Uncategorized

TAKUN SAAKA 16

       Har ga ALLAH kalamansa sun sanyaya ranta. Taji matuƙar kinarsa da girmansa. Sai dai maganarsa ta kusan ƙarshe-ƙarshe akan ba’a barinsu zance ta tsaya mata arai. ta kuma sake tabbatar mata akwai abinda Abba ke ƙullawa game da auren nata da Shuraim, wanda shima da alama baida masaniya akai. 

         Numfashi taja tare da duƙar da kanta ƙasa, dan a karon farko taji kunyarsa da nauyinsa ta lulluɓe ta. Cikin sanyin muryar da batasan tana da ita ba tace, “ALLAH ya tabbatar mana da alkairi”.

      “Amin ya ALLAH”  ya faɗa yana murmushi dan ya fahimci dukkan abin cewar data shigo da shi falon ya gudu.

    Ba wata hira mai tsayi sukai ba, sai ɗan guntun tarihinta itama data bashi sukai sallama ya tafi itama ta shige ciki. Dama ALLAH-ALLAH take ya wuce ta tafi ga aikin da ke gabanta akan files ɗin da dattijon jami’i ya bata (kamar yanda ta raɗa masa suna????). Dan tun randa ya bata washe gari ta kwashe Computer ɗinta da ga falo ta maida cikin bedroom. Koda Ummi ta tambayeta dalili sai tace babu komai zata ajiyesu ne dan ta daina amfani da su sai nan gaba.

     Ummi ta gamsu da bayaninta ɗari bisa ɗari. Sai dai abinda bata sani ba tuni Hibbah ta haɗa kayan a ɗakinta harma ta fara aiki akan abinda aka sakata. Ta samu bayanai na laifukan da Master ya aikata kashi-kashi, sai flash drive guda uku dake ɗauke da wasu rubuce-rubucensa na yanar gozo, da fuskokin da yake amfani da su. Abinda ta yanke na farko shine zaman yin nazari da kutse na musamman akan facemasks da yake amfani da su. Haka kawai taji a ranta tana son samo ainahin fuskarsa ta ainahi da take kallo a matakin farko na aikinta. Zatayi hakanne ta wasu hanyoyi da take ganin zasu taimaketa duk da ko farcensa baya bari a gani rufesa yake. Sai duka handles ɗinsa na yanar gizo da ya taɓa amfani da su ta hanyar tura saƙo. Da nambobin waya da yay kira dasu masu tsananin tsaro.

     Yanzu gaba ɗaya lokacinta da hankalinta duk sun koma akan binciken Master da ayyukansa. Ta matuƙar maida kanta busy batare da kowa ya sani ba. Sai da safe ne idan Yayunta suka ga idanunta duk a kumbure suyita tambayarta miya hanata barci?. Takance karatune na exam da zasu fara. Tanason ta dage ne saboda shirye-shiryen exam ɗin zai haɗe mata da hidimar biki.

      Duk sun gamsu da bayanin nata, dan haka sukai mata nasiha kawai akan ta ringa sassautawa tana barci dan karta saka kanta a matsala. Insha ALLAH zataci.

★★★★★

          A lokacin da Hibbah keta kaikawo akan ƙoƙarin yin kutse cikin lamarin Master a gidansu shirye-shiryen biki ake tuƙuru ta fanin su Hajiya Mama da Abba da ke faman jiyyar ƙafarsa da hannu. Shiri suke na bikin ƴaƴan gata ta kowanne fanni. Dan hatta da gidajen da su Yaya Muhammad zasu zauna da amare Abba duk ya saka abokinsa ya nema musu haya, ya kuma biya kuɗin hayar da kudinsa acewarsa zai biya na farko daga haka su cigaba da biya.

       Komai dake faruwa Ummi na kallo. Sai dai ta maida kanta makauniyar ƙarfi da yaji bata taɓa nuna alamar tana fahimta ba. Sai ma faman nata shirye-shiryen da takeyi ita da Sheikh Aliyu Maina da iyalansa itama. Dan a yanzu haka ma anata shirin miƙa akwatunan lefen auren su Yaya Muhammad da suka haɗama kansu da kansu zuwa gidan amarensu. Gidansu kuma na gab da kammaluwa sai sam barka da fatan alkairi.  

       *______________________________*

     

          Kwanakin biki sun cigaba da turawa, shirye-shiye na ƙara faɗaɗa a kowanne ɓangare. Sai dai kuma a ɓangaren Hibbah ita hankalinta a tashe yake matuƙa bisa dalilai biyu. Na farko shine har yanzu bata sake ji da ga jami’an tsaro ba, musamman akan binciken da sukace zasu mata game da Muhammad Shuraim da zuwa yanzu shaƙuwa mai ƙarfi ta ƙara shiga tsakaninsu. Dan tun daga waccan ranar duk bayan kwana biyu sai yazo gidansu. Bawata hira sukeba mai yawa, mafi yawanci ma akan karatu ne dan tafi sakin jiki da shi. 

        Na biyu ganin yanda su Abba ke shirye-shiryen auren duk da yana kwance har yanzu yana fama da ƙafa sai yake ɗaga mata hankali take ganin tamkar tarkon data ɗana musu domin kuɓutar da yayunta bamai yuwuwa bane a garesu. Cikin ɓacin rai yau ta tattara dukanin kayan da A.G ya bata ta maida a bag ɗin. Dama addu’a taketa faman yi ALLAH yasa Ummi ta fita zuwa gidan malam da taji tana faɗa zata.

      Tana samu yayunta suka fita, Ummi ma ta fita gidan malam ɗin tare da su sai itama ta samu ta siɗaɗa ta fice da addu’ar ALLAH yasa har taje ta dawo Ummi bata dawo gidan ba.

         Tana shirin shiga napep aka dakatar da ita. Tai saurin juyowa a rikice jin an ambaci sunanta. Kallon sama zuwa ƙasa taima matashin saurayin da batasan daga ina ya fito ba. Shima batare da wani damuwar kallon da take masanba ya miƙa mata ƙaramar jakkar hannunsa.

      “Babu buƙatar ki sake komawa can. Zaki sami dukkan bayanan da kike buƙata anan. Akwai waya yace zai kiraki tanan zakuyi magana. Kiyi komai da kula”.

      Batare da ya jira cewarta ba ya juya ya barta tsaye galala da jikka a hannu tana binsa da kallo. Takaici da haushi yasa mai napep jan napep ɗinsa yabar wajen yana masifar an bata masa lokaci.

       Itama Hibbah juyawa tai ta koma gida jiki da sauri…………..✍

TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????

#team ZAFAFA BIYAR????????????????????

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button