TAKUN SAAKA COMPLETE HAUSA NOVEL

TAKUN SAAKA 13

  •  *_Typing????_*

*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

_________________________

*_MACE SAI DA GYARA_*????????????????

 *Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*

_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawa nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki._

*_Muna da haɗin_*

_Turaren wutane_ 

_Humrh_ 

_Kulacham_

_Turaren wanka_

_Turaren Kaya_

_Gyaran jiki_ 

_Na amare_ 

_Da masu jego_

_Da sabulai masu gyara fata_

*_Da magungun nan mata_*

_Irin su kaza_ 

_Tantabara_

_Tsumi_

_Gumba_

_Zuma_

*_Duka akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan ????????_*

Wushishi road KADUNA

08067807620

09057713999

_________________________

*_Chapter Thirteen_*

…………Gaba ɗaya jin su Hibba ya ɗauke ɗaf a cikin kunnuwansu lokaci guda. Dukansu sun zuba masa ido tamkar waɗanda sukai gamo da wata baƙuwar hallita. Namiji ne tsayayye da za’a iya kiransa namijin gaske a kowacce irin nahiya ko ƙabila. Sanye yake cikin shadda oxblood da ta fidda ainahin kalar fatarsa mai sheƙi. Fuskarsa cike take da ƙasunba da wani madaidaicin gemu mai kama da na gayu irin na ustazan wanan ƙarnin (????Bily????). 

       A kallo ɗaya zaka fahimci rashin son hayaniya daga garesa. Da alama kuma ba mutum bane mai yawan sakewar fuska a mu’amula ko a yanayi.

         Ganin sun shagala wajen kalon sa ya saki wani shegen murmushi yana ƙarasa takowa gaban Hibbah gab. Haka kawai takaici ya kama Hibbah da kallo guda tai masa ta ɗauke kanta tun ɗazun. Cikin ɓata fuska da yatsineta ta ce, “Malam lafiya? Tun ɗazun ka ke ta binmu sai kace wani mai gadin mu”.

          Murmushi ya kuma saki, jerarrun haƙoransa farare na bayyana. Ƙoƙarin saka ƙwayar idanunsa cikin nata yake, amma sai taƙi. Sai ma harara da ta sake zuba masa ta ɗauke kai. A hankali taja siririn tsakin da yasa Hafsat da Zahidah shurin ƙafarta da galla mata tagwayen mintsini.

          “ALLAH ya isa”. Ta faɗi tana hararsu bayan ta saki ƴar siririyar ƙarar data saka baƙon nasu ƙyalƙyalewa da wata dariyarsa da ke fita a nutse. Harara ta sake zuba masa zata bar wajen yay saurin shan gabanta.

         Haushi ya sake kama Hibba. A tsiwace tace, “Malam kana shigarmin hanci fa”

       “Ba malam ɗin bane ai. *_Muhammad Shuraim Aliyu_* ne. Idan kina son nabar shiga hancinki address da number kawai nake buƙata”.

       “Baka da man kai” ta faɗa tana raɓawa ta gefensa ta wuce batare da ya samu koda harar ba yanzun. Badan Zahidah da Hafsat sun so ba sukace masa (bye) suna bin bayanta. Motarsa yay azamar komawa ya cigaba da binsu duk da uban sauri da Hibbah ke zabgawa tamkar zataci da ka. Jitake a ranta da da akwai lungunan da zatabi ya kaita gidansu da shi zatabi dan taga ƙarshen naci. Sai dai kash, tun daga islamiyyar har zuwa gidansu layine ɗoɗar. 

        Itace ta fara shigewa gidansu, dan ata wannan hannun itace farko kafin su Hafsat. Dan haka mai mota Shuraim ya tsayar da su Zahidah. Dole suka tsaya dan baiyi kama da wanda za’a cigaba da yarfatawa ba. 

         “Kuyi haƙuri fa na takura muku, naga mahaɗi nane babu damar yin sakaci. Dan ALLAH miye sunan ƙawarku?.”

