SARAN BOYE 76

      Lokacin da su Yoohan ke wancan dabi shi da madam Chioma su Nu’aymah suna shigowa cikin hotel ɗinne tare da jami’an tsaro. Dan tuburewa tai akan saita biyosu. Ganin yanda ta rikice ɗinne ya saka Omar bada shawarar aje da ita ɗin. Sai da jami’an tsaron sukai magana da manager ɗin hotel ɗin sannan suka nufi cikin hotel ɗin kamar yanda alama ke nuna musu dai-dai inda wayar Yoohan take. Wadda toshewar basirar madam Chioma baisa ta kawo a ranta sanadin wayar ballinsu zaiyi ruwa ba.
        Dai-dai madam Chioma ta ɗora kanta saman wuyan Yoohan tana shinshina kamar wata mayya ko tunkiya, hannayenta duka biyu na akan jikinsa. wani irin masifar tafasa zuciyar Yoohan keyi tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito waje. Sai ko faman taunar lips nashi yake da masifar ƙarfi, a ɗaure yake, bashi da wata damar ɗaukar mataki akan uwar tasa…..
       Da sauri ta ɗago saboda jin an buɗe ƙofar. Hakama yaranta dake tsaye a gefe kawunansu a ƙasa duk zabura sukayi suna rarumar bindugunsu…
       “Ƙasa gaba ɗayanku, duk wanda ya taɓa wata bindiga anan kuwa a bakin ransa”.
    Ɗaya daga cikin jami’an ya faɗa a tsawace yana nuna yaran madam Chioma. Da sauri ta fiddo tata ƴar ƙaramar bindigar jikinta ta ɗora bisa kan Yoohan daya buɗe idonsa a hankali ya sauke su akan Nu’aymah da ke shigowa tare da Jami’an.
       Cikin rawar jiki data murya Madam Chioma tace, “Ku fita a ɗakin nan kona tarwatsa masa kwanyar kai duk da kasancewarsa ɗana”.
        Da sauri Nu’aymah tace, “Ƙarya kike munafuka azzaluma. K! Ba mahaifiyarsa bace ba. Yah Yoohan wlhy ba itace mahaifiyarka ba ƙarya takeyi”. Tai maganar da fashewa da kuka tana zaro hoton nan daga envelope ta nuna masa balarabiyar nan. “Kaga mahaifiyarka nan Yah Yoohan, wlhy ba wannan shaiɗaniyar bace. Bana tantama akan har mijinta ba shine ya haifeka ba, akwai abinda suke ɓoye maka. Iyayenka na gaskiya bazasu sace maka ɗanka ba. Mahaifiya ta ƙwarai bazata so tarayya da ɗanta ba koda kuwa bata da addini, sai dai idan dabbace ita mai juyayyen tunani……….”
       “Hhhh da ƙyau tsagera”. Madam Chioma ta faɗa tana dariya har yanzu bindigarta na akan Yoohan da zantukan Nu’aymah sukema kai kawo a rai. Ta cigaba da dariya da faɗin, “Ashe tsaurin idon naki ya kai haka? Ko da yake ashefa kinsan zafin haihuwa ko? Hhhhhhh. Ashe kuwa za’a kwashi gawa da yawa a hotel ɗin nan yau”. Tai maganar da haɗe fuska ta nuno Nu’aymah da bindigar.
       Cikin kaushin murya Umar yace, “Kibar wannan haukar da kikeyi ki ajiye bindigar hannunki kawai madam”.
      Kallonta ta maida garesa. Cikin yatsina fuska tace, “Richard kake kowama? Kai kuma a suwa shiga family issue?. Maza kama kanka wannan ba shigarka baceba…..”
