TAKUN SAAKA 38

*_Chapter Thirty Eight_*
……….Tsabar firgita batasan ta wantsalo da ga jikinsa zuwa ƙasan carpet ba. Ta kalla mask ɗin hannunta ta dubesa har kusan sau uku tamkar wadda kwalwar kanta ke neman juyewa. Kanta ta shiga ɗan girgizawa zuciyarta na sake tabbatar mata ba abinda take tunanin bane ba. Tabbas da wani salon yaudarar ya sake shirya zo mata kuma. Yayi amfanine da face ɗin Yaya Isma’il tamkar yanda yakeyi da wasu a baya.
Cikin rawar murya da hawayen da ke sakko mata ta fara magana tana dubansa, duk da ya tsume fuska tamkar bai damu da a yanda ta gansan ba. Kamar zatai magana sai kuma ta miƙe tana jefar da mask ɗin da ja baya. “Amfani da fuskar Yaya Isma’il domin badda kama bashike nufin zaka samu daraja irin tasa da ga gareni ba ko ga iyayena. Kabar yaudarar kanka Muhibbat Aliyu Gwarzo bazata taɓa amincewa rayuwar aure da kai ba koda mazan duniya sun ƙare. Idan kuma kai amfani da fuskarsa ka aikata wani laifin na rantse da ALLAH bazan yafe maka ba, koda zan rasa raina a wannan gaɓar bazan barkaba, bazan barkaba…….”
Kuka ya sarƙeta ta kasa cigaba da maganar, da gudu tabar wajen dan ji take tamkar falon na juya mata ma. Master da gaba ɗaya bama ya fahimtar zancen nata saboda wani ruɗaɗɗen al’amari dake ratsa jinin jikinsa zuwa kwanya ya cije lip ɗinsa na sama da ƙarfi, dan wani irin mahaukacin murɗa masa mararsa tayi a yanayin da bai taɓa fuskanta ba a rayuwarsa. Tabbas yanajin sha’awa da buƙatar mace batun yanzu ba, amma na yau ko yace yanzun nan dabanne dana ko yaushe. Dan tunda ya kammala shan tea ɗin nan dama yakejin jikinsa tamkar yana canjawa. Bai kawo komai a ransa ba da farko sai tunanin murar dake nuƙurkusarsa ce kawai. Sake ƙullewa cikin yay har yana jan numfashi a fisge zuciyarsa na wani bugu da sauri-sauri. Duk yanda yaso nuna jarumta da juriya ko tunanin daga ina matsalar take hakan ya gagara. Babu shiri ya rarumi waya ya fara neman number Abdull kuma amininsa ɗaya tal a duniya….
Hibbah kam koda ta afka bedroom saman gado ta faɗa tana fashewa da sabon kuka mai tsuma rai.
“Nashiga uku ni Muhhibat wace irin *MAKAUNIYAR ƘADDARA* ce haka ta kutso rayuwata?. Wane irin mutumne wannan da sam baka gane gabansa balle baya. Ya ALLAH ka kubutar da ni daga mutumin nan kozan samu ƴancin rayuwa daga shu’umcinsa. Kai yau duk ma yanda za’ai dolene na bar gidan nan”.
Ta faɗa tana mikewa zumbur tamkar wadda aka tsikara. Ɗankwalin jallabiyarta da yay gefe ta ɗauka ta naɗa a kanta tana share hawayen da suke ziraro mata. Yau fa koma minene zai faru sai dai ya faru saita rabu da mutanen nan kafin su salwantar mata da rayuwar ahalinta da ita kanta. Wadrobe ta buɗe ta ɗaukko hijjab ɗin da ita kanta batasan ina ya samosa ba tana cije baki saboda wani irin kartawa da mararta tai mata a karon farko. A dai-dai nan ya shigo bedroom ɗin waya a kunnensa alamar magana yake da Abdull haryanzun cikin kamar fitar hayyaci, a kuma real Isma’il ɗin sa. Kasancewar yana gab da isowa gareta ita kuma ta juyo sukaci karo. Baya tai ƙoƙarin ja ya riƙo hijjabin hannunta. Koda taja taji bazata iya ba sai ta sakar masa kawai. Shima hijjab ɗin ya saki ya riƙota, nan ma turesa ta shigayi da iya ƙarfinta tana kuka, sai dai ko gezau baiyiba duk da tsuma da jikinsa keyi, sai ma mannata da yay da jikin nasa sosai yana cigaba da amsa wayarsa tamkar zai karya mata ƙasusuwa. Kuka mai cin rai ta sake sakar masa da kaima hannunsa cizo saboda jin azabar riƙon da yay mata.
