Uncategorized

TAKUN SAAKA 15

 *_Typing????_*

*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK????????_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK????????_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK????????_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK????????_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

_________________________

*_MACE SAI DA GYARA_*????????????????

_GYARAN MA NA KAMFANIN TURAREN:_

    *YERWA INCENSE AND MORE*

 *Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.*

_Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawatattu kuma nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki. hadin bornu/chadian na kamfanin turaren YERWA INCENSE AND MORE_

*_Muna da haɗin_*

_Turaren wuta kala kala na gidah_

_khumrahs_

_Kullaccham_

_Turaren wanka_

_Turaren Kaya_

_Turaren wanki_

_turaren mopping_

_Dukkanil al’ajab (Turaren tsugunno na Matan aure kad’ai)_

_khumratul al’ajab (khumrah ta jiki ta matan aure_

_Muna Gyaran jiki_ 

_Na amare_ 

_Da masu jego_

_Da sabulai masu gyara fata_

_Turaren tsugunno_

_zumar goran tula_

_Scented hair cream and spray (man kamshin gashi da gyara gashi_

_Akwaisu kujeran tsugunno

_Dilke and halwa set_

_Burners da igniters da tong_

_turaren fesawa dana ruwa._

_wardrobe balls_

_scented pebbles_

_cotton wooly oudi incense_

_kabbasas_

_Da sauran kayayyaki da yawa da bamu ambata ba_

_Akwai ragi na musanman ga yan zafafa fans❤️_

_Muna bada sari, Ko sayi ‘dai ‘dai akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan ????????_*

 _EMAIL:yerwaincenseandmore@gmail.com ko INSTAGRAM PAGE d’inmu:yerwaincense_and_more dama nambR mu:08095215215_

_MUNA TURAWA KAYAN MU KO’INA A FADIN NIJERIYA DAMA KASASHEN KETARE.

100% TESTED AND TRUSTED_

••••••••••••••••••••••••••••••••

*_Chapter Fifteen_*

………Kamar yanda doctor Bilal ya faɗa a ranar suka sallami Ummi tare da sharuɗan da za’a kiyaye game da lafiyarta. Su Yaya Abubakar sun amsa masa tare da tabbatarwa. Wannan ɗin ma akasi aka samu kawai. Da ga haka sukai masa godiya suka tafi da sanyin idaniyarsu gida.

        Koda suka isa gidan babu wanda yayma Ummi zancen Abbah, hasalima su sun manta ma. Hidimarsu suka cigaba da yi hankali kwance har dare. Sai da zasu kwanta ne Ummi taji shirun gidan yayi yawa take tambayar Hibbah data maƙale a ɗakinta zata kwana. Bargo Hibbah taja har saman kanta tana sake bajewa a gadon na Ummi. “Ummi nima ban saniba. Ƙila sunje ƙauye ne”.

     Shiru Ummi tai tana nazari, tasan Momy ko kowa zaije ƙauye ita dai bazataje ba. Hakama ƴammatan ƴaƴanta. Hajiya Mama da Abban ne kawai suke zuwa, suma idan aikin sharrinsu ya tsikaresu, kuma Abba ma ai bai jima da dawowa ba. Ajiyar zuciya ta sauke da kauda zancen a ranta itama ta kwanta tare da kai hannu ta janye bargon da Hibbah tasa har saman kai. 

      Duk yanda Ummi taso yin barci gagararta yayi, sai ma dulmiyawa da tai a ƙololuwar duniyar tunani da neman mafita. Taja tsahon lokaci tana ƙullawa da kwancewa kafin ta sami mafitar da take addu’a da fatan ta zame musu alkairi ita da zuri’arta.

          Da asuba bayan sun idar da salla Ummi ta dakatar da Hibbah da ga barcin da take ƙoƙarin komawa gado tayi. Cike da shagwaɓa ta lafe a jikin Ummin tana faɗin, “Wayyo Ummi ALLAH barci nakeji, kinga yau weekend ne babu makaranta sai islamiyya, su Yaya bazasuje aiki ba na san suma barcin zasuyi”.