     Kafin ta rufe baki taji an hankaɗata, sai ga ta ita da bindigar ƙasa wanwar. Da sauri ɗaya a cikin ƴan sandamln ya ɗauke bindigar, wani kuma yazo ya danna mata ankwa ta baya. Yaran nata ma duk an kamesu. Nu’ayma kuwa da gudu ta ƙarasa jikin Yoohan dake a ɗaure ta rungumesa tana fashewa da kuka. Biyota Umar yayi ya fara warware igiyar da suka ɗaure Yoohan ɗin da ita, itama Aymah sai ta miƙe tana taimaka masa. Suna gama kwancesa ya rungume abarsa yana shafa bayanta. Sai dai bakinsa ya kasa furta komai saboda irin tafasar da zuciyarsa ke masa. Hoton hannun nata ya zare ya kafe balarabiyar jiki da kallo tare da papa dake gefenta. Jiyay wani abu na tsarga masa tun daga zuciya har zuwa tafin ƙafa. Ya kafe fuskar papa yana nazari sosai akansa batare da su Nu’aymah sun fahimci abinda yake nazartarba. A hankali ya janye Aymah a jikinsa yana miƙa mata hoton, gaban madam Chioma ya karasa. Babu wani kace nace yasa ƙafa ya taɗe ƙafafunta sai gata a ƙasa ta zube. Kasancewar hannayenta ɗaure suke ta baya da ankwa sai ta faɗi a rubda ciki. A take goshinta da hancinta da baki suka fashe, haƙoran gaba guda biyu sai gasu a ƙasa.
     Wata wahalalliyar ƙara ta saki. Yoohan yasa hannu ya birkitota ta dawo rigingine. Gaba ɗaya fuskarta ta gama damewa da jinin raunukan data samu, “Ina ɗana?”. Wannan itace kawai tambayar daya jefa mata batare da ya damu da yanda jini yayma fuskarta jage-jage ba.
       Kanta ta shiga girgiza masa, cikin rawar murya da laɓɓa tace, “Nima ban saniba John, Please ka yarda da ni”.
     Uffan Yoohan baice da itaba, sai bindigar hannun ɗan sanda ɗaya ya fisge ya ɗora mata a goshi. “Humm ke ƙaramar ƴar iskace ashe. Idan kika cigaba da min gardama ba shakka zan tarwatsa ƙaramar ƙwaƙwalwarki da harsashin cikin bindigar nan. Idan kinada taurin kai tun kan haihuwata, ni ki ɗauka bayan haihuwar tawa na damaki na shanye. Da kika ganina anan tsageran kainane nima wlhy. Faɗamin ina Yarona yake?”.
      Wutar bala’in da madam Chioma ke hangowa cikin idanun Yoohan ya sata saurin faɗin, “Zan gaya maka, amma ka taimakeni ka cikamin burina nima, kayi tarayya dani koda sau ɗaya ne naji sanyi a raina John. Ka tausayama wahalar danasha a kanka ta tsahon shekaru”.
         “Lallai k! a tumakin ma balama ce”. Yoohan ya faɗa yana cije baki da ɗana kunamar bindigar ya maida bisa tsakkiyar kanta.
      Jikinta karkarwa ya farayi, tana kuka tace, “Kayi haƙuri karka kasheni zan faɗa maka Jonh. Na rantse zan faɗa maka. Yaronka na a hannun Papanku acan wani gida dake cikin G.r.a, nima ya sakanine na kai masa kai, shine nai amfani da wannan damar domin fara cikama kaina burina a kanka na tsahon shekaru. Na biyo da kai tanan kafin na miƙaka wajensa. Miracle ita aka saka ta sace maka yaro a wajen bikin da kukeyi, dan dama muna biye da duk wani motsinku…….”
      Duka ya kai mata a fuska ɗan sanda yay saurin riƙesa. “Cool down Mr Yoohan. Karka damu dolene ta kaimu har inda suke ai. Kwantar da hankalinka kaji”.
      Huci kawai Yoohan ya keyi, tsabar zuciyar dake cinsa sai ga hawaye sharrrr suna sakkowa. Matsowa Nu’aymah tayi ta riƙe masa hannu batare da tayi magana ba. Da sauri ya jawota jikinsa ya rungume ko zaiji sassaucin zuciyarsa.

