UBAYD MALEEK 31

Afia ta kalla zatayi magana 

Afia tarigata da cewa”

Ina wuni mum.

Kin amsawa tayi tana cewa”

Wannan shine sabon manner dinki da  farhat?

Da mamaki afia ta kalleta tace”

Sabon manner kuma mum?

Maida kallonta tayi kan farhat dake jikin NURU tana kallon lailah da dukkanin hankalinta sbd tanason zuwa gurinta tana shakkar irin tsawar da lailan ke Mata wani lokacin duk Bata mantaba sbd lailah batason Ana fado Mata ajiki kokuma yaro yace koyaushe Yana cikin jikinta.

Farhat kixo ki gaida mum.

Wani kallo lailah tayiwa NURU wadda gabaki daya Bata sake kallon inda lailan takeba sbd Jin take gabaki daya dakin ya gundureta ga Mr jalal ya fita ta zare hannunta daga na farhat da har lokacin take tsaye bataje gurin mum dinba ta nufi gurin Imran daya bude idanuwansa alokacin ya zuba Mata ta qarasa gurinsa ta zauna kan sofa ta qaqalo murmushi daqyar tace”

Ka tashi kenan Yaya jikin?

Bai dauke kallonsa daga kantaba ya gyada kai Yana miqawa farhat hannu cewa tazo.

Lailah zuwa lokacin ranta yafara baci sbd kowa sai acting dumb  yakeyi ta gyara zama ranta nafara baci akan afia tace”

Afia nice na haifeki komai girman dakike ganin kinyi Dan haka you better stop acting dumb with me kafin ranki ya baci kokuma kinason nunamin zama da bayi kin manta girman uwarki,…

Da mamaki afian take kallon mum din cikin rashin sanin abinyi tace”

Mum please idan wani yabata Miki Rai acikinmu daga zuwanmu kiyi hkr Amma wlh Ni bansan me mukayiba anan,

Farhat kije gurin mum ki gaidata nace….

Just shut up afia

 before I lose my cool ki fita daga gabana Dan Naga gabaki daya kin rasa tarbiyanki Kamar Ni Ina Miki magana kina cewa Farhat ta gaidani sbd nace Miki gaisuwan ne agabana kawai.

Hawayene suka ciko idanuwan afia sbd gabaki daya batasan metayiba da mum din keta faman wannan janye janyen ta bude Baki cikin rawar murya tace”

Kiyi hkr mum Amma dai kaman kina saukemin fadan da banawa bane.

Sai alokacin NURU da duk takejinsu ta Dan waiwayo afia din takai hannu zata dafata sbd ganin yanda hawaye suka tsinke Mata

Lailah ta aika Mata wani qanqantaccen kallo tana cewa”

Excuse me miss wannan tsakanin uwa da ‘ya ne stay within ur limits ok 

Bana saka trashes cikin al’amurana

For God’s sake ma meyasa haryanxu kikeda auren MALEEK akanki bayan duniyama tasan bazaki tana zama Matar da maleek zai iya zama da itaba 

Ke yarinya ce bazaki gane hakan ba Amma nasan Zaki gane kalmar pack and leave sbd ma nafasa komawa San Francisco zandawo gidan sbd afia na wannan little ant din sun dauki wani hali da bazan dauka ba..

Jekadi da padima dake bakin kofa suna Jin komai dadin duniya yagama kashe padima duk da Jin takeyi Kamar tashiga tayiwa lailan mugun duka Amma dai Kuma yanda take nuna isarta akan ‘yayanta da NURU ta mallake yasata Jin Dadi taji inama tanada ikon shiga dakin taga yanayin NURU sbd har lokacin NURU Bata juyo ta sake kallon ko gefenda lailah maleek takeba sai lokacinda tace zata dawo rayuwar MALEEK NURU ta waiwayo ta kalleta daidai suka hada ido lailan ta gyara zama zatayi magana aka turo kofar data Sanya NURU kallon kofar da idanuwanta dasukai jajir sukai ido biyu da MALEEK Wanda Mr Omar ya budewa kofa 

Shima ita ya kalla dakyau sbd baisan da zasuzo asibitin ba Amma ganin su jekadi a waje yasa yasan suna ciki.

Dauke kanta tayi tareda maidawa kan Imran sbd rashin sanin abinyi Dan gabaki daya dakin jintake numfashinta a toshe yake.

Lailah dake zaune har lokacin ta zubawa maleek fararen idanuwanta tana jiran abinda zai fara fitowa daga bakinsa idan ya idanuwansu suka Shiga cikin na juna.

Da fararen idanuwansa ya kalli Imran dake kokarin tashi Amma Babu me kamasa sbd NURU ce kawai a kusa dashi afia har lokacin tana gaban mum dinsu hawaye take na baqin cikin wannan halin da mum ta nuna.

