SAMEEHA D

*_????SÂMÊĒHÂ????_*
*_(D)_*
Bayan sun kammala karya kumallo ne Sameer ya dubi Sameeha dake shirin miqewa tsaye yace,””Ya kamata muji Kiran da Momy take Mana kafin tasake aikowa koya kike gani,ni kam Samee kunya nakeji idan Na hada Ido da Momy,hmm zaki Dena ji ne ahankali da zaran kun Saba tunda zaman guri 1 ya hadaku ke Bari ma kiji ita ma kamar yanda Umma take agunki haka Momy take Babu wani banbanci tsakaninsu nasan yadda Momy ke sonki Dan Allah kema
sameeha kisota ki Mata biyayya Kamar yanda nake mata sannan kiyi haquri da duk abinda zai faru nasan wata rana dole asamu sa6ani pls ki jure Koda daga nine kin ji,cikin sanyin murya sameeha ta amsa da”insha Allahu zaka sameni ayanda kasani koma fiya da hakan Momy uwa ce agareni bazan so wani Abu ya ratsa atsakanin mu ba mara dadi da yardar Allah,,Allah ya amince nace ko zaki dan dagoni qafata tamin sanyi,harara Sameeha ta jefawa Sameer yayi murmushi ya miqe itama ta miqe,daki Sameeha ta koma akwatin kayanta ta bude inda ta jera hijabanta tazaro milk daga cikinsu ta saka har qasa suka jiro tare hannunta nacikin na Sameer din suna tafe suna ta6a hira har sukayi barin da Momy take.
Tsaye take a window tana Raba ido daga nesa ta hangesu ba komai yadauke mata hankali ba illah haduwar da hannayen su sukayi da junna duk Wanda yagansu yasan akwai tsantsar so da qauna hade da kulawa ta musamman da sauri ta kauda kanta gefe ta juya tayi hanyar da zata kaita fallon ta zuciyarta na ayyana mata abubuwa dayawa dake qoqarin fasa kwanyar kanta.
“”Oyoyo oyoyo diyata,Momy ta tafi da sauri ta ringumi Sameeha har kujera ta kaita ta zauna tanai mata oyoyo Sameeha taqi Zama akai tayi qas da kanta gabanta na faduwa sai raba ido take Wai ita kunya.
Cikin girmamawa suka gaisheta ta amsa asake tana Mai tambayar lafiyansu,kana ta dora da.
Alhamdulillah,naji dadin ganinku cikin farin ciki da annushuwa Ina fatan zaku kasance ahaka har abada,Momy ta dubi Sameer dake kallon ta,”am na manta ban sanar da Kai da wuri ba Zee na Nan tafe zata biyu jirgin yamma insha Allahu sai ku fara shirin tarbar ‘yar qanwar taku duk da nasan Diyata Bata santa ba sai dai labarinta abakin ka yanzu kuwa zata sonta tunda ta dawo Nan da Zama gaba daya “Amma shine sai yau za asanar Dani momy”Ni kaina sai jiya take sanar min wai yau zata biyo jirgin yamma kasanta da shiririta”Aiko ba inda zanje in Dakota ta hawu Moto ta dawo,ba’ayi haka ba Ni na Ari bakinta nace kayi haquri, Momy ki barni da ita kawai Jalolo yaje yadakota sai da aka gama bikin nawa zata dawo dama zamanta tayi achan dayafi mata,Ummm Diyata kisa Baki mana nasan ke kina magana zai huce,Dan mirmushi sameeha tasaki ta sake duqa kanta qasa alamar Jin kunya,au kema bazaki haquran ba kin taya mijinki fadan,Aa Momy ni na Isa,to maza bashi haquri Dan baza abar min Diya akan titi tana jiran Moto ba.
Dan Allah kayi haquri badan Ni ba.
Dariya sukayi gaba daya Jin furucin da Sameeha tayi Kamar wace zatayi kuka,Sameer ya dubi Sameeha.
Allah taci darajarki da ba inda zanje in dako ta Amma na haquri tunda kin saka baki.
Iyeee lalai Sameer yau naga Zamani mata tafi ‘yar uwa to na gode Diyata tunda ke kin fishi kirki yanzu dai ya kamata katashi kabamu waje akwai zantukan da zamu tattauna da ‘yata Dan ban son gulma.
Kai Momy yanzu Ni din ne baza azanta agabana ba har sai na tashi na baku waje lalai kam na Zama sorry agunki Dan kin samu wata sabuwa.
Yo ga sabo me zakayi da tsohu Kai Kan ka yakaji kalmar abakin ka ni da Diyata zan yi Kuma ‘yar uwa abokiyar shawara me zanyi da Kai ai chan daii na sake ‘ya,, Sameer ya miqe Yana mita daga Momy har sameeha dariya suke Masa,Momy ta dawo da dubanta ga Sameeha dake zaune akan kafet.
