TUN INA KARAMA Complete Hausa Novel

To haka nan zan makale ko ajikin tayar motar yusuf ne nima in bishi katsina gidan ummah don nasan akwai rigima kwance mai zuwa ya biyoni????
???????????????????? masha Allah takuce sa’ar mataaaa ina gdy gareku readers ngd sosai da kulawarku.????
TUN INA KARAMA ????????????????????????????????
By sa’adatu Bello saadatu@gmail.com!
Page 14
…….koda suka kama hanya babu mai mgn cikin su kowa da nasa tunanin arai umar tuki yakeyi amma zuciyarsa fal da tausayin dan uwansa kuma amininsa gsky ne yusuf yana tsananin son littel amma ya kamata ya nuna mata ita ce abokiyar rayuwarsa ta har abada amma ba komi zai kara ankarar da shi batare da wata matsalaba, yusuf kuwa irin tashin hankalin da zai tarar yake tunanin fuskanta a haka har suka kusa shiga katsina wajan karfe 8:30 na dare suka shiga cikin katsina umar ne yace to kadai tanaji amsar da zaka ba ummah ko?batare da ya kalli yusuf ba yayi mgn “haba frnd ai bani da wata amsa wacce ta wuce in bata hkr sbd koma me xance mata ba yarda zatayi dani ba ” umar yasake kallonsa yace ni kasan ma babbar damuwata?a’a yusuf ya bashi amsa “to walhi marin da tayi ma littel umar ya fada tare da daukar abun da muhimmanci wanda nidai a tarihin rayuwata ban taba ganin haka ba tsakanin ummah da diyarta amma gashi kayi abunda har haka ta faru tsakaninsu kaga ko dole ummah taji haushinka sosai yusuf duk da ummah itace mahaifiyarka walhi bazai hana ta hukunta ka ba akan yarinyar nan tunda ummah mace ce mai son gsky da rikon amana haka Abba shima kasan kaifi daya ne don haka ina mai shawartar ka da idan Allah ya baka hawwa kada ka jawo wani abunda zaizo yazamar maku matsala sbd ita dai hawwa kai ne zaka dorata akan turbar duk abunda kake so wanda dama tun yarintar ta kaine idonta don haka plss ka amshita amatsayin makauniya kaine idonta abunda yasa kaji ina fada maka haka nayi imanin jamila da mahaifiyarta bazasu barku ba amma ya kamata ka daura damarar yaki dasu tsakaninka da iyalinka.
” gsky ne umar yusuf ya fada tare da cewa insha Allahu zanbi shawarar ka ngd da kauna.kafadar shi umar yadan buga yace kai mal meye na gdy bayan biyana zakayi gaba daya suka sa dariya dai dai lkcn suka iso get din gidan su yusuf sunayin horn baba mai gadi ya bude suka shiga ciki tare da gaishe shi ya amsa cikin mutunci suna isa wurin parking sukayi suka fito gaba daya kamar basu da wata damuwa ledar da mami ta basu suba umma ce umar ya dauka tare da cewa to ango shiga gaba cikin zolaya “a a yusuf yace saidai mu jera ka idan ummat ta tashi maido mu sai ta maido mu tare ko haka suka shiga falon gidan tare da sallama Asabe ce cikin falon tana ta faman yima nabila tsiya wai bata da aiki sai nemo girke girken zamani awaya tace suma sai sunyi irin shi maimakon ta nemo na gargajiya.amsa sallamar sukayi tare da yi masu sannu da zuwa kaka Asabe hira kukeyi hakane?yusuf ya tmby eh walhi tabashi amsa Alh karami ya hanya ya kuka baro su mamin kaduna?Asabe ta tmby cikin walwala yace lfy klau suna gaisheku gama wani sako nan ki mika ma umma to in sha Allahu ta amshi ledar dake hannun umar ta wuce.” Umar ne yace ma nabila ina littel?cikin jin dadi tace tana daki taki fitowa ummah fa yasake tmby tana part dinta tana sallah taba shi amsa.”ok yace tare da cewa muje ki rakamu wurin littel kafin ummah ta fito to ta amsa tare da mikewa tayi gaba shikam yusuf saurarensu kawai yakeyi hankalinshi na wurin yaga ya littel din shi take suna tafiya shima yabi bayansu.
