TAYI MIN KANKANTA COMPLETE HAUSA NOVEL

TAYI MIN KANKANTA 33

 

???????????????????????????????? *TAYI MIN ƘANƘANTA*

????????????????????????????????

*Zahra Surbajo*

*Tayi min ƙanƙanta bafa na kuɗi bane,shimfiɗar aurena shine na kuɗin,kuma acikin watannan zan sakeshi,ku dinga karanta headlines ɗin da kyau,*

*A hanzarta a siya kar ayi babu ku,ɗari biyar ne 500 kacal ba tsada,SHIMFIƊAR AURENA littafine daya kerewa saa,sunanshi daban haka ma taken dake cikinsa,na musamman ne, me kuke jira,ku siya ku karanta,ɗauke yake da ,magunguna na gyaranmu mata,salo domin burge megida da ƙawata shimfiɗarki ta Aure,sassanyar soyayya me tsayawa azuciya,abun al’ajabi,ban haushi,gamida ban dariya da tausayi duka acikin SHIMFIƊAR AURENA,hanzarta ku mallaki naku 500 ne kacal*

*Zahra muhammed nasir 2084024749 UBA*

*07044600044 a turo shedar biyan kuɗin tanan*

*33*

Hammad lallaɓata yake kamar ƙwai,koya ta motsa ya dinga jero mata sannu ba adadi.

Bacci ne yayi awon gaba da ita,yayinda hammad kuma idonshi ya bushe,ya cika da tsantsar mamakin ta yadda zahra ta iya ɗaukeshi da haɗamarshi,wanda yasan aykin da yayi ko cikakkiyar mace bazata ɗauka ba,amma segashi zahra ta bashi mamaki,lalle dole ya ƙaryata kanshi kan furucin tayi mun ƙanƙanta da yake faɗi.

Zumar daɗin daya kwasa ajikinta ko koya ya tuno se murmushi ya suɓuce masa,a fili ya furta “ba ƙarya babyna akwai sugar”

Wanka yayi ya kimtsa sannan ya dawo kan kujera ya zauna gadinta,dan bejin ze iya fita ya barta.

Be jima da zama ba ta farka,miƙewa zaune tayi, tana mutstsuke idanunta,ɗagowa tayi carab suka sarƙe ana juna,se murmushi yake sakar mata,wata azababbiyar kunya ce ta kamata,rufe fuskarta tayi da tafin hannunta tana murmushi.

Ƙarasawa gunta yayi ya ɗan rungumota,yana ƙoƙarin buɗe mata fuskar,sinne kanta tayi a ƙirjinshi,tana ci gaba da murmushin.

“no baby kar muyi haka dake mana taya zakimin rowar fuskar taki dana jima ina bege”ya faɗi yana leƙa idanunta.

Cike da shagwaɓa tace”to ni yaya ban so ka kalleni ne ay”

Murmushi yayi me sauti sannan yace”saboda princess ɗita bataso na kalleta?”

“kunya nakeji yaya Allah kuwa”ta faɗi kamar me shirin yin kuka.

“to shi yayan naki me yasa bejin kunyarki?”ya tambayeta yana shafa bayanta.

Turo ɗan ƙaramin bakinta tayi gaba sannan tace “beda kunya ne shiyasa”

“Au baby nine mara kunyar? lalle yarinyar nan kinga gurin baccina”hammad ya faɗi yana rungumota gaba ɗaya jikinshi.

Dariya ce ta kwacewa zahra wacce ita bata ma san tayi ba,sannan tace”au iya gun baccinka ma kawai na gani,hmmmm danƙari”ta faɗi tana jinjina kai alamun lamarin babba ne????

Cike da mamaki hammad yake kallonta,sosai dariyar tata ta burgeshi,har wani sanyi yakeji aransa,yace”to in banda gurin baccin nawa ina kuma kika gani nawa,kinga baby ki fice idona in rufe”ya faɗi yana murmushi.

“lalle ma yayan nan,ka mance dukan ƙartin da kaimin da kulkin ka shine har kake faɗin in fita idonka ko”tayi maganar harda ɗan hawayenta.

Zuwa yanzu dariya yake kamar cikinshi zeyi ciwo,da kyar yace mata”ni bani da wani kulki ƙarya kikemin”

Ayko nan da nan zahra ta shiga rantse rantse,kan yana da shi,shikuma yace beda shi,ƙarshe de daya bata haushi tace tana kamo wandonshi “joystick ɗinka ay shine kulkin naka”

Faɗowa hammad yayi ƙasa dan dariya,ko da wasa be ɗauka wayon zahra yakai rabin haka ba ma,itako duk haushi ya cikata yazo ya sata gaba yana mata dariya.

Miƙewa tayi a hankali,dan har yanzu da sauran zafin ta fara takawa zuwa toilet.

Da sauri ya miƙe ya isa gareta ya ruƙota yana faɗin,”muje in miki wankan babyna”ay kamar wacce ya tsikara,tayi saurin kwace hannunta tace”Allah kyauta,daga wanka se aƙara wankeni ko,to bana so”tana kaiwa nan ta buɗe ƙofar toilet ɗin ta shige ta kullo ƙofar,

Kan kujera hammad ya koma yana dariya,dan shi sosai rahar tasu ta burgeshi,dan Allah yasani yana son zahra son dashi kanshi besan adadinsa ba,wanda daga daren jiya zuwa wayewar garin ya nunko a zuciyarshi ba adadi.

yana nan zaune ta fito daga wankan,shi ya taimaka ya kimtsata,sannan ya ruƙo hannunta suka dawo falo,basu jima da zama ba gidan abincin da yay musu order suka kawo.

Shi suka ci suka sha lemu da ruwa sannan zahra tayi lamo ajikinshi,alamun bacci takeji,ɗaukarta yayi cak,ya nufi ɗakinta da ita,ya kwantar da ita ya manna mata kissa akumatu sannan yace”zanje mu gaisa dasu mummy,bazan jima ba zan dawo kinji babyna ki kulamin da kanki”

Murmushi tayi masa gamida gyaɗa masa kai,dan baccin yafara fin ƙarfinta,rufeta yayi da duvet,sannan ya fice ya nufi gidan iyayen nashi cike da farinciki.

Muje zuwa.

Surbajo for life.

[ad_2]

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button