TUN INA KARAMA Complete Hausa Novel

Kuma yake kyautata mata, itama haka zamansu yake cikin mutunci da girmama juna.to amma duk da haka basa shiri da hjy mariya sbd ita gsky halinta ya sha banban yan uwanta, ita mace ce wadda tasa duniya gaba bata tunanin komi sai son zuciya, sbd tana fita kasashe tana haduwa da kawaye sun zugata tana ganin kowa ma bai isa ba.sbd haka ne basa shiri da Alh bashir yayanta shikam duk harkar wani shashanci baya cikinta.kuma shi mijin nata sbd son dayake yi mata baya iya magana duk yanda take so to haka za ayi Allah ya kyauta.itama mijinta dan katsina ne nan suke zaune a le out.shima Alh bello yana katsina tare da iyalinsa, sai hjy rabi’atu dake aure a kano ita mijinta dan kano ne a nan kundila suke da zama anan take aikinta a ma’katar lfy dake jaha.
Allah ya Albarkaci Alh bashir da haihuwar yara uku aunty zainab ce babba sai yusuf sai kuma Nafisa wadda itace auta.rayuwar farin ciki da kaunar junan su haka rayuwa take tafiya.hjy khadija su uku ne wurin mahaifinsu Alh suleman shine babba sai ita umma sai kuma babana wanda shine kaninta Alh mansir shine mahaifina Allah yayi masa rasuwa ne a sakamakon hadarin mota.daga kaduna zuwa katsina, Allah ya gafarta ma iyayenmu yasa Aljannace makoma Ameen ya hayyu ya qayyum.
To lkcn mahaifina shi yana kaduna ne zaune tunda can yake aiki tare da mahaifiyata wadda dama it yar kaduna ce anan ya aureta alkcn daya rasu an haife ni amma shekareta daya lkcn.sbd haka iyakar zaman danayi da mahaifiyata kenan ana yayeni hjy khadija tace lallai sai an badani haka dai mamana tayi kawai ci sbd karamcin yayar mijin nata ta hakura ta bada ni haka na tashi ina ganin umma itace mahaifiyata tunda koda wasa bansan umma da Abba ba basune iyayena ba tunda ko yaransu ban taba ji abakinsu ba kowa yana sona.nasan dai akwai mamin kaduna tunda haka naji suna ce ma mamana.kuma sai inji suna ce mata mamin yusuf naga kuma yawancin zaman shi acan wurinta ne .na tmby umma sai tace mani ai ita mami itace mamanshi dana dameta da tmby sai tace tashi kibani wuri harga Allah ban kawo komi araina ba.mami tayi aure ta auri wani aminin dad dina wanda shima matarsa wurin haihuwa ta rasu shima mutumin kirkine .amma mami da kyar ta amince da auren shi dayake kuma Allah ya kaddara haka ta auri Alh isma’il shima dan zaria ne amma enginer ne yanzu haka yana Abuja can yake aiki amma nan yabar mami a kaduna sbd tace tafi son zaman kata anan tare da yaranta saidai yarinka zuwa weekend ko kuma wani lkc suje su danyi hutu su dawo
Diyarshi wadda matarshi tabari itace babba wurin mami sai wadanda ta haifa guda uku yaran shi hudu amma baka cewa mami ta haifi ummi ba sai Abdul da khalid da halimatu sune yaran mami
Hjy mariya yaranta biyu jamilace babba sai kanwarta nabila sakamakon tsada haihuwa datayi wai ita bata son ta tara yara kuma su tsaida mata harkokinta nabila ba halinsu daya ba da jamila shiyasa gaba daya basa shiri shiyasa koda yaushe tana gidan umma muna tare ita kuma hjy mariya ta tsani hakan shiyasa ko hidima akaje ta rinka yima umma habaici kenan ita kuma bata kulata.
Masha Allah ku biyoni yawan comment yawan typing ???????????? takuce sa’ar mataaaa????
TUN INA KARAMA ????????????????????????????????
By sa’adatu Bello saadatu99@gmail.com!
Page 8
………..yaya yusuf da umar cousins ne sbd umar shine babba wurin Alh bello kanin Alh bashir baban yusuf, tare suka taso tun suna yara babu abunda ke raba su sai in yazama dole.ko karatunsu tare sukayi shi india couse dinsu ne ba daya ba shi yusuf permacy ya karanta shi kuma umar Account ne.duk da haka dasuka dawo gida nigeria suna tare acompany daya wanda dama na su ne company babu abunda akeyi cikin shi sai hidimar magunguna sakamakon dama abunda yusuf ya karanta kenan.kuma suna samun kwangila daga gwamnati sbd babu kasar da basu kawo magani kuma masu inganci basu yarda su hada hulda da kasashen da suke yaudarar kasarsu sbd kishin kasa.