Kwance take ta juya bayanta in banda hawaye babu abunda ke zuba a idanuwanta wanda sun maki tsayawa sallamar nabilace tasa ta tasake lafewa agadon jin muryar umar ne da ya kira sunanta littel baki da lfy ne ya tmby tare isa gaban gadon yasa ta juyo sukayi ido hudu da yusuf dake bayansu cikin azama ta tashi da sauri tayo kan yusuf kallonta umar da nabila sukeyi cikin mamaki ta tana zuwa ta fada jikinshi ta fashe da kuka mai cin ran mai saurare baiyi yunkurin hanata ba ya riketa shima ji yake kamar ya kurma ihu sbd tausayinta “umar ne ya girgiza kai ya kalli nabila almar su basu wuri ya raba ta gefensu ya fita itama nabila ta bi bayan shi tare da jin dadin samu farin cikin kawarta bayan fitar sune yusuf ya dago ta yace my dear wife, gabanta ne ya fadi cikin sauri ta dago kai ta kalle shi daga mata gira yayi tare da murmushin sa mai tsada ya ce to be insha Allah kuka ta sake fashewa dashi hankicib ya ciro a aljihunsa ya cigaba da goge mata hawayen dake zuba littel ya kirata yace ko baki auren yayanki?cikin jin kunya ta juya zata bar wurin saurin riketa yayi kinga shikenan duk inda xani sai mu tafi tare babu mai hanamu ko?ya tmby ta rufe fuska tayi tace bacewa kayi baka kara dawowa gidan nan ba haba littel ni na isa wasa fa nayi maki turo baki tayi tace shine kasa har ummah ta mareni ta karashe mgn hawaye na zubar mata kuma har yanzu fushi takeyi dani matsawa yayi ya zaunar da ita kan gado shima ya zauna yana jin wani yanayi na da ban dan gane da ita shiyasa yayi dabarar raba jikinsu ya zaunar da ita cikin kulawa yace babu abunda zai rabani dake hawwa kuma me yasa kika ce ma ummah bata son ki ?ai kinga dole ranta y baci don haka mu duka munyi laifi ya kamata muba umma hkr kuma koda wasa kada ki kara fadar haka kinji ko?yanzu kinga da Abba ya dawo mgnr auren mu za ayi kinga ai gidana zankai ki saidai ki rinka zuwa kina gaisheta ko?cikin jin kunya nace kullum ko?dariya yayi yace haka kike son ko?eh na amsa mashi yace gud
Agogon ahannusa ya duba yace bari inje wurin umar daga nan mu gaisa da umma don banganta ba nima mikewa nayi nace falon zani, muna fita muka samesu falo gaba daya bayan umar ya gama ba ummah hkr tare da ban baki kuma da kara jaddada mata son da yusuf yakeyi ma hawwa dama kuma Abba ya kirata tunda sukayi mgn da mami ya fadi mata komi ta kuma yarda hakama mami ta kara kiranta ta bata baki da lallashi don haka zuciyarta fes ta daina jin haushin yusuf tuntuni haka ma hawwa bata jin haushinta kawai dai tausayin yarinyar takeyi dakuma data sanin marin datayi mata bawai fushi takeyi da itaba kawai kunyar ta takeji koba komi ai matar danta ce kuma son da take ma danta ne yaja ta fada mata haka.tana cikin wannan tunanin ne suka fito gaba daya cikin jin dadin ganinsu “ummah tace to uban yan rashin kunya kaje ka taho da ita ko?ai ganin yanayin ummah yasan ta sako baiyai wata wata ba yaje gabanta yana kwasan gaisuwa da tuba haka su Asabe da umar nabila sukaita dariya niko inda nake tsaye ban kara motsi ba jinayi ummah tace auta duk da yayan naki ya dawo fushi kike dani kuma?rufe fuskata nayi na karaso wurinta na kwantar da kaina a cinyarta nace umma nima na tuba bazan kara ba shiiiiit naga ta dora hannunta abakina tace kada in karajin haka ya wuce ta kalli yusuf ta dungure shi tace tashi kabani wuri ja iri mara kunya haka ya tashi yana sosa keya umar yayi ma su umma sallama don dare ya farayi kuma yace ma yusuf dama gida zai wuce haka suka fita suna dariya.bayan sun fita ne umar yace to mu godema Allah da komi yazo cikin sauki haka ya rakashi yace saidai ya dauki mota shi bazai raka shi ba don ya gaji dariya umar yayi a amshi key din ya shiga ya daga masa hannu ya fita ya wuce gida.