UBAYD MALEEK COMPLETE HAUSA NOVEL

UBAYD MALEEK 46

Shigowar jekadi ne daukeda tray na silver me Dan girma daukeda dafaffiyar Nonon raqumi da wani ruwan madaran na musamman sai Dan breakfast Mara nauyi 

Sai wata kyakkyawar qaramar jaka dake hannunta na akayan NURUn dake ciki wainda ayau din akai odarsu aka kawosu 

Cikin girmamawa tace”

Allah ya qarawa maleek lafiya da walwala 

Barka da tashi.

Da Kai ya amsa Yana daukan wayarsa dake ringing ta sudada ta wuce cikin palonsa na gaba ta ajiye komai akan dining ta koma palondasu maleek din suke shima 

ta zuba Masa breakfast kadan yafara ci Mr Omar naci gaba da koro Masa bayanai.

Sai Sha biyu ta farka ta bude idanuwanta dasukai mugun nauyi fuskarta harta Dan kumbura kadan ta dafa ta tashi zaune tana sauke ajiyar zuciya ahankali 

tareda rufe ido ta bude tana zuro qafafunta qasa saidai abinda takeji batajin zata iya tashi tsaye.

Shiru tayi agurin zaune tana kokarin miqewa cikin dauriya taji anbude kofar dakin 

Bata buqatar dagowa sbd tasan shine yashigo 

Jin shiru yasata dagowa daidai isowarsa dab da ita ya rankwafo baice komaiba ya dauketa gaba daya

Tayi qasa da Kai tana rufe idanuwanta yakaita har cikin toilet ya kwantar cikin ruwan dumi ya kalleta tareda shafa gefen fuskarta ya matso da tashi fuskar 

yakai bakinsa kunnenta ahankali ya furta”

Sorry.

Zamewa tayi ta kallesa ya sake shafa fuskarta ya juya ya fice yabarta da mamakinsa Bata fito daga mamakinba sai ganin jekadi tayi cikin toilet din da sauri 

ta zame cikin ruwan tana shigarda jikinta ruwan tana rufe ido

Kenan shine yake cewa tayi hkr.

Cikin nutsuwa jekadi ta qaraso gurinta tana cewa”

Ni tamkar uwace karki ji komai magani kawai zanbaki wannan sirrinkine da mijinki Nima sbd baisan yazaiyi mikin bane kisamu kyakkyawar kulawa.

Ruwan zafi ta kunna ruwan da NURUn take ciki suka dauki zafi Sosai 

Ta bude wata babbar kwalba cikin kayan data shigo dasu ta zuba cikin ruwan take toilet din yadauki wani qamshi NURU kuwa tanajin ruwan na shigarta ta koina 

jikinta yafara Dan sakewa Yana Mata wani iri 

Jekadi taqara zuba Mata wani abun daban kafin ta dibi ruwan zafin ta zuba cikin wata roba tayi hade hadenta ta ajiye Mata tace”

 idan kingama wankan kiyi tsarki da wannan.

Juyawa tayi ta fice sbd tausayin NURUn takeji sbd alamun dasuka nuna tana cikin mawuyacin hali.

Wanka tayi sosai taji dadin jikinta tayi tsarki da ruwan da jekadin ta jiye Mata tun alokacin taji wani irin sauyi Sosai agurin ta Gama tafito ahankali 

daureda towel ta nufi gaban mirror dinsa ta shafa mansa tareda spray ta dauki kayan data gani an ajiye Mata Wanda da Alama jekadi takawo ta daga kayan tana 

kallo dukkaninsu Babu me nauyi duk na Shan iska ne 

Bata wani damuba sbd jirin datake gani ta saka wata doguwar qaramar riga Mara nauyi tayi drying gashinta daqyar ta ‘daure da sabon band fito palon tana 

tafiya ahankali jekadi dake tsaye dining tana jiranta tai Mata sannu tareda ja Mata kujera ta zauna tana gabatar Mata da abubuwan dazata fara Sha kafin 

komai.

Daqyar ta daure Tasha duka ko abincin Bata iya tsayawa taci ba Takoma daki ta kwanta 

Jekadi ta tattare kayan ta fice dasu

 tana fita Mr Omar ya sulale yabi bayanta Dan bawa maleek lokacin hutawa 

Ya miqe ya koma ciki Yana duba lokacin sallah da yayi.

##MAMUH#*_Mamuhgee 47_*

Bacci takeyi har lokacinda ya Shigo din,ya kalleta tareda sauke boyayyar ajiyar zuciya ya juya ya nufi toilet yayo alwala yazo ya fice batareda ya tada ita 

ba Dan baccin Yana Bata nutsuwa da damar yanayinda takeji.