            An tattara yaran madam Chioma zuwa police station da su. Su kuma su Yoohan da sauran jami’an suka shiga motar da aka sato Yoohan tare da madam Chioma bayan an sakata kiran papa ta sanar masa cewar gata ta samo Yoohan harda Nu’aymah ma. Wani ihun gigitacciyar dariya papa ya saki har su Yoohan na jiyosa. Umar da Jami’an sun rufe fuskokinsu tamkar su ɗinne yaran madam Chioma. Itace ta dinga nuna musu hanya har suka isa anguwar. A daidai ƙofar gate ɗin gidan suka tsaya. Maigadi na leƙowa yaga motar sai ya buɗe da tunanin su madam Chioma sun ciyo nasara suma.
        Yoohan da Nu’aymah aka sakama ankwa a hannu suka fara shiga, jami’an tsaron da fuskokinsu ke a rufe na biye da su a baya. Umar ne ƙarshe da madam Chioma a gabansa. Acan waje dama tuni ƴan sanda sun gama zagaye gidan dan dama babban burinsu shine kama papa da sauran mutanensa. Abinda suka share watanni biyu suna nema ga dama ta samu a lokacin ƙanƙani.
      Da sauri Papa dake zaune cikin kujera su Joshua zagaye da shi duk suka miƙe sabida ganin Yoohan da Nu’aymah. Deen na kwance akan centre table ɗin falon cikin showal ɗinsa. Yayi kukan wahala har ya gaji yayi barci. Gefensa an ajiye sharɓeɓiyar wuƙa.
       Cike da wata irin mahaukaciyar dariya papa ya shiga tafa hannayensa yana kallon su Yoohan.
   Ya tako gabansu a hankali batare da tunaninsa ya haska masa cewar waɗanda ke bayansu ba yaransu bane ba. Da dariyarsa ya shiga faɗin, “Oh my Son & Darling daughter in-low ɗina. Welcome to my new land. Nice meeting you my guys”.
       Da ga Ayma har Yoohan dai kallonsa kawai suke. Papa ya kalli jami’an da yake tunanin yaransa ne yana fa faɗin, “Ku cire musu ankwa amfaninta ya ƙare ai. Dan game zamu buga da su mai zafi”.
     Babu musu ƴan sandan nan suka cirema su Yoohan ankwa. Komawa papa yay ya zauna a kujerar daya taso. Ya ɗan taɓe bakinsa da dora ƙafa ɗaya kan ɗaya ya ɗauki kofin giyarsa ya kurɓa yana kallon su Yoohan. “John badan inada ƙarancin lokaci ba dana baka wani labari mai ban mamaki da al’ajabi. Amma share kawai muje ga game ɗinmu. Idan lokaci ya rage mana a cikinsa sai na baka labarin. Daughter in-low karki tada hankalinki kinji, ɗanki yana lafiya, kingama barci yake abinsa”. Yay maganar da tasowa daga kwanciyar da yayi jikin kujera ya yaye showal ɗin da deen yake ciki yana lakatar hancin yaron da ɗan yatsa. “Daughter kin iya haihuwar ɗa fa”. Ya faɗa yana kecewa da dariya su Mike na tayasa. Giyarsa ya kwankwaɗa ya ajiye kofin yana haɗe hannayensa waje guda. “Oh Sorry my son karka fusata na sanka da zuciya”. Takardun dake a gefen Deen ya jawo ya tura ƙarshen tebirin ta sashen da su Yoohan suke. “Wannan takardun sune game ɗinmu tare da ɗan jinjirinku ƙyaƙyƙyawa. John kanada zaɓi biyu. Kuɓutar da yaronka ta hanyar yimin signing a duk takar dunnan, ko kummaaaaa nai masa yannnnnkan rago da wannan wuƙar tawa a wannan lallausar fatar tashi”. Ya ƙyalƙyale da dariya yana ɗora wuƙar bisa cikin Deen dake barci a binsa yanata sakin ajiyar zuciyar kukan da yasha.