Sameeha.
Na’am momy,Sameeha ta amsa cikin girmamawa.
Abinda yasa nace kuzo Ina nemanku ba wani Abu bane ilah game da yanda zamu tsara ayukan gidan Nan tunda gaki Allah ya kawo ki Ina ganin Babu amfanin ajiye masu Mana girki da sauran ayukan daba’arasa ba na gida Ina fatan Zaki dage da kulawa akan tsarikanmu da duk sharadan Dana gindaya Miki dan na san ansaba a chan gida ko?.
Shiru Sameeha tayi Jin kalamar da Momy ke furtawa Kamar ba ita ke magana Mai sanyi yanzu ba,,,ganin batada damar yin magana yasa Momy taci gaba da.
Ina fatan Zaki kiyaye da duk abinda bana so,ki hanzarta yin abinda nake so sannan idan zakiyi Abu Ina son ayishi cikin tsafta da kulawa ban cika son surutu ba bana Kuma San Jaye Jaye na San dai kin gane abinda nake nufu sannan duk inda Zakije ki fara sanar Dani kafin ki sanar da Sameer haka ko Mai zakiyi ki nemi shawara a guna ko waye zai zo gunki ki sanar Dani da wuri kafin lokacin zuwan yayi ga Zee Nan dawowa Kar Inga Kar inji kin sa6a mata duk abinda tace tana so ayishi cikin sauri kafin naji wallahi 6acin ran Zee Kamar 6acin Rai na ne kina jina.
Gyada Kai kawai sameeha keyi Momy ta Dora…..
Kar Kuma kiga komai a banza adinga ibar mana Ana kaiwa gida komai alissafe yake idan za’adubo tsohuwa asanar Dani da wuri ko qanzo atara akai mata,ba Kuma na son gulma da munafunci duk abinda kika gani ko akai Miki shi a gidan nan kar ki sake ki kwashe ki gaya masu ko shi kansa Sameer wlhy mudin Zaki dinga haka to zamu Sami sa6ani bazaki ji dadin Zama Dani ba kwata kwata koshi Sameer dakike gani Bai Isa ya tsallake inda nasaka Masa karaba bare wata ke,darmmmmm gaban sameeha yasake faduwa akaro na biyu.
Idan kinji bayanina Kuma kin bi ruwanki in Kuma kin qi bi shima yarage inake ki tashi muje na nuna Miki babban kicin dinmu Wanda ashi Zaki dinga aiwatar da komai na griki muna da masu aike in kina buqatar wani Abu akwai kudi a loka duk zan nuna Miki su.
To,kawai sameeha ke fadi hade da girgiza Kai Momy ta miqe sameeha tabi bayanta jikinta duk ba qwari……….
Babban kicin din gidan Momy ta Kai sameeha duk wani Abu na amfanin girki Dana gida sai da ta nuna mata sannan ta qara da Bata umarnin tayi maza ta hadawa Zee kayan motsa Baki Wanda Baya lalata ciki,jikin ta na rawa ta amsa da to tafara kiciniyar abinda zata dafa,gas ta nufa ta tsaya tayi duru duru ta rasa me zata dauka duk a Kan idon Momy,cikin tsawa tace da ita.
Me Kuma Zaki dauka achan ko shima Baki iya kunnawa bane?.
Aa tukunya nake nema zan Dora abincin.
Ban nuna Miki lokar da suke ba.
Kin nuna min jikinta ya soma rawa.
Dallah wace ki ban waje ga inda na nuna Miki Set din su Mai ya Kai ki gun gas ko kunnawa zakiyi ki kashe mu.
Da sauri Sameeha ta toshe Baki tana girgiza kanta chan Kuma sai kuka, Momy ta zaro Ido hade da Sallati.
Na shiga uku ni Hauwa dukan ki nayi ko zagi.
Aa Momy.
Shine Zaki saka kuka daga magana,Ni wai me ma zakiyi da tukunyar.
Cikin kuka sameeha ta furta.
Abincin zan dafa.
Murmushin ta Kaici Momy tayi ta hade rai lokaci daya.
Ke…..
Na’am.
Ki tsaya ki nutsu da kyau ban son rawar Kai abin motsa Baki nace kiyi mata ba girki nasaka ki ba ko Baki sanshi bane.
Na sani.
Meye shi.
Farfesu ko kayan Snk.
Guda maza kiyi Mata farfesun kaza da Dan Snk mara nauyi idan kin kammala ki saman a fallo,ki Kuma rufan Baki idan sharri kika taka to Bari kiji gidan kika zo,,Momy tayi juyawarta tana taku 1-1.
Saida Sameeha taci kukunta ta qoshi tukuna tafara aiki tana tunanin yazatayi tun yanzu ta fara fuskantar matsala inaga gaba abin mamakin ma agaban Sameer ba haka Momy tayi ba……