Zee Baby Book 1 Page 30

Da misalin karfe biyar na yamma zee baby ce kwance a bedroom tana waya” wlh my dear Allah nayi miki fushi kinki zuwa kiga kayana ko waike kunya Hamm nagode”ayya my dear wlh nima umma ce ta hanani fita amma bari yanzu zanzo dan Allah karkiyi fushi ko har ankai kayan can gidanki? ” ba’akaisu ba kizo wlh nayi missing d’inki “ok zanzo yanzu wai angama dinka miki anko kuwa ni nasamu dinkuna na fah salma tace naki sunyi mugun kyau na dinner dariya zee tayi Dan Sam batason zancen tace”kibari zamuyi maganar idan kinzo?” OK bye ta tsinke Kiran dariya ta saki ta mike ta saka doguwar Riga ta saka hijab da niqab ta fesa turare ta fito tana jin jiri dan azumin bugata yakeyi gashi yau tin safe takejin ciwon kai ita daya zata rika zabura saboda mafarkin da tayi jiya wai kar tayi aure tanada auran sarkin Aljanan k’udis bushewa tayi da dariya “Allah mafarkin shirme baiyiba parlon babu kowa su ghaisha da ummi suna part d’in Daddah har hafeeza zaune tayi a parlo tana kollon TV Nisha ta shigo da sallama na Mike da gudu na nufi gunta muka rumgume juna najata muka nufi gun kujerun parlon muka zauna Niqab ta cire mun “wow haka kika zama dariya nayi na maids niqab din nace “kema kinyi kyau wlh tsaf dake amarya yayana dariya tayi” ina ghaisha ne? ” suna gun Daddah muje kiga kayan kafin suzo zaki kwana ne? ” A,A Yayamu idan yazo zai maidani wani iri zee taji ta kalli Nisha “wlh kibar bari kuna kebewa dashi kibari zansa my heart ya kaiki ba aso amarya da ango suna haduwa “Allah my dear “wlh my dear Karki sake yarda Sardauna ya ganki sai an daura muku aure shigowa yayi da sallama karaf akunnesa abinda zee take fadama Nisha idanu ya zaro Nisha ta sada kanta kusa da ita ya zauna fuskarsa babu wasa ya kamo hannuta yace” Humairah waye ya baki izinin fitowa kin fadamun ne? kika fito ya fada yana murza hannuta cikin wani Dan iskan salo Nisha ta rikice ta dago ta kalleshi wani irin kallo ya watsa mata Wanda taji kibiyar sonsa ta soketa kanta ta sada “Kayi hakuri yaya my dear ce tayi kewata shine nazo mu gaisa zee, baby Allah kadai yasan halin da tashiga ganin abinda Sardauna yakema Nisha kokowa ta shiga da numfashinta har ta daure ta dake ranta ta Mike dan so take ta janye Nisha daga gunsa ta kamo hannu Nisha” My dear tashi muje muyi abinda ya kawoki zata tashi Sardauna yace”babu inda zata tashi mutafi na maidaki gida amaryata Nisha jikinta ya Saki bazata iya masa musuba ya Mike ya kama hannun Nisha yana gyara mata mayafinta zee baby jirine ya debeta amma haka ta daure ta danne haushin Sardauna ta Kalli Nisha “my dear Ngd yau kin nunamun matsayina kin zabi mijinki Akan yar uwarki fuskarta ta bude tana murmushi tana kallonsu nagode Nisha kije bakomai wlh banji haushinki ba ta fada tana murmushi ta nufi hanyar bedroom dafe da kanta da yake Sara mata Nisha fashewa tayi da kuka “Yayamu Dan Allah kabari naganta kartayi fushi dani wani shegen murmushi ya sakar mata yaja hannuta suka nufi kofa wani. irin gigitaccen ihu zee baby ta Saki sai da parlon ya amsa sai gata timmm ta zube ak’asa tana karkarwa kumfa na zuba bakinta ai baisan lokaci da yasaki hannun Nisha ba yayi kanta da gudu yana kiranta” Zainab…. menene ya sameki dai de lokacin su ghaisha suka shigo da ummi hankalinsu atashe sukabi bayan Sardauna da gudu Nisha Ma kuka ta Saki me ciwo ta bisu da gudu……….✍????
[ad_2]