       Ko motsi Yoohan baiyiba, haka ma Nu’aymah duk da hankalinta a tashe yake kallon papa kawai take zuciyarta na tunanin anya kuwa wannan mutumin ma mahaifin Yoohan ne?
        Hannunta taga Yoohan ya saki tare da takawa a hankali zuwa gaban papa yana wani ƙyaƙyƙyawan murmushi, dan cikin ƴan sandan nan ɗaya yay masa alamar yaje. Zuwa yanzu sunsan sauran ƴan uwansu sun gama tattare yaran papa gaba ɗaya dake cikin gidan. Sannan sun gama nazarin su papa kaf babu wani makami tare da su anan sai wuƙar dake akan Deen. Babu wani alamar damuwa a fuskar Yoohan balle tambayar papa ba’asin yin hakan. Yazo gaban tebirin ya zauna akan ƙaton tum-tum dake kusa da shi yana murmushi. Cikin kwanciyar hankali ya ɗauki pen ɗin dake saman takardun ya rike a hannu. Shafin farko na takardun ya karanta cike da nazari. Yaɗan ɗago ido ya kalli papa da shima ke kallonsa. Murmushi Yoohan ya sakar masa da taune lip ɗinsa na ƙasa ya ɗage gira ɗaya da lumshe idanunsa ya sake buɗewa akan takardun. Har cikin jini Murmushin Yoohan ya daki zuciyar papa da su Mike. Amma sai basuyi magana ba. Ɗaya bayan ɗaya Yoohan ya fara signing takardun. Yana gab da gamawa Mike da ya farga babu Madam Chioma. yace, “Brother wai nikam ina madam ma ne? Ta kawo mana su amma banga ta shigoba ita”.
     Da sauri Papa ya kalli Mike, sai kuma ya kalli Yoohan dake signing yana murmushi da taunar lip dinsa na ƙasa. “John mikake kullawa? Ina matata?”.
    Ko motsi Yoohan baiyiba balle ya kalli papa. Sai da ya gama signing ɗin duk takardun sannan ya kalli papa da tsoro ya fara bayyana masa a fuska. Wuƙar kan Deen ya dauka yana faɗin, “Ashe kuwa inhar wani abu ya samu matata saina halaka wannan yaron”.
      Murmushi Yoohan ya sakeyi har haƙoransa na bayyana. Ya miƙe tsaye hannunsa ɗauke da takardun da yay Signing. Yaɗan sosa pen din a gefen wuyansa yana duban papan. “Oh my sweet papa ya da karaya haka da wuri?”. Yay maganar da wani shegen murmushin yaƙe. Sai sukaga ya girgiza kansa yana ɗan buɗa hannayensa. “Karfa ka damu papa. taya zan cutar da mahaifiyata. Guys Please ku kawo masa matarsa”. Ya juya yana kallon ƴan sandan nan. Umar dake can ƙofar falon bai shigoba ya turo madam Chioma ta fara shigowa bakinta a ɗaure. Bindiga a bisa kanta.
    Wani irin zabura papa yayi jikinsa na rawa. Kafin yay magana Yoohan yay ƴar dariya yana faɗin, “Oh my sweet papa relaxxxxx!!. Idan ban mantaba kace zamuyi game ko? So karka damu bazan canja ba zamu buga ai. Nasan kana son matarka, ba kuma zakaso rasata ba, gata ƴar ƙyaƙyƙyawa kuwa”. Yay maganar da wata shegiyar dariya. Sai kuma ya gimtse fuska da haɗe hannayensa waje guda yace, “Oh sorry papa bazan sakeba. Ga takardu na maka signing kamar yanda ka buƙata. Sai dai kana da zaɓi. Matarka ko waɗanan takardun. Idan su kafi buƙata, zan baka, amma zan tarwatsa kwanyar matarka a gabanka. Idan kuma matarka kafi bukata, zaka bani ɗana, na kuma wuce da takardun nan a gabanka. Wannan shine game ɗin Yahyaaaaaa! Much????! much????!!, I love you my papa!!”. Suka kwashe da dariya a ƙarshen maganar shi da Nu’aymah tare da tafawa.