Jamila tare suka taso don itama dakadan suka girmeta ko a skul shekara daya ce tsakaninsu da ita itama india tayi karatu tare da su yusuf amma ita kwararra likita ce yanzu haka tana cikin likitocin da ake ji dasu a cikin jihar katsina tana aiki ne da fedaral medical center dake cikin garin katsina.jamila tana son yusuf sosai arayuwarta sbd irin mazan da mace zatayi alfahari dasune.kuma tanada wani hali duk abunda take so to bata boyewa ko jin kunyar nuna mashi kuma tana da son kanta da yawa da son zuciya kamar yadda ta gani wurin uwarta.nidai na taso hannun ummatah da Abbanah wanda su nake ma kallon iyayena da suka haifeni.sbd karamci irin na dangin mamana tunda ko su ban taba jin sunce wani abu ba na dangane dani kawai dai abunda nafara fahimta ina dan kama da mamin kaduna amma bana sawa araina akwai wani abu kuma ina jin ina son matar sosai araina amma tunani nako don tana mahai fiyar yaya yusuf ne.na tashi cikin so da soyayyar yan uwana su aunty zainab.
Haka nayi krtuna primary da secondary anan katsina lkcn dana gama secondary ne ina da shekara 17 kuma ashekarar akayi mani aure da yaya yusuf wanda dama wai jirana kawai yakeyi sbd duk matan dake bibiyarsa baya ma kula su ciki ko harda jamila.bai so maganar aurena yanzu ba amma hakan bata samu ba.
Sbda yaso ace na fara jami’a kwatsam sai gashi ya canza shawara sbd wani dalili nashi.hakan yasa aka gaggauta yin auren mu.
Bana manta wannan ranar da akayi bikin wata cousing dinmu Aisha wanda aranar ne ne komi ya canza a sakamakon wani hoto da da jamila ta hada tare da wani saurayi ta turo ma yusuf shi kuma lkcn yana gida.abunda ya faru, mun shirya nida nabila kanwar jamila zamuje wurin dinner to dama gsky itace kawata sai na nafisa autarsu yusuf tunda duk kanmu daya kuma mun shaku da juna sosai, to nafisa tana wurin aunty zainab a Abuja.mun gama shiryawa muka fito daga dakina muka samu ummah tana zaune tana kallon tashar sunnah tv tana ganinmu ta fadada murmushinta cikin kulawa tace masha Allah kunyi kyau yan matana cikin jin kunya muka rufe fuska tare da isowa kusa da ita muka zauna gefen ta muka sata tsakiya.cikin shagwaba wadda tariga ta zame mani jiki nace ummatah ina yayana?tare da kallon kofar da zata sadaka da sashin shi cikin kulawa tace yaje masallaci amma naga alamar kamar ba zai fita ba, yanzu dai bari in sanar ma Adamu driver ya kaiku tana magana tana kallon wayarta dake caji kafin tayi ta kara mgn na mike na dauko wayar na mika mata.bugu daya ya dauka ta sheda masa abunda zaiyi ya amsa da to hajiya mikewa mukayi tare da yi mata sallama tace kada mu wuce karfe tara komi mukeyi insha Allahu muka ce tare da fita waje muna fita muka ga Adamu yana kokarin fiddo wata katuwar jeep prado blue sai shaning takeyi har inda muka tsaya ya iso ya bude mana muka shiga baya muka zauna tare da gashe shi ya amsa mana cikin walwala baba mai gadi ya bude mana muka fita sai liyafa place inda akeyin dinner .
Fitarmu kenan shikum yusuf ya fito daga masallacin kofar gidanmu yana fitowa ya hangi motar gidanmu ta fita daga get cikin mamaki yace to wa yafita yanzu a wannan motar?cikin hanzari ya shiga cikin get din gidan tare da sallam baba mai gadi ya amsa kafin yace komi yusuf yace baba waya fita da mota yanzu cikin mutunci yace ai yallabai Adamu ne hjy tace yaje ya kaisu autarta wurin biki da yake duk ma aikatan gidan haka suke kira na da autar hjy.ok kawai yace ya shige cikin gidan tare da sallama umma ta dago kai tare da amsa masa sallamar babu walwala a fuskarsa ya zauna kusa da umma yace umma saida kika bar yaran nan suka tafi wurin dinner nan ko?”eh tace ai banyi tunanin zasu dade ba kasan hawwa ma da ba son hayaniya ne da ita ba.ai umma da kin kinkirani sbd darene kuma kin san jamila zataje tana iya yima su hauka tunda sakarai ce cikin damuwa ya karashe mgnar.”tace ba komi insha Allahu lfy zasu dawo amma duk da haka shirya ka dawo da su saikace ma Adamu ya taho gida “ok yace tare da mikewa zuwa dakin sa ya canza kaya tunda dama kafin yaje masallaci yayi wanka.yana shiga ya shirya cikin kananan kaya wanda sun karbi jikinsa yayi kyau sosai yana shiri ya na kallon agogon dake manne a dakin.ya dauko perfumes yana fesawa wayar shi tayi kara alamar text ya shigo da kuma hasken da wayar ta karayi.kamar bazai duba ba kuma kawai sai yaji yana son ya duba koda ya dauki wayar sai yaga ashe sako ma na whatsapp ne kuma sunan jamila ne ke yawo akan sakon kamar zai aje wayar sai kuma yayi tsaki mtss ya bude sakon