SARAN BOYE 73

No. 73

………….A yau kam su Nu’aymah da duk wanda yasan da wannan shirin sun tashi a shirye tsaf bisa yaƙinin tarkon da suka ɗana ya ɗanu. Kasancewar sanyi da akeyi duk sauran jama’ar gidan da ƴan biki suna can a sassan gidan a maƙale, duk da madai ƴan bikin da suka rage duk na jikine babu bare. Babu kowa a tsakar gidan sai yaran Jay dake ɓoɓɓoye.
         Yau kam Jay ya shiga har falon baba malam tare da lauyan malam mahaifin su baba malam a zuwan zasu tattauna akan kaddaririn baba malam ɗin. Acan kuma ta waje little bee ce da wasu jami’a a harabar gidan a mabanbanta wajaje duk da Jay yasan akwai camaras ɗin da Afrah ta saka masa a wancan zaman. Yafi buƙatar gani ga ido ga kowa kafin ya bankaɗa sirrikan dake a cctv ɗin. An kira Aymah da Yoohan falon, sai su Abban Abdallah da hajjo data san komai itama. Sai Omar da yazo matsayin lauyan Nu’aymah shima.
       Bayan buɗe taro da addu’a baba malam ya fara da nasiha a garesu duk dai a cikin salon tarkonsu, dan a zahiri fa babu wani maganar mallakama Nu’aymah kaddarorinsa da yakeyi. Shirine kawai irin nasu Jay.
      A gefe kuwa idanun su Yoohan gaba ɗaya na’a Windows ɗin falon a kaikaice. Baba malam kuwa na cikin nasiha sai ga abinda suke jira ya bayyana. Kallon juna sukai shi da Jay dasu Yoohan sukayi murmushi. Daga haka ya cigaba da bayaninsa hankali kwance.

