Uncategorized

TAKUN SAKA 25

     Wani irin daɗi ne ya tsarga zuciyar Hibbah ganin mace. Macen ma babba da zata iya kira uwa ko kaka. “Sannu mama” ta faɗa cikin girmamawa. Murmushi baba Saude tai mata tana ajiye trayn.

       “Yauwa ɗiyata sannu kinji. Yaya ƙarfin jikin naki?”.

       Da ɗan mamakin jin abinda tace Hibbah ta dubeta. Har zatai magana sai kuma ta fasa ta amsa da “Alhmdllh mama”.

     Baba Saude ta ce, “Masha ALLAH. ALLAH ya ƙara afuwa kinji. Babana yace ga abinci kici”.

      (Babana) Hibbah ta maimaita sunan a zuciyarta tana gyaɗama baba Saude kai batare data sani ba. Baba Saude da har cikin ranta kallon mara lafiya take ma Hibbah saboda yanayinta ta fice abinta ganin kamar batason hayaniyar. 

     Jin ƙarar rufe ƙofar yasa Hibbah ɗan zabura tana ƙoƙarin dakatar da ita. Sai dai harta fice abinta. Kanta ta dafe tana cije lips nata dan takaici. Sai kuma ta duba trayn abincin da ƙamshinsa ya gauraye ɗakin tunkan ma ta buɗe. Cikinta ta shafa dan babu abinda yafi buƙata a yanzu kamar abincin. Hakan yasata miƙewa ta nufi trayn da tunanin abincin kawai zataci ta samu ƙarfin yin tunani akan halin da take ciki a yanzun.

       Lafiyayyen abincine da ƙamshinsa kawai ya isa saka ma’abocin ganinsa kwaɗayin fara ci. Duk da zuciyarta na gargaɗarta da cewar kartaci na ɗan homo ne sai ta kasan daurewa saboda yunwa. Jikinta har ɓari yake ta haɗa ruwan tea duk da bai wani dameta ba ta fara sha. Dan tasan yanda yunwar nan ta cita shine kawai zata fara sha ta samu nutsuwa. Ai ko cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala wata irin zufa ta fara karyo mata. Yanda yake ratsa jijiyarta yasa dole sai da takai kwance na wasu ƴan mintuna. Sai da ya nutsu a cikin jikinta sannan ta sake miƙewa ta hau cin lafiyayyen breakfast ɗin shima. “Alhamdulillahi” ta faɗa a hankali jin uwar hanjinta ta ɗauka. Hakan ya sata miƙewa zuwa saman gadon ta sake kwanciya ƙananun zufa na cigaba da tsatstsafo mata.

           Idanu ta lumshe dan zuwa yanzun hankalinta ya fara dawowa jikinta. Sai kuma ƙwaƙwalwarta ta shiga kai kawon lissafi da tariyo abinda ya faru jiya akan bin bayan Abba da tayi. (Idan har lissafinta yayi dai-dai tun farko dama A.G da Abba tare suke. Da farko ta shiga rayuwar ƴan sanda a dalilin jefama masu power rider na’urar bibiya. A dalilin bincike da sukayi akanta suka gano ita ɗin wacece kuma ɗiyar wanene?. Ta wanann hanyar A.G yasan tana da alaƙa da Abba abokin shaiɗancinsa. Zata iya yuwuwa ya sanar masa komai da ya faru shine shi kuma yay amfani da wannan damar wajen saka A.G ya cigaba da amfani da ita wajen bata ayyukan Master da sukace yaronsu ne. Su kuma zasu dinga samun sirrin ƴan uwanta da Umminsu ta wanann hanyar suna musu illa da sunan suna bata kariya batare da sun fargaba.) “Tabbas babu tantama wannan lissafin nawa haka yake. Dan alamu ya nuna lokacin danai tracing wanann shu’umin shegen jami’in can ne ya sanar masa shiyyasa ya gudu. Shi kansa sun maidashi wawa suna amfani da shi da ƙuruciyarsa wajen gina kansu da wargazashi batare da ya sani ba. Wannan itace matsalar da *_MATASANMU_* suke fuskanta a wannan lokacin. Kuɗi da rashin aikinyine rauninsu. Azzaluman kuma sunda kuɗi da faɗa aji a hannunsu. Sai suke amfani da wannan faɗa ajin da kuɗin da matasan ke ƙishirwa su jawosu a jiki suna amfani da ƙuruciyarsu wajen sakasu zama ƴan ta’adda. Shima da alama wannan tarkon ya faɗa. Ya ALLAH!”. Ta kare maganar da dafe kanta da ya sara mata. Duk da sunce amfani suke da shi su gama mora su yadda dolene ta tonama guy ɗin nan asiri ma duniya shi da ubannin gidan nasa. Hakan na nufin kuma zata cigaba da zama a wajensa kafin burinta ya cika. Idan kuma ta zauna Yayunta da Umminta da ke a cikin tarkon su Abba fa?. Kuma hakan bazai yuwu ba sai ta kasance da su suma ta sanar musu gaskiyar shirinsa. Amma kuma wannan mutumin bazai bar hakan ta faru ba. Dan bai sato ta nan danta kuɓuta ba, saboda duk yana cikin shirin Abba na wargaza rayuwar ahalinta. 

     Hannu ta kai ta share hawayen da suka silalo mata. Sai kuma ta tashi zaune tare da mikewa ta hau safa da marwa a cikin ɗakin. Lissafin Abba shine sai ƴaƴansa sun sami ciki zai fara salwantar da rayuwar yayyunta. Hakan na nufin dole tayi wani abu kafin nan da wata guda kenan. Babban abinda zatai kuma shine nutsuwa ta fahimci nan ɗin da aka kawota. Na biyu tai iya ƙoƙarinta na tattara bayanai akan wannan mutumin acikin wata guda ɗin nan shi da iyayen gidansa. Na uku duk tsanani karta bama kowa wannan binciken idan ta kammala sai Yaya Abubakar. Na huɗu duk yanda za’ai tayi ƙoƙarin yin magana da ko ɗaya da ga cikin ƴan uwanta ne. To amma ta yaya? Tunda shi da kansa ya tabbatar mata kozata shekara nemansu bazata samu ba.

    “Ya rabbi ka agajeni”. Ta faɗa tana dafe kanta. Cikin sauri ta ɗan zabura sai kuma ta saki murmushi saboda tuno wannan dattijuwar data kawo mata abinci. Tabbas inhar tana da waya da ita ya kamata tayi kiran. A kuma sirrance batare da tsohuwar ta sani ba.

       “Kenan zan sato wayar”. Ta faɗa a fili tana ƴar dariyar farin cikin zuwan mafita ta farko a gareta…………✍

*_Alhamdulillahi na biya bashin wanann satin duka harma da ɗaya na wancan week ɗin. Asha hutun lahadi lahiya guys. Dangin su Master kuma zamu dawo da hirinmu ne ku kiyayemu????????????????????_*

   

TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*????????????????????????

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI……_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_

_NISHADI_

_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA’AYI NA DABANNE_*

*MAZA ‘YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI’AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300

2____400

3____500

4____700

5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*????????????????????????????????????????????????

#team ZAFAFA BIYAR????????????????????

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*

[ad_2]

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button