       Kallon juna Hafsat da Zahidah sukayi. Roƙonsu da ya sake yi ne ya saka Hafsat cewa, “Muhibbat! Aliyu Hamza”.

          “Masha ALLAH, nice name. Nan ne gidansu?”.

     A taƙaice suka bashi amsa da eh. Shima sai bai sake jan zancen ba yay musu godiya ya koma motarsa ya wuce.

           “Gaskiya Hibbah ƴar yawa ce, amma fa guy ɗin nan ya haɗu ALLAH. Yaci sunansa Muhammad Shuraim”. Zahidah ta faɗa tana lumshe ido.

       Hafsat tace, “Shiyyasa ai na faɗa masa sunanta. Waya gaya mata ana sakaci da irin waɗan nan gayun a wanan ƙarnin.”

        “Barta ai zamuyi maganinta. ALLAH dai yasa har a hallaya haka yake, da kuma zancen aure yazo mu raƙwashe. Dan zanso Hibbah ta auri guy ɗin nan kodan ta kere sa’a a cikin shaggun su Amlah ɗin gidansun can. Masu shegen kakkafi da son asani. Su adole suna hawa motoci. ALLAH idan suka ga guy ɗin nan sai sun haukace. Sai dai kuma ya musu nisa da na Hibbarmu ne”.

       “Insha ALLAH”. Cewar Hafsat tana ƙyalƙyala dariyar mugunta. dan harta hango idon ƴan gidan su Hibbah da kullum suke mata iyayi akan su sun waye, sun girmeta. Suna hawa motocin da Abbansu ya saya musu su ƴaƴan so banda Hibbah.

★_____________★____________★

            A ɓangaren Master kam tunda suka koma L.E street shida yaransa sukai luf abinsu tamkar basa ƙasar. Da wannan damar jami’an tsaro suka sami na barazanar cewar ya tsorata da harin da suka kai masa ne, ƙilama sun sami nasarar kashesa dan sun harbesa.

      A lokacin da yaga wannan rahoto ba ƙaramin dariya abin ya bashi ba ƙwarai da gaske, ya saki wani malalacin mmurmushi mai ƙunshe da ma’anoni masu yawan gaske da shi ya barma kansa saninsu. Har cikin ransa yana mamakin sai yaushe ne ƙasarmu ta gado zata canja ne? Ji dai shareriyar ƙarya da wanɗan da suke amsa sunan iyaye manyan ƙasa suka karkace suka gilla dan kawai su burge su kuma kankaro ma kansu girma.

       Yaransa kansu abin ya basu dariya. Har cikin ransu suna tausayin ranar da Master ɗinsu zai maida murtani ga waɗan nan mutanen. Inhar bai kaisu kwance ba tabbas sai ya sakasu kuka da hawayensu ko su ajiye aikin koda lokacin ritaya ɗinsu baiyi ba. 

                 Shi ba’a sakashi yin abu dole, dan haka baice uffanba sai ma sake lafewa da yay domin tabbatar da zancen nasu. Yayinda a gefe kuma idanunsa ƙur akan batun matar gwamna da hukumar sa’ido akan ta’annati da kayan gwamnati take bin cika har yanzun. Jira suke suyi wani sakaci ko kaɗanne ya sake bankaɗo wasu surukan nata ma duniya harma da su kansu…

____________★__★__★___________

           

           “K kuma lafiya kika shigo kina cikama mutane baki da iska?”. Ummi ta faɗa tana kallon Hibbah da dawowarta kenan da ga islamiyya.

      “Babu komai Ummi. ALLAH yunwa nake ji ne”.

           “Shi abincin da kika tafi da shi fa?”.

       “Ummi naci fa. Kawai wata yunwar dai nake sake ji”.

          “To ALLAH ya ƙyauta, sai kije ki fara yin wanka kiyi salla sannan kizo kici”. 

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button