TUN INA KARAMA Complete Hausa Novel

Ba ” nabila tace ma ummah Adamu yace rai bace yaya yazo cikin mamaki tace to koma menene ai sai ya dawo mani da ita gida ko.bata rufe baki ba na fado falon da kuga gaba daya juyo sukayi cikin mamaki suna tmbyta me yafaru?cikin kuka nace umma kada kibari yaya ya fadi Abbanah ina son aure na hade hannuwa na alamar rokonta.cikin rashin fahimtar maganata ta zaunar dani kan kujera nabila kuma ta zauna gefena tare da rike hannuna “ummah tace wai meke faruwa?waye baki so kuma?” Yusuf ne ya shigo tare da sallama amma fuskar nan tashi babu annuri sai ji sukayi yace dama kin daina kuka ki fara shirin aurenki.”cikin daga murya umma tace wace by irin mgn kakeyi yusuf?me ya faru ne?”umma ki tmby ta abunda tayi dama ni nace abarta ta fara jami’a to yanzu ra’ayina ya canza zan jira dawowar Abbah tunda ya fara mgn umma ke kallonsa tana nazarin irin soyayyar hawwa tsantsa a idon shi da kishin ta cikin kauda kai umma tace baka isa ba yusuf babu wanda zai takurata da mgnr aure”amma umma ya kamata ki saurareni mana”cikin tsawa tace banda lkcn saurarenka zai kara mgn ta daga masa hannu tare da cewa ya isa haka bai kara mgn ba ya nufi sashensa yana jin wani zafi a zuciyarsa ta juyo tace na nabila tashi ku shiga daki ku kwanta.
Masha Allah don Allah frnds kuyi hkr da typing din nan ba yawa sakama kon ina cikin hidamar biki ne next page zan biya bashi.ku biyoni ???????????? taku ce sa’ar mataaaaa????
TUN INA KARAMA ????????????????????????????????
By sa’adatu Bello saadatu99@gmail.com!
Page 11
……….( koda ya wuce daki yana shiga ya cire kayan jikin shi ya wuce toleit yayi wanka, wanda ya zame mashi jiki duk idan zai kwanta sai yayi wanka.haka ya gama ya fito daure da towel ajikinsa yana daure da daya yana kuma tsane jikinsa da dayan saida ya gama goge jikinsa sanna ya dauko mai lotion din shi mai dadi da laushi yabi jikin sa ko ina ya shafa sanna ya dauko spray dinsa na jiki ya fesa ko ina haka ya gama shirinsa na bacci ya dauki wasu kaya T shit fara da shot nick yasanya ya dauko lapton dinshi ya dawo falo ya zauna da niyyar duba wani aiki da yake son kammalawa amma abun ya gagaresa gaba daya ji yayi baya iya aiwatar da komi, haka ya tashi yakoma cikin bedroom din sa ya kwanta ba don yana jin dadi ba.tunanin kawai yakeyi aransa ina zai samu mafita?yasan dai umma ba sauraren.gsky dana bi shawarar Abba dayace in fito ayi mani aure da hawwa da haka bata faru ba gashi tun ba’aje ko ina ba abubuwa na shirin lalacewa .naso in barta ta fara karatu domin ta kara samun wayewa ne amma kash, kishinta bazai barni ba ina sonta itace mace ta farko dana ke jinta araina amma bata sani ba ina ganin tayi kankanta da zan nuna mata wacece ita agareni.don har yanzu kallon dan uwanta takeyi mani na jini ba wai ta fahimci sona take ba.gsky nayi kuskure yakamata hawwa ta san tun tana karama nake dakon sonta.