Duk da yaga abinda take da niyyar yi bai saketa ba, saukar hakwaranta kan fatar hannunsa ta sakashi rumtse idanun da ƙarfi har yana janye wayar da ga kunnensa ya katse kiran…..
“Ouch!”. Ya faɗa da janye hannunsa a ɗan zafafe saboda yanda cizon yay masifar ratsa masa jiki ga azabar da ke neman kiɗima rayuwarsa. Sam baiyi tunanin zatai cizon da bakar mugunta bane irin haka shiyyasa ya barta. Barin jikin nasa tai da sauri ya sake fisgota cikin fara ficewar hayyaci. Shi kansa zuwa yanzu ya tabbatar akwai matsala, dan ji yake inhar bai kasance da mace ba zai iya rasa ransa ma.
Ita kanta Hibbah baƙon al’amarin dake ratsa magudanar jininta ne ke neman saka hankalinta gushewa gaba ɗaya, tama rasa ina zata tsoma ranta taji sanyi da wannan yanayi mai rikita tunani. Wani irin mahaukacin cikuykuyesa tai tana fashewa da kuka, taringa jujjuya kanta bisa ƙirjinsa jikinta na wani irin kakkarwa sai cije baki take. Cikin sake ficewa da ga hayyacinsa saboda rungumar da tai masa, ga yanda take juya kanta a ƙirjinsa ya sashi faɗawa da ita saman gadon yana rufe mata bakin ruf da nasa, dan kukan nata wani irin tunzura fitinarsa take zuwa gareta..
Da zafi-zafi yake cuɗata tako ina har shi kansa baisan mima yake ba. Dan ɗan haɗin kan da take bashi cikin gushewar nata hankalinne ke sake harmutsa tunaninsa da gigita dukkan jarumtarsa. Canjawar salon wasan ne ya saka Hibbah fara turesa ta fisge bakinta, tanada ilimin addini tasan minene ma’anar addu’ar da yake karantowa, cikin karkarwar jiki da jujjuya masa kanta tana sake sakin wahalallen kuka ta hau roƙonsa da magiya.
“Dan ALLAH kar kayi bana so. Na tuba Yayana, wlhy na haƙura bazan sake cewa zan tafi ba har sai ka yarda. kaimin rai, ka dubi maraicina karka ruguzamin rayuwa”.
Kansa ya shiga juya mata shima yana sake riƙota. Yanda idanunsa ke sake canja kala sak na bahagon zaki ya sake sakata fashe masa da kuka, gashi ita tunaninta facemask yasa dan ya yaudareta da fuskar Isma’il. Sake turata yay cikin jikinsa, da wata irin muryar da batasan a wanne fanni ko rukini zata sakata ba ya fara mata magana cikin kunne. “Uhm-uhm Hibbaty, kiji tausayin Yaya Isma’il ɗinki karya m…u…tu”.
Ya kai karshen maganar da ƙyar yana kamo hannunta ya ɗaura a jikinsa da yakejin tamkar an ɗaura dutsi mai zafi dan azaba. Gaba ɗaya sai ta sake ruɗewa. Tai azamar jan hannunta baya ya sake damƙewa. Duk yanda yaso magana bakinsa ta cigaba da fita hakan ya gagara. Itama ya hanata cigaba da roƙonsa dan yasan bazai iya mata alfarmar da take buƙatar ba a wannan halin.
Tun Hibbah na tunanin samun alfarma da ga garesa harta fidda rai, ta fara kwala kiran sunan Ummi da su Yaya Muhammad suzo su taimaketa, daga ƙarshe ma sai kukan ya gagareta balle neman samun ceto, tun tana fahimtar mi duniyar ke a ciki har komai ya koma ɗiff a cikin kunnuwanta da idanunta…
__★★★__
A yayinda Master ke can yana angwancewa da gwangwaje sadakinsa da ranar ALLAH anan hukumomin jami’an tsaron jihar ne gaba ɗaya sukai zaman meeting akansa da yanda zasu ɓulloma al’amarinsa. Dan video ɗin daya saki a safiyar ta yau ba karamin tsaya musu yay a rai da zuciya ba. Tsare-tsare suke na tashin hankali da taimakon su A.G da suke iƙirarin sanin sirrinsa a baɗini, a zahiri kuwa suna nuna cewar ƙwazon aiki ne ya sakasu jajircewa da son ganin iyalansu sun dawo hannunsu. Dan a cikinsu iyalan Abba ne kawai ba’a ɗiba ba. Sai dai yanda Abban keta surutai tamkar zararre yana neman buɗe musu sirrika yasa A.G aika amintattun yaransa wai su bama su Abban tsaro saboda kar Master ya bibiyesu. Da wannan damar sukai amfani wajan sakawa a ɗirka masa allurar barci danya samu hutu. acewarsu jininsa yayi sama.