        Acan waje kuwa su Little bee na mammaƙale a maɓoyarsu sai ga mutum sanye cikin dogon hijjab har ƙasa da niƙab ya fito daga tacan bayan gidan yanda babu mai iya fahimtar daga ainahin sashen da aka fito. Basu da tabbacin mace ce ko namiji, dan komai an rufe ba’a gani.
      A yanda mai laɓe ke tafiya da dabaru zaka san cewar lallai an ƙware, sannan aikine da akeyi tunba yanzuba. Cikin salon iya aiki Little bee taima abokan aikinta wani salo da yatsun hannunsa suka bada ɗass!! Sau ɗaya. A take duk suka ƙara shiryawa dan suma dai suna biye da mai laɓe akan idanunsu.
       Sai da suka tabbatar mai laɓe ya isa dai-dai sashen Malam marigayi alamar dai ɗan gidanne, tunda har ansan a ina su baba malam zasuyu taron nasu aiko sai wanda yasan gidan. Kamar yanda mai laɓe ya saba a koda yaushe ya isa jikin Window. Wani siririn abu ya saƙa a tsakanin glasess ɗin Window ɗin da alama na ɗaukar magana ne. Dan yana gama turashi ya kai hannu ya taɓa kunnensa alamar tabbatar da daidaitar komai. Ƙaramin tsaki akaja jin Nasihar da baba malam ya fara dan ba ita ake buƙataba a yanzu. Jin baba malam zai fara jawabinsa mai laɓe ya ƙara nutsuwa da maida hankalinsa ga window ɗin domin saurare..
         Da wannan damar su Little bee sukasamu isowa wajen cike da ƙwarewar aiki suka toshe gaba da baya na ɗan siririn lungun bayan ɗakin malam marigayi. Ƙarar saƙon daya shigo wayar Little bee daga Jay ne ya fargar da mai laɓe ya juyo da sauri. Sai kawai ganinsa yayi zagaye da mutanen da baisan ta ina suka ɓullo ba.
      Tashin hankali ba’a saka maka rana. Wannan shine ɓoyayyar kalma a zuciya da bakin mai laɓe duk da bai fito ya furta manaba a zahiri. Dan kuwa dai gabas da yamma kudu da arewa babu wajen guduwa. Katanga a bangon gabas. Ginin sashen malam a bangon yamma. Little bee da jami’ai uku a bangon kudu duk sun nunasa/ta da bindiga. Dawood da jami’ai uku shima a bangon arewa duk sun nunata/sa da bindiga nanma.
     Wannan itace kwana casa’in da tara ta barawo ɗaya tak ta mai kaya. Little bee ta ciwo wayarta da hannu ɗaya a aljihu ɗayan kuma riƙe da bindigar data nuna mai laɓe. Kiran Jay tayi a waya. Yana ɗagawa tace, “Sir! Aikinmu ya kammala zaku iya fitowa”.
       “Woow!” Jay ya faɗa yana miƙewa idonsa akan su baba Malam. Takawa yay jikin windown da yake hango inuwoyinsu ya zuge gilas ɗin tare da net. Abinda mai laɓe ya saƙala ya faɗo. duƙawa yay ya ɗauka yana jujjuya shi a hannunsa kafin ya kalli su baba malam da suma duk shi suke kallo.
           “Malam zama ya ƙare ai, suspect ɗinmu yazo hannu zamu iya zagayawa”.
    Harga ALLAH sai da gaban baba malam da Umm ya faɗi. Hakama Aymah duk sai taji tsoro kuma. Su Abba Musbahu da basusan mi akeyiba suka shiga kallonsu da tuhuma. Ko a jikin Yoohan da Umar. Dan sunema farkon ficewa a falon.
    Baba malam dake kallon su Abban Abdallah yace, “Kuyi haƙuri wannan itace kawai mafita a garemu gudun kar wataran a kai ga rasa rai bisa makircin da bamusan wake ƙullasa ba”. Daga haka yay gaba ya barsu da kallon kallo ma juna sai dai ganin kowa ya fice suma sukabi bayansu jiki a sabule.
      Ganin duk sun iso Little bee ta dakama mai laɓe tsawa da faɗin, “Cire Niƙaf”. Ko motsi ba’ayiba. Sai dai yanayin tsayuwar ya tabbatar da koma wanene a tsorace yake kuma cikin ƙololuwar tashin hankali da firgici.
       “Inada cikaken dama nayin harbi, hakan na nufin bullet ɗin zasu iya fita a cikin bindigarnan zuwa jikinki/jikinka a koda yaushe. Zan irga iku kawai bisa lasisin dama a gareki ko a gareka. Ɗaya! Biyu! Uku!!” ta fita daga bakin Little bee tare da bullet ɗinta zuwa ƙafar mai laɓe da ko motsi baiyiba balle ya nuna kota nuna zata cire nikab din da aka bada umarni.
     A take ƙarar muryar mace ta karaɗe gidan saboda azaba shigar bullet. Ƙasa ta durƙushe jiki na rawa. Da wannan damar Little bee ta ƙarasa gareta tasa hannu ta fisge niƙab ɗin ta jefar gefe. Baba malam da Umm da sauri suka kauda kawunansu gefe da tsananin fargabar tsoron ganin koma wanene. Sai da Nu’aymah ta furta,
       “Illalillahi wa’inna ilaihirraji’un Addah!! Kece dama?!!!”.
     Sannan su Umm suka juyo a firgice. A take wajen gaba ɗaya ya ɗauki salati. Dan duk jama’ar gidan kururuwar ihun Addah da Little bee ta harba dama duk ya fito dasu a hautsine.
     Cikin girgiza kai hawaye na sakkoma Umm a guje tace, “Inaa bazai yuwuba. Addah ki sanar musu ba abinda suke zargi bane ya kawoki nan. Dan ALLAH ki tabbatar musu domin bamu kariya kema kika zo nan. Ki tabbatar musu bake bace kike laɓen nan dama can dan ALLAH, kicemin yau kika farayi……”
      “Bata da bakin baki waɗan nan amsoshin domin wanke kanta Umm-Muhammad. Domin kuwa duk saɓaninsu da baki eson ji daga bakinta sune gaskiyar amsoshin naki da ma kowa dake anan wajen”.  
     Bily dake kusa da Jay tsaye ta bama Umm amsa kanta tsaye.
        “Karkice dani haka Maman Awwab. Dan ALLAH karkice haka. Wannanfa Fauza ce, wadda muka tashi tare tun ƙuruciya tamkar uwa ɗaya uba ɗaya ta haifomu. Ban taɓa ɓoye mata sirrinaba, itama bata taɓa ɓoyemin nata ba. Tare muke raba farin ciki, sannan mu raba kuka tare idan ya samemu…..”
         Murmushi Bily tayi da takawa a hankali zuwa gaban Addah daketa faman magowar azabar ƙafarta dake zubda jini. Ta nunata tana mai kallon Umm ɗin, “Tabbas a zahiri haka take a gareki Umm-Muhammad. Amma a baɗini itace babbar maƙiyyarku. Idan kuna buƙatar tabbatarwa mu a shirye muke wajen nuna shaidar gani da ido a gareku dan duk mun tanajesu dama”. Ta ƙare maganar tana duban su baba malam da alamu ya nuna tamkar duk sunyi sumar tsaye ne har yaran Addah da duk suma suna a wajen.
      Daga haka Jay ya bama Yoohan da Omar damar cire bullet ɗin jikin Addah. Cike da ɗacin murya Yoohan ya dubi Jay ɗin idanunsa jazur. “Uncle ka gafarceni, hannuna bazai taɓa iya aikata jinƙai ga maci amana ba”. Daga haka ya kama hannun Nu’aymah da jikinta ke karkarwa suka bar wajen.
      Murmushi kawai Jay yayi. Baba malam zaiyi magana Jay yace, “Karka takura masa Malam. Umar Please ka cire mata sai mu wuce da ita. Malam sai ku samemu a statlon ɗinmu nan kano mu ƙarasa maganar”.
       Da sauri baba malam yace, “A’a Jawaad ina neman alfarma komi zai faru muyisa anan cikin gidan domin rufin asirinmu, wannan itace alfarmar da zan nema a gareku”.
     Ɗan jimm Jay yayi, sai kuma ya kaɗa kansa alamar karɓawar alfarmar baba malam ɗin.
     Badan Umar yaso ba ya amince zai cire. Dan haka aka ɗakko Adda daga lungun zuwa sashen Malam. Gaba ɗaya yaran sa’an su Muhammad zuwa kansu Adawiya ba’a barsu sun shigaba. Duk da kuka da Adawiya keyi iyakar ƙarfinta wanda babu wanda yasan dalilinsa. Su Hajarah da sauran yayunta na ma’auri duk suna gidajensu basusan abinda akeyiba. Sai malam ƙarami kawai da sauran ƙannensu. Shiko gaba ɗaya da alama ma jinsa da ganinsa sun gushe dan bai iya motsawa a lungunba har kowa ya fice. Hakama Abba Mustapha saida Hajjo ta kama hannunsa da kanta saboda tsabar firgici.

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button