Cikin kamewar murya Kai tsaye MALEEK yace”

Kana samun sauqi kenan,

Allah yaqara lafiya.

Maida kallonsa yayi kan NURU dataqi waiwayowa ta sake kallon kowa ahankali yace”

Muje.

Dagowa tayi ta kallesa direct cikin ido kafin ta dauke tana miqewa tsaye da wayarta a hannu ta wuce batareda ko sai anjima tayiwa Imran ba sbd a rayuwarta Bata taba yin mummunan danasaniba Kamar zuwanta asibitin Nan yau.

Tana fitowa Jekadi ta taso zata bita Mr Omar yayi saurin Yi Mata hannu Yana  nuna Mata MALEEK da ido Takoma ta zauna tana cewa”

 Allah ya tsare hanya MALEEK.

Harya fita ko afia alamu Basu nuna yasan dasu a dakinba bare lailah harya fice,

Ita kanta afia tashiga shock

 ta dago ta kalli mum dinsu da Bata nuna damuwaba sbd tasan halin MALEEK dama Dole saita fuskanci fushinsa kafin yasan yanda zata sauko dashi dakanta sbd soyayyarta me qarfi dake ransa,

Ganin NURU yanzu datayi yasa taji bazata iya komawaba tana buqatar kasancewa da maleek yanzu Dan kuwa batai tunanin NURUn takai hakanba duk da yarinyace Amma tanada wani irin kwarjini me fizga.

##MAMUH#

 

***************Washe gari tunda safe Kamar kusan dai yanda ta Saba kitchen ta nufa aikin breakfast tayi su Fana da mum Sarah na tayata suka hada abincin safen saina maleek data hada Masa daban ta jera a tray sbd har lokacin Bai fara saukowa qasa cin abincin tareda ‘yayansa Kamar yanda ya Saba ba 

Ga afia har lokacin batasan yayi rashin lafiyaba ko da safen taje har sama ta gaidashi Amma bataga komaiba lafiya kalau ta gansa.

Tana gamawa tabarwa Fana aikin jera abincin a dining ita ta dauki nasa ta fito saidataga alamamun afia na daki kafin ta haye sama cikin sa’a kuwa baya palon saita ajiye ta juya ta fitowarta.

Tana saukowa dakin Farhat ta nufa Dan har lokacin bacci take itama kusan gidan yau kowa na gida tunda hutu suke.

Zaunarda farhat din tayi tana cewa”

Sweetie kitashi Haka fa ko kinmanta yau zamuje yawo.

Cikin bacci ta bude Yan idanuwanta tace”

Aunt ai ba yanzu zamuba Saida Rana kibari muyi bacci Mana.

Murmushi tayi kawai tareda kyaleta ta wuce toilet dinta anan tayi brush ta fito ta nufi dining Bata jira kowaba ta zauna taci ta koshi ta tashi ta nufi dakin padima dake zaune tana latsa wayarta ta dago suka kalli juna tasaki murmushi tace”

Ranki ya dade ta tashi kenan.

Batajin biyewa padiman Dan haka ta datse zancen da cewa”

Padima idan kinci abinci ki shirya anjima zamu fita ko.

Dan Dadi taji ta qaraso gurin NURUn tana cewa”

Inane zamuje?

Ko amsa Bata bataba ta juya ta fice tana cewa”

Ba takamaimai ko Ina aka samu zuwa za’ayi.

Qaramin tsoki padima taja tana dawowa ta zauna bakin gado tana cewa”

Duk zanyi lokacinkine daga baya indai fara Isa komai yashigo hannuna tukuna.

Dakinsu Takoma ta tararda afia zaune tana waya cikin damuwa take cewa”

Inshallah anjima zamuzo aunt Allah yabashi lafiya yasa kaffarane duk wannan.

Kashe wayar tayi tareda dagowa ta kalli NURU data tsaya tana kallonta cikin son Jin wayene baida lafiya taga duk afian tashiga damuwa.

Numfashi me zafi ta fitar kafin ta zauna bakin gado cikin sanyi tana cewa”

Jikin Imran ne yayi tsanani  tana cewa sai anyi Masa aiki,

NURU inaga duk wannan nice sanadi.

Kallonta NURU tayi jikinta amace sosai itama da tausayin Imran din sbd tabbas tasan Imran na Mata so me qarfi Amma ya suka iya Haka qaddara ta taho saidai hakuri.

Muryarta a Sanyaye tace”

Kidaina fadan haka wannan duk yin ubangiji ne haka ya tsaro dama 

Shima Inshallah zaiji sauki ahankali zai Saba ya rungumi kaddara da zaran yasamu wadda zata kula dashi.

Previous page 1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button