       Wani irin huci papa ya fara fitarwa kamar zai shiɗe. Ya kai hannu zai fisgi wuƙar nan Yoohan yay saurin faɗin, “No! no! no no no no!!!! Pastor goshpower. Karka fusata da yawa fa, kasan ɗan naka mai faɗa da cikawa ne. Ai yanzun game ya tashi daga tsakanin takardu da yarona, ya koma tsakanin takardu da matarka ok?”.
     Kafin papa yace wani abu Yoohan ya  fisge handkerchief ɗin da suka ɗaure bakin Chioma da shi. Wani wahallalen ƙara ta saki da fashewa da kuka. Cikin roƙo tace, “Please Darling ka basu yaronsu, ka taimakeni, na rantse john zai iya kasheni, kagafa yanda ya ciremin haƙwara, karkai jayayya dasu nan duk jami’an tsarone ba yaranmu ba”.
     “What!!!”.
  Papa da su Mike suka ambata a firgice. A take duk jami’an tsaron da Omar suka janye abinda suka rufe fuska. Sai ga wasu na shigowa suma akai ma su papa zobe. takawa Yoohan yayi gaban papa yana dariya ya ɗauki Deen ya rungume a jikinsa tare da sumbatar goshin yaron. Da sauri Nu’aymah ma ta matso garesa ta haɗashi shi da yaron ta rungume. Umar kuwa ya damkama ƴan sanda Madam Chioma ya matso ya ɗauki takardun da Yoohan yayma Signing yana dubawa.
      “Kai!! Dude!, anya kuwa mutumin nan ma shine mahaifinka kuwa?”.. 
     Ɗagowa Yoohan yayi daga sumbatar kumatun Deeen, yasa hannu ya share hawayen da suka cika masa ido yana miƙama Nu’aymah yaron. Yace, “Goyashi akwai sanyi”. Babu musu Aymah ta juya ya ɗora mata Deen a baya ta goyashi, ya gyara mata hijjab ɗin jikinta sannan ya dubi Umar da yay tambayar da furzar da zazzafan huci.
       “Bana zaton haka Umar, dan abubuwa da yawa sun banbanta tsakaninsa da wanda ke a hoton nan. Sannan waɗanan takardun mallakin kaddarorine a cikinsu wanda alamu suke nuna ba nasa bane sam. Dan signing ɗin cikinsu ba irin nashi baneba. Akwai sirrin da yake ɓoyema duniya a kaina……..”
         “Sirri mai girma kuwa”.
Muryar da basuyi zato ba ta karaɗe kunnuwansu a bazata. kusan gaba ɗayansu suka dubi bakin ƙofar inda maganar ta fito. Jawaad Abdul-aziz Yusuf ne tsaye cikin ƙananun kayan da suka rage masa shekaru, sai dai duk wanda yasan shekarun girma ya kallesa yasan shiɗin bana wasan yara bane, (Duk ya girmi masu karatu yanzu, duk da a gabansu aka haihesa????????????????).
         Bayansa jami’ai ne biye da shi. Cikin falon ya karasa shigowa ya zauna a kujerar da ke kallon papa dake a durƙushe bisa gwiwoyinsa yanzu shi da su Anthony saboda zagayesu da akai da bindugu.
