

Suna isowa shagon Mai dinkin yacewa anty Sa’adah Bai kammala ba
Dama hakan takeson ji Dan Haka ta nema guri Suka zauna tace ya kammala zata jirasa.

Kallonta Laylah tayi tana kallon agogon shagon cikin nutsuwa tace”

Anty Sa’adah karfe daya saura
Ni Zan koma gida
Kinga ban Dora abinci ba Kuma kada Momy tanason wani aikin bana Nan ga Abb….

quiet please Laylah,
Bazan barki ki komaba Zaki jira nagama tunda Nina fito Dake zamu koma tare so just sit quietly muyi zaman jira,
Fushin Momy na rashin aikinki yafi Miki zuwan umma Jamila so dubu.

Shiru tayi sbd Bata iya hayaniya ba bare tayita magiya saidai hankalinta gabaki daya Yana Kan abbanta da momyn,
Dan kuwa har cikin ranta qaunar uwa takewa momyn shiyasa Bata qaunar ta Bata Mata Rai.
ga zazzabin dake cinta har lokacin.

Zama yayi zama sune har la’asar Basu koma gidaba sai qarfe biyar Adaidaita sahu ta ajesu kofar gida
Anty Sa’adah ce agaba taba bayanta riqeda ledar kayan anty Sa’adah din suka shigo da sallama tun daga tsakar tasan Bata kyautaba qin dawowa da wuri sbd Yar dattin da gidan yayi na iska da aka danyi kamar za’ai ruwa.

Kallon inda su momyn suke zaune tsakar gida Kan babbar daddumar baqin girman momyn sun Gama cin abincin da aka kawo musu daga gidan umma Jamila din tunda yau baai abinciba Nan gidan suna magana hankali kwanci saidai shigowarsu yasa bacin ran da umma Jamilan ke dannewa tasowa ta kalli Laylah bayan ta amsa gaisuwar Sa’adah data zauna gefenta tana daukan ruwan robar swan Dake gurin ta bude tana sha
Tace”

Zainab haryanzu kin kasa gane illar jini,
Shi Abu idan akace a jininka yake to saifa iko na ubangiji,
Kinada ‘ya mace budurwa a gabanki da kikewa fatar samun miji na hutawa da Jin Dadi kike Bari suna fita tare da yarinyar nan?
Ta Yaya kike tunanin namiji daya zai kallesu idanuwansa su kasa tsolewa da wannan kodaddiyar fatar ta jinin gado,
Mahaifiyarta da mahaifinta akwai wani gadon dasuka bar Mata bayan na jinin cin Amana ne,
Magana daya itace na soke fitar Sa’adah da laylan daga yau karna ji ko a labari wannan umarni nane,

Shine kina zaune zata saka qafa ta fice  ko aikin abinci Babu idanma kinyi baqin kunya Dole kece da tsufanki Zaki shiga kicin girka abinci
Ke kenan Haka rayuwarki zata qare a bautar Mahmud da ‘yarsa bakya tunanin Taki Yar?
To Allah ya kyauta,
Sa’adah ma Inshallah saiki fara shiri ki fadawa Mahmud din babban ‘dan Alhaji Sadiqu commissioner Dake aikin Lawyer a Lagos munyi mgna da  alhajin zasuzo neman aurenta
Allah yayi Kinga tasamu miji gidan Jin Dadi da arziki Kar aja wani lokaci ayi Mata auren tasamu ta tafi gidanta inda zatai irin rayuwar da kike Mata fatar samu
Kema Kinga kin samu nutsuwa shikenan Babu Wanda zakiwa wahalar nema saiki zauna abinda yazo kibasu Wanda baizoba saisu dangana shida ‘yarsa.

Idanma bazaki iyaba Ni bayan auren Sa’adah din kiban laylan Dan masu aikina duk sun isheni wlh
Saina ringa biyanki kudin aikinta Kuna dawainiyar dashi kin huta ya komaima.

Momyn dai batace komaiba sai kayan wayarta datake dubawa tana hada Kan wani lissafi
Saidai fuskarta sosai ya bayyanarda farin cikin zancen mijin Sa’adah din da akai takumayi na’am da maganar auren saidai maganar Laylah batace kala ba duk da tariga tasan cewa tabbas Sa’adah tayi aure zamanta daga ita saisu Laylah din bazai musu dadiba su dukan Dan tasan zamanta a gidan zai iya karanci Dan kuwa zata saka kanta busy ne da yawon kasuwanci ta ringa Hana kanta zaman gidan sosai.

