SALON SO 47-48

???????????????????????????????????????? ???? SALON SO ????
????????????????????????????????????????
BOOK ONE ????
Story & written by
Mommyn fareesa
????️47&48
………mr Aliyu suna a cikin mota shida khaleel a back sit”koda khaleel yahango imaan ita kad’ai”yak’ara tabbatar da zargin sa akan mr Aliyu “son yasmeeen yakeyi mai tsanani….tunda yana nuna kishinsa akanta
A anguwar G R A suka ajiye khaleel kafin su wuce gida”
gaba d’aya mr Aliyu beda wata nutsuwa”tunanin yasmeeen dason ganinta dajin muryarta sun addabesa”ga tsananin zafin ance anganta da wani na damunsa”
wanda shida kansa yanama kansa tambayar meyasa bayason ganinta da kowa?”
Ruwa ya watsa ya wuce masjeed bebi takan imaan ba”
bayan ya idar da sallar isha’i,ya siyowa imaan kaji da ice cream”
Lokacin daya shigo parlourn imaan na waya da yaya khaleel”
tana ganinsa takashe wayar”tab’e baki yyi yana zama gefenta”
ya ajiye mata ledojin”ta kwanto ajikinsa tana kukan shagwab’a”tsintar kansa yyi dajin inama ace yasmeen ce haka ajikinsa tana masa wannan shagwab’ar….
baby zan tambayeki kifad’amun gsky kina jina?”
Eh yaya zan fad’a maka idan nasani”waye da marece yaje gun yasmeen agidansu??”
nidai k’awar ta nasamun lalle muna zaune ad’akin umma sai yashigo”
Duk muka gaishesa, yagaishe da umma”sai yajuya yafice”
babu jumawa Ahmed yashigo cikin d’akin da gudu yace”.anty yasmeen wai yaya hamza yace”.kizo yana soro”
sai naga anty yasmeen taja tsaki tana cewa ita bbu Inda zataje”
Umma ta harareta tace”.maza ta tashi taje”to sai naga ta tashi taje”kusan 3O minit tadawo”
Iya abinda nasani kenan”ajiyar zuciya mr Aliyu yasaki”sbd yama fahimci yasmeen batada laifi” tajene sbd tayiwa umma biyayya”gashi takirashi yakashe mata waya”
tausayinta yaji sosai aransa” hakan yasa yatashi tsaye bece wa imaan komaiba”yawuce sashensa”
kwanciyar sa yagyara akan royal bed nashi”yyi calling d’in yasmeen….
yasmeen kuwa tun bayan tafiyar imaan tana cikin damuwa sosai”taku maji haushin mr Aliyu dabaice tazo koda gaisawa suyiba”sbd bata daraja da matsayi agunsa shine y’ar uwarsa kawai yanema”
hakan yabata haushi sosai da sosai”tasha kuma alwashin gobe baza taje gidansu ba”
tagama shirin kwanciya bacci tayi addua ta kwanta tun 8:45 pm”
wayarta ta d’auka da nufin tahau online,kiran mr Aliyu yashigo cikin wayarta”
harta tsinke ba’ta d’aga ba”yakoma kira har sau 3 duk ta share”
dafe kansa yyi yad’auki gudar wayarsa yana cewa”my yasmeeen tayi fushi dani” yasaka number d’in ta”
yad’auki kusan 15 minit tukum yasaka kira”
yasmeen kuwa haushin kanta taji akan k’in d’aga kiransa datak’iyi “dukda k’asan zuciyarta na nuna mata ajinta taja”
wani kiran yasake shigowa da bak’uwar number”azaton ta koma shine sai taga bak’uwar number”
kamar k’arta d’aga”tadai daure ta d’auka tanayin sallama anutse”
wata iriyar ajiyar zuciya mr Aliyu yasaki”ahankali yace”.my yasmeeen!!
kukan zan tasaka tak’i mgn”gaba d’aya duk ta susutashi da shagwab’ar ta”
Murya can…..
Ayi hak’uri da kad’an banida caji????
[ad_2]