Kuma ai ina nuna mata banbanci tsakaninta dasu nabila da nafisa kuma me yasa dana tafi india kullum mukayi waya sai tayi kuka wai in dawo kuma umma tana fadi mani in rike alkawari kada in yarda wata mace ta shiga rayuwata bayan hawwa don ta lura hawwa akwai soyayyata mai tsanani atare da ita gsky akwai sona ranta saidai bata fahimci sona take ba.haka dole ya samu mafitar cewa mami ce kadai zata nuna ma Abba ya amince cikin sauri ayi auren nan namu.dole ne gobe insha Allahu inje kaduna in samu mami da mgnr.haka bacci barawo yayi gaba da shi.itama hawwa da nabila haka suka shiga daki tare da tunani kala_kala wanda mamaki ya hana su kwanciya kowa da abunda yake tsakawa akan abunda ya faru, haka nabila ta zaunar da hawwa bakin gado itama ta zauna cikin damuwa”ta dafa kafadarta tace hawwa kiyi hkr insha Allahu komi zaiyi daidai amma ki bari kawai koma waye yayi mana wannan abu Allah zai tona masa asiri”cikin kuka nace ni walhi nabila yanda naga yayana ya dauki abun ne tsoro ya kamani yanzu idan har Abbanah yaga wannan pic din ai na shiga uku nabila”nabila tace kema kinsan yaya bazaiyi haka ba kawai dai abunda na lura kishi ne kawai ya ruda yaya, cikin hanzari hawwa ta daga kai ta kai dubanta ga nabila “tace kishi kuma?jinjina mata kai nabila tayi alamar gsky ne ” to ni sbd me zaiyi kishina?sbd yana sonki to ai kuma yana sonku A a hawwa yana mana so na yan uwantaka ne amma ke soyayyace tsakaninki dashi.”haba nabila ni bai taba cewa yana sona ba ai ba sai yace ba mu da muke tare daku mun gane ai juya wa nayi na kwanta nace bar mgnr nan saida safe.
Haka muka tashi da asuba mukayi sallah da addu’oin mu tare da tilawar alkur’ni mai girma, wanda dama mun saba saida gari ya fara wayewa muka tashi.na kalli nabila nace mata sis zan dan koma in kwanta don kaina ke dan ciwa ok ba damuwa tace ki kwanta ki huta ni zanje in taya Asabe break.to shikenan nace na koma na kwanta.nabila tana shiga sashen umma ta shiga dakin tare da sallama.umma tana hada wasu kaya da zatayi amfani dasu ta juyo ta amsa ma nabila sallam cikin fara’ da kulawa nabila har kasa ta tsugunna ta gaishe da umma bayan sun gama gaisawa na ta tmby hawwa ko lfy nabila ta amsa da bacci ne ta koma ta kwanta”umma tace to ba damuwa kema ki koma ki kwanta mana a a ummah zan taya Asabe ne break to shikenan ki sameta kichen din.yaya yusuf koda ya tashi da asuba yaje masallaci ya dawo ya gama abunda yakeyi ya shirya tsab tunda ya gama yanke hukuncin tafiya wurin mami kaduna.bayan ya gama ne ya fito ya wuce part din ummah ya shiga dakinta tare da sallama ta amsa masa ba yabo ba fallasa bayan sun gaisa ne yake sheda mata tafiyar da zaiyi kaduna .hmmm kawai tace tare da fadin Allah ya tsare hanya yasa a adawo lfy.Amin ya amsa mata tare da jin dadin addu’arta gareshi, sbd duk fushin da ummah tayi bata fasa yima yaranta addu’a haka ya tashi duk da baida wata walwala amma yaji ranshi ya fara sanyi.bayan ya futa ta girgiza kai aranta tace zan nuna maka darajarta kafin in tabbatar maka da aurenta bazan bari ka rasata don ita ta dace da rayuwarka insha Allahu.bayan ya fita yaje wurin motarsa tare da budewa ya saka jakar lapton dinsa ya shiga motarsa tare da Addu’a yayi rivos ya nufi get baba ya bude masa tare da ftn alkairi ya amsa da amin
Yana fita bai zame ko ina ba sai wurin umar.to frnd dama shiyasa nace maka indai har zaka saurari jamila to zata samu galaba akanka yanzu kai ka yarda da wannan pic din?da har zaka tada hankalinka?umar yace ni dai ban yarda ba walhi amma kuma auren naku shi zafi tun wuri kafin wannan shidaniyar ta lalata komi ya kamata ka baiyana ma hawwa tun tana karama kake kaunarta simple.yusuf ya sauke ajiyar zuciya tare da kallon agogon hannunsa yace yakamata mu wuce ko?”umar ya daga kai alamar eh haka suka fito daga part din umar inada suka samu Ammi a falon gidan su umar suka gaisheta cikin girmamawa Ammi tace yusuf yasu hjy ya amsa da lfy klau Ammi “to masha Allah Allah ya taimaka suka amsa da Amin suka mike tsaye zasu tafi umar yace Ammi zamuje kaduna sai yanda ta yiwu to ba komi Allah yasa adawo lfy amin suka amsa suka fita tabi su da kallo tana jin dadin alakarsu sosai haka suka shiga motarsu suka fita umar na tuki sai kaduna garin gwamna sai muce Allah yasa a dace yusuf.