Zee Baby Book 1 Page 39

shakoshi na fadashi da duka banza na masa naci gaba da kukana harda shasheka wata uwara tsawa ya bugamun wacce ta tsoratani mutika” wlh zainab idan baki tashi ba zanyi mugun sab’amiki tashi kifice ko naci ubanki jikina ya dauki rawa na Mike tsaye nayi kansa jikinsa na fada na rumgumesa gam ina wani irin kuka”Yayana don Allah kadena mun tsawa haka abun yamun yawa ni bansan ma meke damu naba. tunda aka raba auranmu da Ya mahbeer da safe banida nutsuwa shine wai Nisha wai take tamun zancan kuna soyayya yo ni ina ruwana Yayana kacewa su Daddy su maidamun aurena zan zauna nima inason baby irin na Nisha wani mugun haushinta yaji da kishi ya tokareshi ya ingijeta zata bigi bango yayi saurin tarota Dan bazai iya barinta ta fadi ba saman kirjinshi ta fada makaleshi tayi ashagwabe tace” Yayana da naji ciwo fa kaidan kanada matarka shine zaka zalumci kanwarka ta fashe masa da kuka tana dukansa akirjinsa gabaki daya Sardauna baima san abinda yake masa dadiba tunda yaji zee baby a cikin jikinsa nutsuwarsa ta kwace masa azababben sonta da tsantsar kaunarta ya taso masa muryata ya tsinto tanacewa”Yaya Sardauna muje kasa amaidani gidana zan zauna kaji janyeta yayi jikinsa ya hankadata ta fadi ya fice yabar gun tashi tayi da gudu ta biyosa tasha gabansa tana rusar kuka idanunsa ya rumtse zuciyarsa na bugawa da karfi Dan ciwo take masa bakin cikinsa zee ta auri waninsa har an ketata tazama saura bakin cikinsa na biyu sakin da aka mata anmayar masa da ita bazawara gashi babu aure tsakaninsu kuma ko akwaima saide ya mutu da sonta bazai taba aurantaba kuma sauran wani jinsa yake kamar yabar duniyar saboda bakin cikin daurewa kawai yakeyi gashi bayason kukan zee gashi ta tisasa gaba tana masa kuka
idanunsa ya bude ya kamo hannuta gudun kar wani ya gansu lungun suka koma ya tsayar da ita ya tataro mata gashinta da yarufe mata fuska ya daure mata hawaye sai kwaranyo mata yake saman fuskarta fuskar ya riko ya goge mata hawaye da hannunsa ya ruko hannayenta duka biyu” zainab idan kinaso Nasaka amaida muku auranku to kiyi shiru ki hadiye kukanki ko nayi mugun sabamiki hadiye kukan nayi na dago muka hada idanu kaina na Sada saboda bazan iya kallon wannan idanunsa masu mugun dafi ashagwabe nace”Ya Sardauna na daina kukan kayi hakuri tarine ya sark’e Sardauna ya Saki hannuwan zee yana dafe da kirjinsa yana tari ya sunkuya arikice zee ta sunkuyo ta rikeshi”Yayana menene mura kakeyi sanu ta fada tana bubbuga bayansa ganin yaki dainawa ta rumgumeshi ta fashe da kuka”Yayana menene Dan Allah kabari kaji kalli yada jikinka yake karkarwa kuwa ta fada tana riko kansa ta kora masa idanu yada yake tarin kansa ta tallabo ta shafi fuskarsa
mai kewaye da kwantaccen saja” Yaya Sardauna kabari ta fada tana kifa fuskarta saman tashi tana kuka ganin bazai bar tarin ba bata tsaya komaiba ta had’e bakinsa yana mata tarin kokarin janyeta yakeyi yana girgiza mata kai gashi yanaso yatsayar da tarin Abun ya faskara zee idanunta sharkaf da hawaye ta lalubo harshen Sardauna tana tsotsa cikin nutsuwa cikin ikon Allah tana fara tsotsa tarin ya tsaya
idanu ya zuba mata yada take tsotsar bakinsa tana hawaye wani mugun kishine ya tokare masa zuciya bakinsa ya zare yana huci ya hankadeta ta fadi k’asa fashe masa tayi da kuka”Yayana duk ka canza mun bansa me nayima ba please kabarni nasha sweet yawunka wata biyu ban shaba Dan Allah karka hanani yayana ta fada tana ririkeshi tana kuka”Ya Allah wai ni wace irin masifa ce take tunkaroni zee kibarni na huta karki kasheni please yi shiru hakan babu kyau kiyi hakuri za’a maida muku auranku bari kukan ya fada yana janyeta daga jikinsa shagwabe masa tayi cikin shashekar kuka tace” Yayana to muyi kiss ni inaso nasha yawunka kaji ta fada tana Kara shigewa jikinsa tana kukan sangarta”Yaya Sardauna kabani yawunka kar na mutu wlh mutuwa zanyi ta fada tana ririkeshi tana masa wani irin kuka mata tab’a zuciya tana kiran sunansa Yayana Sardauna Numfashinta ya fara sama da k’asa jikinta ya fara Saki ta fara wata irin karkarwa idanunta na lumshewa arikice ya mannata jikinsa yana girgizata” zainab ke meye haka wai ya kikeso nayi da raina cikin fitar Haiyaci tace” Yayana Sardauna abubuwa sunmun yawa gashi ka kimun abunda zan samu nutsuwa ga bakin cikin abinda matarka ta fadamun ya tsaya azuciyata Yayana zan mutu gwarama na mutu na huta da bakin cikin duniya ta fada tana tari tun karfi jikinta na rawa”Yayana danne min kirjina ciwo yakemun ta fada tana wani mugun tari wata wawar rumguma ya mata yana ririketa yana buga bayanta cikin tsawa yace “inji ubanwa zaki mutu saboda ni kiyi hakuri karki kamu da irin ciwona kuma bazaki mutuba inko hakane wallahi saide mu mutu tare………………..✍????
[ad_2]