HAUSA NOVELSAMARIN SHAHO Complete Hausa Novel

SAMARIN SHAHO Complete Hausa Novel

So Kafin yamma har hajiya billy ta amince tayi ma ummahm gayyatar secret programe din da yazeed din yake shirin yi
Da sunan idan suka hado suma anan sai ayi maganan auren formally
Asa a jarida sai ya dawo kamar babban events da ci gaba ma kungiyar su…

Yazeed ya shawo kan Iyayen sa ne da cewa ai hakan zai dada sa shi ya wanke zargin sa da na sarah a idanun mutane kamar yadda su alhj nafiu suke gani..

A nan wajen sarah kuma ta dauka har gida za’aje a same ummahn nata ayi magana batare da kowa yaji ba

Sai ya mata proposing dinner
Akan suje su dan yi discusing muhimman abubuwan da zai faru idan iyayen su suka bada go ahead na auren su cikin kwana biyun nan

Tunda ta sanar da hapsys asalin shawarta sai taga rashin jin dadi a fuskan ta amma tayi mata fatan alheri,

Sai dai bata ji dadin ranar ba sam sabida tasan cath tayi fushi da zabin ta sannan hapsy ma ta san bata so har ranta
Every one around her become cold with her.

But she knws that auren yazeed its the sad truth that she must have to accept

Gani take kamar don basu san komai game da rayuwarta na baya bane ya sa suke nuna hakan..

So bayan ta tashi a aiki sai suka fiice da yazeed din Anan yake kawo
Mata cewa idan har yau iyayen sa da nata sunyi magana to lallai ranar juma’an nan zasu zama miji da mata
Dats ranar da ya gama shirya secret partyn nasa

Thats in Just 69hours time daga lokacin

Ummah kuwa anata bangaren ta kasa samun nitsuwa sai da ta kira mahfud akan yazo ya same ta har gida suyi magana..

Baiya jin dadi amma haka ya taso ya zo gidan chan da yamma
Ya same ta…
Itakam Bata yi kasa a gwiwa ba
Ta nuna masa exctly abunda ke zuciyan ta game da auren sarah da wanda ta zaba

Har ta kawo masa sugestion cewa in har bazai damu ba ita zAta sa sarah ta yi mata biyayya ta aure shi…

don ta zauna tayi ta tunani sai ya kasance ko wani awa tsakanin jiya da yau take warware dalilin ta Take kuma ganin hankalin ta zai kwanta da shi din duk dama tasan
Yasan ita wacece..

Da mamakin ta sai yaki amincewa da hakan, ya kuma nuna mata cewa zabin sarah shine abun dubawa yanzu ba son ransu ba shi sam baya son ya takura mata ta zauna da shi..

Tausayin sa gaba daya ya addabae zuciyan ummah duk ta rasa ya zatayi da wannnan lamarin..

Haka ya rika lallashin zuciyan ta akan maganan ya kuma nuna mata cewa zai yi hakuri..

Amma jin da yayi ta kawo maganan iyayen yaron suna son auren da wuri

Sai ya sa shi dole ya fada mata bazai samu daman halartan auren ba..

Bata sha mamaki ba don taga hakurin sa da nagartan sa ..
Ba a gane hakurin mumuni na kwarai dama sai abu uku sun same sa

Yunwa…heartbreak da kuma cuta..

Daf Daga bakin kofa sarah ke ji sallamar sa da ummah..
Cike da masa adduar Allah ya haskaka rayuwar sa ya bashi wanda ta dace da shi fiye da yarta suka yi bankwana..

Tayi hawaye sannan ta sa ya mata alkwari wata rana zai zo ya dube ta..

Sosai ta so ta sa shi kuka amma bazai iya ba don baya so ya bata expression din halin da yake ciki..

Koba komai yasan ya samu soyayyar mutane nagari a rayuwa…sai yayi kokarin ajiye rashin samun soyayyar sarahn a matsayin jarabawan sa wajen ubangijin..

Yana fita daga bakin door bayan ummah ta koma yaji an kamo hannun sa…

Cikin sanyin jiki ya juyo ita kam ta dade anan bayan dawowar su da yazeed tana jin maganganun su da ummah.

Da suka hade ido sai da yaji wani sabon karayar zuciya amma sai ya daure ya rufe shi da murmushi ya ce mata ya kike?
Bata amsa ba sai tace masa “hero pls dont go away…

Abun sai ya dada sa shi murmushi,ya ja hannun sa daga nata”

Yace ni zan tafi sarah..U shud take care of ur mum Allah ya bada zaman lpya..

