HAUSA NOVELRASHIN ADALCI Complete Hausa

RASHIN ADALCI Complete Hausa

*????????AINUWA ????RITER’S✍????*
*????SSOCIATION????????*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*????????

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*

 

*PAGE 9*

Dariya ta rinƙa yi ita kaɗai a ɗaki,ganin yadda kowa ya hallara a cikin group ɗin ana jiranta,voice ta yi ta ce,”innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!! innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!!! wai jama’a yau kun ji zafin rana gaskiya yau naji zafi kamar zan zaucewa.”

Voice ɗin ta tura,dariya ta ci gaba da yi,cikin sauri kowa ya buɗe voice ɗin, Chairman ya fara turo voice,Husna ta buɗe voice ɗin,”amma wallahi wannan Husnar….ke gaskiya sai dai ki yi haƙuri amma dai ke Banza ce…. wallahi da ki ka fara salati nayi zaton mutuwa aka yi za ki sanar damu.”

“Kai yanzu Chairman ni kake ce ma banza?”Husna ta tambaya ta na dariya saboda ta san ta kai su ƙarshe.

Hadiza Muhammad (wadda Husna ke ce ma jakarta)ta ce,”kai jikata wallahi kin burgeni da ki ka masu haka da sun bar mana gida babu kowa.”

“Ke yanzu mai makon ki yi mata faɗa sai ki zauna kina gayamata ga ra da ta yi haka?”Inji Iro.

Cikin dariya Husna ta ce,”My Kakus gani nayi sun bar mana gida shiru babu kowa amma yanzu ga shi har sun zo.”

“Gaskiya wannan yarinyar sai an chanzoki wallahi ina sauraren maganar gabana na faɗuwa wallahi ba ki yi ba,”Abdul Dabai ya faɗa yana dariya.

“Kai My Husna gaskiya kin tsorata mu da yawa,”Inji Anty Maryam ta faɗa ta na dariya.

“Ke dai bari Sis ni kaina ba ki ji yadda na tsorata ba wallahi da naji salatin,”Fadila ta faɗa ta na murmushi.

“Wannan yarinyar gaskiya kin raina mutane muna aiki amma ki ka sanya muka bar aikinmu akan wannan shirmen!”Iro ya faɗa cikin jin haushi.

“Haba Yayana ba ga shi yanzu har kun zo ana magana ba ai Allah ya ma jikata albarka,”Hadiza Muhammad ta faɗa.

“Ke kike sanyata take raina mutane kenan to zan sanya a je har gida a yi mata ɗaukar amarya,”Iro ya faɗa.

“Wallahi Husna da ina kusa da ke yau da sai kin sha bugu saboda naga rashin bugune ke damunki,yarinya duk kin bi kin raina mutane to zamu yi maganinsu,”Abdul mai kasuwa ya faɗa.

“Kina wuta Husna gaskiya ina yin ki ko garin babu kowa,gaskiya da gaske ke ɗin ce farin cikin ƴan amana,”Mustapha Madina ya faɗa.

“Yauwa musty shi ya sa nake sonka,ka dai faɗa masu idan su sun manta ni ce farin cikinsu,”Husna ta faɗa.

“Ina farin cikin yarinya kin zo duk kin ta da mana hankali sannan za ki kira kanki da farin cikinmu?” Iro ya faɗa wanda da alama har yanzu bai huce daga cikin haushin da ya ji ba.

“Kai Iroro wai kishi kake da ni?ko dai ana so ko ba’a so dole ni ce farin cikin ƴan amana dan haka Malam ka haƙura kawai kayi mubaya’a!”Husna ta faɗa da son ƙa ra hayaƙa Ibrahim.

“Dallah Malama ki je ki kwanta duk kin dame mu da hayaniya,”Inji Iro.

Cikin dariya Husna ta ce,”kan ka ake ji Malam ni ban da lokacinka!”Inji Husna.

“Ke waye ba ki da lokacin na sa?” Inji Iro.

 

Hussy Saniey.????
*RASHIN ADALCI 2021*

*NA*

*HUSSY SANIEY*

*____________________________________*

*????????AINUWA ????RITER’S✍????*
*????SSOCIATION????????*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*????????

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*

 

*PAGE 10*

 

Husna sai dariya take ita ɗaya saboda ta san yau ta hassala Iro,idanuwanta suka sauka akan saƙon da Iro ya turo mata yanzu cikin sauri ta buɗe,gani ta yi ya ce mata,”ke dai kin raina mutane saboda kin ga kowa na tattalinki ba kamar waccan Kakar ta ki.”