           Murmushi kawai Ummin tayi, zuciyarta najin tausayin autar ta bisa hukuncin data yanke akan lamarin duk ƴaƴanta a daren jiya. “Muhibbat!”.

    Ta kirayi sunan Hibbah dake lumshe idanu babu wasa. Idanu Hibbah ta buɗe tana kallon Ummin, dan yanda ta kirata da cikakken sunanta babu wasa tasan ƙwarai magana ce mai muhimmanci.

     “Na’am Ummi”.

“Tambayarki zanyi?”.

“To Ummi, ALLAH yasa na sani”.

     Numfashi Ummi taja da kafe Hibbah da ido. “Duka yayunki babu mai neman aure ne dama?”.

    Ɗan jimm Hibbah tai alamar nazari. Kafin tace, “Ummi wai kina nufin sunada ƴammata?”.

      Kai Ummi ta jinjina mata kawai.

Hibbah ta ƙyalƙyale da dariya tana kwantawa ta ɗaura kanta a cinyar Ummi. “Uhm ai Ummi fa dama tun kwanaki nakeson na baki labari Yaya Umar ya gargaɗeni. Wai so suke suyi miki surprise ne. Kinga Yaya Muhammad yana da budurwa, Maimunatu (Kausar) ɗin gidan Sheikh Aliyu Abdul-Ra’uff Maina abokin Daddyn mu, mai islamiyyarmu kuma ɗiyar kawarki…….”

      Wani irin farin ciki da sanyi ne ya lulluɓe zuciyar Ummi lokaci guda. Ta katse Hibba cike da zumuɗi. “Da gaske Tanee?”.

       “Wlhy kuwa Ummi. Kin dai santa babu ruwanta ga hankali, kina zuwa gidansu, suna zuwa nan gidan kinsan tarbiyyarsu. Gata malama a Islamiyyar tamu. Akwai wani dabino da zam-zam da zuma da Yaya Muhammad ya kawo miki kwanaki na rantse itace ta bada a baki. Amma yace idan na faɗa sai ya fasan baki.”

      Yanda Hibbah ta ƙare maganarne ya saka Ummi ƙyalƙyalewa da dariya. “Kai Mamana har yanzu dai ke sakara ce ALLAH, basai ki gayamin a sirri ba. Sam baki biyo mai sunanki ba. To Abubakar fa?”.

          Cikin dariyar zancen Ummi Hibbah tace, “Tab na Zahidah kenan.”

     “Wannan Zahidah ta gidan Auntyn ku Kulu dai dana sani?”.

     “Eh wlhy Ummi. Amma yace karsu faɗama kowa sai ta gama makaranta. Nima basusan na ganeba a ɓoye sukeyi”.

     Nanma dariyar farin ciki ce ta bayyana akan fuskar Ummi. Har ranta zaɓin Yaya Abubakar da na Yaya Muhammad sun mata hundred percent. Hibbah ta cigaba da faɗin, “Shi kuma Yaya Umar Nafisa ce nasan kin sani dama. Yaya Usman kuma Hafsat itama kin sani. Zakin ki kuma babu kasuwa har yanzun”.

     Sosai Ummi taji matuƙar daɗi, dukkan damuwarta sai ta gushe a lokaci guda. Taji ƙwarin gwiwa bisa ga abinda take shiryawa. Dukkan fargabarta ta gushe. A ɓangaren muhalli bata da matsala da yaranta, duk gine-ginensu sai dai ƙarashe. Dan suna fara aiki suka haɗa hannu wajen fara ginin filin da taketa tattali da kaffa-kaffa domin su. Burinta ita da mahaifinsu yanda suka tashi kansu a haɗe su cigaba da rayuwa a waje guda. Shiyyasa koda ya sai filin sai ya damƙashi hannun amininsa kuma malaminsa har sai da suka fara aiki ya basu. Shiyyasa har yanzu Abba da Hajiya Mama basusan da zancen ginin ba……..

1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button