SULTAN 11-12

Jiki babu ƙwari na goge hawayen idona na bi bayanta, ko da muka shiga ɗakin sauran maids ɗin ma cire kayansu suka yi sannan suka faɗa kwamin wankan tare, wasa suke sosai wanda duk na banza ne kafin ta juyo ta kalleni tare da miƙo min hannunta alamun na je, babu yanda na iya haka na je ɗin, wanka aka yi mana sannan muka fito. Bayan na shirya na dubeta na ce “zan tafi”
Drawer ta buɗe ta ɗauko wani zobe mai masifar kyau ta kama hannuna ta saka min sannan ta kalli ƙwayar idona ta ce “gobe zan aiko a kira ki snow white” ta yi pecking goshina sannan na fita.
Ko da na fita gari ya soma duhu alamun na yi mugun dare a wajenta, da hanzari na nufi ɓangarenmu ina jin yanda cikina ke kukan yunwa, ina tura ƙofar sashen na gansa zaune kan wani ɗan dakali ya rafka tagumi yana kallon ƙofar, wani tausayinsa ya dirar min tunawa da na yi bai ci komai ba tun sanyin safiya, yana ganina ya miƙe yana kallona, na ɗan ƙaƙalo murmushi na ce “na bar ka da yunwa, yi haƙuri”
Bai tanka ba don na san ba zai tanka ɗin ba na ja hannunsa zuwa ciki, kan kujera na zaunar da shi na ɗebo madara na ba shi, ya sha sosai sannan na sha ni ma na fito waje, yana biye da ni, wuta na shiga hurawa, idona sun yi jajur sai fitar hawaye suke saboda hayaƙi kafin na samu su kama na ɗora tukunyar faten wake da karas ɗin da zan yi, ina ɗagowa ya ƙura ma fuskata ido sai ya kai hannunsa ya shiga share min hawayen da ke gudana na hayaƙi, ɗan murmushi na yi masa na ce “mu je” na ja hannunsa zuwa dakalin na shiga gyaran wake, an ɗau lokaci sannan na kammala abincin muka zauna cikin farin wata ina ba shi yana ci, sai da ya ƙoshi Ni ma na ci, bayan nan na shiga ba sa labari, ƙurrr yake kallona alamun yana saurara duk da kuwa ba ya cewa komai, wajen tara na dubesa na ce “mu je ciki ka kwanta dare ya yi” ya rufa min baya bayan na tashi. Direct ɗakinsa muka wuce na kwantar da shi tare da rufa masa bargo sannan Ni ma na jingina da gadon ina buga bayansa a hankali, saukar ɗumin numfashinsa da na fara ji a hannuna ya sanya na gane ya yi bacci, leƙa fuskarsa na yi, na ga sai baccinsa yake cikin kwanciyar hankali, he looks so innocent and cute, hannuna na ɗora kan dimples ɗinsa da suka lotsa na danna na ce “mai kyau ina fatan ka warke nan kusa”, na jima ina kallonsa kafin na rufa masa bargon da kyau na kashe fitila sannan na fice daga ɗakin, sanin ba zan iya bacci ba ya sanya na koma ɗaki na ɗauko bargon da Prince Wahid ya rufa min jiya na fita, da mamakin nake kallon…
*????SULTAAN* # Nml grp ~N~ 300 vip ~N~ 500 via 1401611541 Access bank, shaidar biyanki ta wannan numbern 08167888934
*Mss Flower????*
TSINTACCIYA
Nimcyluv
Baƙar fata
Autar manya
DATTIJON ARZIƘI
Real ladingo
Gaba ɗaya 800
Via 6850917335 Na’ima Shu’aibu Sulaiman Fidelity Bank, ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218
*Mss Flower???? 08167888934* For more information????
[ad_2]