Zai juya tayi saurin shan gaban sa cikin damuwa da son Ta ruda sa da hawayen ta

Tace ” kenan zaka tafi ka bar rayuwata don a
nace zan auri wani mahfud?

But why?arent we suppose to be there for each oda? wahts wrong with you….ta karashe adan razane idanun ta sun wanke fuskan ta da hawaye.

Sai yaji ya kasa yin komai nitsuwa ne ke taho masa na ban mamaki ya jiyo ya dube ta yace”
Kiyi hakuri sarah.
Nasan lokaci da yawa mun tsaya ma juna amma zan so kimin uzurin wannan bazan iya halartan auren ki da wani ba sabida ina son ki”

Kamar zata hadiye ranta ta ke janye kukan nata dake fitowa silently

Cikin Dauriya tace ni dai banga dalilin da ya sa haka ba,kawai kace dama so kake ka barni
And Thats so unfair you know

Yasan tana cikin tsananin damuwar rabuwar su ne take fadan haka,he knws that tana son shi har yanzu amma tunda son wani ya take nashi sai ya sa dole ma ya hakura kawai

Yace aha”ai ke da kanki kinsan akwai matsala idan na zauna da kaunar matar wani araina bayan nasan itama tana so na

U told me yestadey tht i dont dersrve that from you, so meyasa kike tunanin zan miki haka?
Is it not better if am no where to be seen in your life?

Kinga ke da mijin ki bazaku samu wani mixed feelings ba..ko ba haka bane heroine?

Ta dago tana kallon sa
Ita kadai tasan baya jin dadi ko kadan a zuviyar sa..
He’s really heartbroken and pained
Gaba daya sai ya sama ta tsoron hukuncin da ta yanke makanta again..

Ganin tayi shiru ya sa ya juya shima ya shige motar sa.

Anan ta daskare tsaye tana kallon sa har ya fice ya bar haraban compound din

Ko kafin ta kai dakin ta zazzabi ne mai zafi ya rufe ta wanda ya hanata bacci har washe gari

Bata samu taje aiki ba ma sai da ummah ta shigo take fada mata shirin da iyayen yazeed din suka gayyace su acahn hall din

Ta kuma mata bayanin extly kamar yadda suka mata

So yazeed want the weding to be special har haka?

This is just like an official engagement ta san yana so ya bayyana ma duniya ya mallake ta ne..
Tayi kwafa tare da ajian zuciya mai nauyi

Ciki ranta tace pooor me ni ina nan ina fama da rashin masoyi na kai kana chan kana famar shirin sabuwar rayuwar mu..
Allah dai yasa hakan shine mafi alheri…

nan bangeran su mahfud kuwa shi da yazed suka riga sun kulla shirin su

Yazeed ne ya goya masa baya da ya nuna masa yana so ya tafi gida abunsa ko zai mance da damuwar sa…
Inyaso wata rana zai dawo musu

Shima yazeed din so yake mahfud ya tafi ko zai dena jin haushin ganin sa hakan..

Gashi baya so yayi duk wani plan din sa da yake shiri a goben agaban mahfud

Don Yasan bazai goya masa baya ba duk dama yasan mahfud bai san yarinyar ba

gashi dama su mum basu gaya masa komai ba tukun..Sai tacee kar a dame danta da maganan banza sabida dama ita yanzu ba son auren da sarah take ba

sannan yazeed bai fito filj ya gaya musu komai da komai game da shirin goben ba
Su dai sun san zasu hadu da iyayen sarah..

Nn kuma Da kyar su ka
Karbi uzurin gaghawar komawar mahfud din germany..

Don sai da suka hada musu da karyan cewa zai dawo da wuri…kafin suka saduda

So washe gari da safe in just 4hrs left to the game of love party

Yazeed ya raka mahfud airpot

Inka gansu kyawawa kamar su suka kera kansu cike da bawa juna gwarin giwa suke tarairayan kansu..

 

Inda yazeed din ke tabbatar ma mahfud cewa nan da sati biyu ma zai iya ganin sa don yana sa ran zai zo paris yayi engaging safeenah burdurwan sa…

 

*SARAH idan da kinsan shirin da sis sadnaf tayi miki jiya da kin kashe kanki kawai???????????????? ahhh my god sis ur coments are drunking me mad*

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button