Yana fita bada jimawaba ta farka ahankali ta tashi zaune itama tayo alwala tazo tayi sallar Takoma ta kwanta tanajin zazzabin datake ji na qara shigarta ta 

lumshe ido tana sake shigewa bargo idanuwanta a rufe.

Qarfe goma aka Isa da lailah airport acikin wata sirrantacciyar mota 

Lokacin afia tafi mintuna ashirin agurin tana jiran isowarsu Dan Haka tana ganinsu ta fiddo doguwar jallabiya da Dan qaramin mayafi da goggles datazowa da 

mum din Tata dashi ta nufi motarsu itama tata fuskar Bata bayyanataba yanda za’a gane itace ta bude motarsu ta shiga baya inda mum dinta ke zaune tana 

kakkama jikinta tayi wani duhu cikin kwana biyu ga wani irin tsamin dauda da wahala na tashi ajikinta

Cikin tsananin baqin cikin ganinta Haka da kaunar mahaifiyarta me qarfi afia ta rungumeta gabaki daya tana cewa”

Mum.

Zarewa Lailah tayi ta kurawa afia ido idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin baqin ciki da dumuwa tarema da tsoron halinda rayuwarta tashiga kokuma ma 

Wanda tariga tashiga,

Ahankali ta bude Bakinta dake rawa wani tsamin Baki ya feso yacika motar Amma afia ita Sam batama jisa sbd Babu abinda uwarta zata zama ta gujeta da rawar 

murya tana hawaye tace”

Afia,afia my baby,afia my little princess I’m sorry baby ki yafewa mum dinki Amma ki yarda Dani bantaba aikata kisa ba Kuma bazan taba aikatawaba…ban 

aikata ba…bazan taba iya aikatawaba…ban aikataba…banyiba…

Riqota afia keyi tana cewa”

Mum mum na yarda Baki aikataba 

Mum na yarda 

Na yarda mum”.ganin mum din takasa daina fadar Bata aikataba cikin firgici Kamar lokacin abin ke faruwa yasa afia rikicewa tana korarin kwantar Mata da 

hankali cikin kulawa hankalinta na neman tashi sbd ganin alamun kaman mum din har lokacin tana cikin shock saidai Kuma….

Imran ne cikin hali na damuwa daya shiga akan lailan tun lokacinda Mr Omar yayi Masa bayanin komai gameda Dan tabuwa da kan lailan yayi sbd Shiga hali na 

shock lafiya zata ringa komai Kamar yanda take sai dai idan ta tuno abindaya faru na kisan abin zai dawo Mata zata fara fizgewa tana fadar ba ita tayiba 

cikin tsananin tsoro da firgici,

Shi kansa bazaiso afia tasaniba sbd hankalinta zai tashi yakoma kan kula da neman lafiyar mum dinta bazata taba maida hankali kan karatuntaba Kuma Dan Haka 

shima ya shirya kula da al’amarin bazai Bari tasaniba yanzu sai tagama kammala karatunta tsaf yanama fatan zuwa lokacin lailan tasamu lafiya Dan Haka shima 

ya yanke shawaran komawa Vegas gabaki daya zai zauna da lailah Dan nema Mata lafiya ta dawo daidai ta gyara rayuwarta ta ingantata yanzu kan tunani da 

hanyar dazata bullar da ita sbd Lailah tamkar uwa ya dauketa Dan kuwa itace wadda tafi sonsa aduniya bayan iyayensa sbd itanema yake Paris baibi iyayensaba 

Koda tabar maleek dasu afia Basu rabu ba shida ita Kuma sbd itane yake tareda maleek Yana aiki a qarqashinsa farko sbd ya kula dasu farhat dasuka shaqu.

Ajiyar zuciya ya sauke ahankali tareda fitowa ya zagayo yashigo bayan ya zauna dayan gefen lailan suka sanyata tsakiyansu ya dago ya kalli afia data fara 

shiga firgici cikin kulawa da kwantar Mata da hankali yace”

Tana cikin damuwar abin daya faru sbd case na zargin kisa wani abune da bakowa ne zai iya daukaba

Dole zata shiga wannan halin musamman yanzu data fito Kuma taganta agabanki Dole zataji wannan damuwar da shauqin son sanar dake ba halinta bane.

Hawayene suka gangarowa afia ta rungumeta tana sakin siririn kukan tausayin mum dinta ta dago tana kallonta tace”

Mum Inshallah komai yariga ya wuce bazai sake dawowaba 

Ki yarda da wannan wata jarabawace Allah yayi Miki danki gyara Kuma Inshallah nasan kin gyara mum kimin alqawarin bazaki sake zuwa gizah ba sbd bakida 

abinda yarage Miki anan sai tarihi.

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button