Itadai Laylah sallah tayo tazo tanata ayyukanta batareda ta dago Kai ta iya kallonsu ba bare ta nuna damuwar zance ko daya acikin zantukan sai kaida kawonta take tana aiki.

Anty Sa’adah ma shigowar zancen aurenta cikin maganar ya hanata saka Baki ta kare Laylah tareda sanar dasu burinta dataci alwashin duk ranarda tayi aure zata tafi da Laylah Dan inganta rayuwarta da ilimi Mai zurfi na boko.

Har akai magriba Bata Gama aikin abincin data doraba
su Kuma tuni Suka shige ciki suka bar wajen ta sake share tsakar gidan kafin ta sauke abincin ta zuba a kuloli takai musu tadawo ta gyara gurin,
Bataci nata abincin ba Saida tayi wanka tayi sallah ta dawo kicin din ta Dan ci kadan ta fito ta nufi gurin abbanta.

Zaune yake Kamar kullum Kan kujerarsa zugum Yana sauraron duk abinda yake faruwa a tsakar gidan
Maganganun Umma Jamila sun tabasa sosai sbd bayajin har abada idan ba aureba zai iya bawa wani Laylah,
Yasan a yanda yake dinnan tabbas yanaji Yana gani umma Jamila zata iya daukan Laylah kamar yanda tafada Wanda yasan tabbas duk juriya da hakuri irin na Laylah taje gidan umma Jamila rayuwarta tagama Shiga hawula’i Dan Haka bazai taba Bari hakan ta faru ba
Matuqar zasuwa Sa’adah aure yasan Laylah bazata qara Jin dadiba ko sassauci Dan Haka itama auren zai Mata a inda zata ingantu Koda Babu soyayya yasan zatai daraja.

Tana qarasawo gabansa ta zauna tareda abincin data debo zata basa ya kalleta da idanuwansa dasukai ja ya Mata alamar ta matso da hannu
Ta kallesa cikin sanyin jiki kafin ta matso din batareda tace komaiba takai kunnenta bakinsa
Cikin rawar muryar Dake tafe da kakari daqyar can qasa yace”

Zan Miki aure kafin auren Sa’adah zakije inda zakiyi rayuwa kema
Allah zai Baki farin cikinda sai sunyi Miki kukan Dadi da godiya su umma Jamila……..

Wani irin faduwa gabanta yayi tsananin mamaki zancensa yasata bama firgici ba sbd tasan Babu wani maganar aure a rayuwarta yanzu,
Tayi aure tabarwa wayeshi Abban.

Kallonsa takeyi cikin nisa a tunani Dan batamasan Mai zatace Masa ba kafin daga baya ta miqe ta fice ganin dare yayi.
Tana fita abdullahi na shigowa yayi Masa alamar Kira tareda fadar sunan AB TURAKI daqyar alamar shiyakeson Akira masa
Take abdullahin ya fidda wayar Abban Dake drwer wadda aka aje sbd Kiran mutanensa da basa daukan sabuwar number Amma suna daukan me sunansa ya lalubo Numbern qasar AMERICA.

MAMUH

👇👇👇Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete 👇👇

Mamuhgee @Arewabooks

Rabo sai Mai shi…Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!
Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon ‘da amatsayin nata mijin TAYAYA ZATA KALLA AMININ MAHAIFINTA A MATSAYIN MIJINYA
Qaddararsu wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?
NOOR ALBI Hasken rayuwata
Littafina dayazo muku da wani salon na dabam Wanda soyayyarsa ta kere sauran labaraina,salonsa ya bambanta da sauran,nishadinsa da shauqinsa na musamman ne
Fata dai ku kasance taredamu kuji zafi zafin damuka dawo muku dashi
NoorAlbi#MAMUH

Follow me @ArewaBooks
Mamuhgee For my latest updates

KUFAN WUTA
Safiyya Huguma

BAQAR INUWA
Billyn Abdul

RAYUWAR MACE
Hafsat Rano

MASARAUTA
Miss Xoxo

NOOR ALBI
Mamuhgee

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

09032345899

KATIN MTN

09166221261

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button