       Ƙafa ya ɗora ɗaya kan ɗaya yana wani shegen murmushi, yace, “Hii Goshpower, sai kuma gaka. Hhhh ALLAH sarki. Haka rayuwa take ai, duk iya gudun mai tsere bai isa zarta ƙaddararsa ba. Dama naji a jikina dole ka dawo, dan yanzu da dukiyar da wannan takardun kawai kake tunanin ka tsira. Kafa birgeni, dan da gaske ka iya wasa. Kana da basira ƙwarai da gaske. Sai dai kuma kanada daƙiƙanci a wajen kuskuren lissafi. Da ace bakabar Yoohan a raye ba da lissafinka bazai taɓa ɓata ba. Sai dai kash a dalilin ƙwaɗayin abinda baka taraba ka saka kanka a tarko tsahon shekara talatin da biyu. Tsem! Tsemm tsemmm!!! Gaskiya ka bani tausayi. A farkon labarin dai cike yake da birgewa da ƙayatarwa ga marubucinsa. Sai dai a ƙarshe an samu dagulewar ƙwaƙwalwa ga marubucin. Mai makon yanda aka fara da nasara a ƙare da nasarori sai aka ɓige da faɗuwa ƙasa wanwar. Kash matsalar tunani ko Mr goshpower”.
     Jay yay maganar ƙarshe yana ɗage gira da sakin dariya. Ya cigaba da faɗin, “Oh sorry bara na taƙaita, dan ka sani tafiyar da ban shiryaba a daren nan daga Abuja zuwa kano ga uban sanyi. Maganar gaskiya ma ban yafe ba. Ƴan jarida ku shirya kayan aiki”. Ya faɗa yana shafar girarsa da nuna hanyar ƙofa.
       A take kuwa suka shigo kusan su shida. Duban Yoohan da Nu’aymah da Umar yay ya nuna musu kujerun alamar su zauna suma.
      Zama sukai a sanyaye kamar an doke gwiyawunsu da ƙarfuna.
     Jay ya kalli agogon hannunsa sannan ya dubi papa. “Mr Goshpower bamu da isashen lokaci, dan awoyi uku da mintuna ashirin da ɗaya suka rage alfijir ya keto. Bana son wasana da kai yay tsamari a wannan gaɓar dan daga ni har kai mun jigatu, inason sanin wanene Yahya? Su wanene kuma waɗanan na jikin hoton?”.
     Shiru papa yayi ya ƙi magana, hakan yasa Jay ɗinma bai sake magana ba, sai kawai ƙarar bibdiga su Aymah sukaji da ƙarar papa. Ruɗewa Aymah tayi ta ƙwaƙume Yoohan jikinta na rawa. Ga Deen dake bayanta ma ya farka da wani irin firgitaccen kuka. Taimaka mata Yoohan yayi ta sakko da shi, ya rungumesa a jikinsa yana jijjiga shi. Da kallon papa da Jay yayma harbi biyu a duka ƙafafunsa saboda tsabar ƙwarewa a iya harbi.
      Jay ya girgiza kansa da dafesa. Yace, “Oh kana neman fusatanine Mr Goshpower. Gashi ni kuma hannayena ƙaiƙayi sukeyi. Na faɗa maka a jigace nake matuƙa, karka jani da nisa ana idar da sallar asuba nake son komawa Abuja”.
       Cikin magautar raɗaɗi papa ya fara magana. Ga wata irin zufa ta jiƙesa a take duk da uban sanyin da ake zubawa a garin. Yace, “Shima sunansa Goshpower, shi ɗin twin brother ɗinane. Wannan kuma matarsa ce”.
       “Yayi ɗan gari, haka nake buƙatar jinka. Omar a cire masa bullets ɗin nan”.
       Da sauri Omar yace, “Okay Uncle ”.
       Tsabar son azabartarwa Umar sai ya ɗauki giyar da papa yasha ya rage ya zuba masa akan harbin. A take kuwa ya saki wata wahalliyar ƙara ya suma. Ko a jikin Omar. Ya amshi First aid box a hannun wani jami’i da sukazo da shi ya cire bullets ɗin cike da rashin tausayi. Sai da ya kammala komai sannan aka zubama papa ruwa ya farfaɗo.
       Sai da suka bashi damar hutun kusan mintuna biyar ya daidaita sannan ya fara bada labari.

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button