Husna cikin dariya ta maida ma shi da amsa,”Haba sweet Irona ta ya zan raina ka ai ban isa ba!”
“Haba yarinya daga baya kenan wallahi ki kiyaye haɗuwata dake saboda har yanzu gabana bai daina faɗuwa ba nayi tunanin mutuwa za ki sanar amma shine za ki zo da wannan shirmen!”Iro ya faɗa da alama har lokacin bai gama sauka ba.

Voice Husna ta danna ta ce,”haba sweet Iro tuba nake kasan ni da kai five and six ne,ka tausayaman mana ka yi haƙuri,” ta tura masa tare da sake ƙwashewa da dariya.

Amsa ya maido mata da cewa,”haba yarinya za ma kiyi bayani idan na riƙe ki dan haka ki roƙi Allah kada mu haɗu shine kawai mafita amma idan dai muka haɗu sai kin gane shayi ruwane yarinya.”

Cikin marerecewa kamar ta na a gabansa ta tura masa da saƙo kamar haka,”haba Sweet Irona kai fa nawa ne dan haka ka da ka bari wasu su ji su yi mana dariya mana kaji Sweet Irona.”

Bayan kamar minti biyu Ibrahim ya sake turo da saƙo ya ce,”yarinya duk wannan marairecewar ba amfanin da za ta yi dan haka ki ma daina kawai ki jira sakamako.”

Ƙara shagwaɓewa Husna ta yi kamar ta na a gabanshi ta ce,”dan Allah Sweet Irona kayi haƙuri ka ga dai ni taka ce nasan kuma a kowane lokaci kai mai tausayine a gareni dan Allah Sweet Irona na tuba bazan sake ba ka ji sweetyna!”

Amsa Ibrahim ya maido mata da ita ya ce,”yarinya kin yi sa’a zan tausaya maku saboda ka da Mama ta shiga damuwa idan na sanya aka maki ɗaukar amarya dan haka kin ci albarkacinta.”

Husna na duba saƙon cikin sauri ta maido ma shi da amsa ta ce,”lalle ma Sweet Iro to aikuwa tunda ka ce haka ban tuba ɗin ba,gobe ma sai na ƙa ra yin wanda ya fi wannan ɗin!”

Dariya Ibrahim ya yi saboda da ma yasan halin Husna zai yi wuya ta bari a gane ta karaya akan abu,sai da ya tsagaita da dariyar sannan ya ce,”haka ki ka faɗa ko?”
“Eh haka na faɗa ka ɗauki mataki!”Husna ta faɗa.
“Ki ka sake mai-maita wa kuma?”inji Ibrahim.
“Eh yadda ka ji haka na faɗa ko akwai damuwane?”Husna ta faɗa.

Dariya Ibrahim ya kama yi sannan ya ce,”haba Sweet Husnata ni ne fa Sweet Ironki!”
“Bawani Sweet Irona bayan sai lallashinka nake amma ka ƙi yin haƙurin sannan za ka wani ce kai ne nima ai Ni ce!”Husna ta faɗa da alamun ta fara hassala.

Ibrahim na ganin wanann saƙon ya san ta hassala,dan haka bai sake tura mata wani saƙon ba sai waya ya kirata,amma ta ƙi ɗauka sai ma ta rinƙa datse kiran,sun yi haka ya kai sau goma,daga ƙarshe ma wayarta ta kashe gaba ɗaya.

 

Hussy Saniey.????
*RASHIN ADALCI 2021*

*NA*

*HUSSY SANIEY*

*____________________________________*

*????????AINUWA ????RITER’S✍????*
*????SSOCIATION????????*
“`{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}“`
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*????????

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*

 

*PAGE 11*

Husna na kashe wayar ta kama dariya saboda tasan Ibrahim na chan yana ta kiran wayarta,ta san duk lokacin da suka yi irin haka hankalinsa tashi ya ke sosai,Husna na cikin tunanin yadda hankalin Ibrahim ke tashi idan ta yi fushi sai ta ji ƙaramar wayarta na ƙara,ta manta shafi ba ta kashe wayarba,duk da dama ta yi tunanin shine amma ta na ganin lambarshi ce sai da taji gabanta ya faɗi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button