NAJEEB 45

Bayan sun isa Gida ibtisam tana ganin ya faka motar ta fita tayi cikin Gida da ledan wayar daya siya mata, koda ta shiga ciki babu kowa a falon d’akinsu ta tafi Kai tsaye inda ta iske Zarah zauna tana danna waya, ajiye ledan wayar
tayi akan gadon d’akin
Zarah d’auka tayi tana bud’ewa lokaci d’aya tace wow latest iPhone, waya baki??
Ibtisam tace wa kike tunani zai bani
Dariya zarah tayi tare da fad’in your darling hubby
Ibtisam Hararanta tayi tare da fad’in kyaji dashi dai
Zarah tashi tayi tare da saka wayar a caji tana fad’in, ni kam so nake inga camera din wayar nan, da suka saka har guda uku, bari yayi caji in gani
Ibtisam tace uhm aiki ja
Najeeb ganin ta fita yasa ya girgiza Kai tare da fitowa shima yayi cikin gidan inda yayi d’akinshi direct
Ibtisam bayan sun fito yin dinner inda Mum take tambayanta gidan yayi
Tace eh mum cikin jin kunya
Dad yace ina najeeb din yake ma??
Mum tace yana d’akinsa Nasan
Dad bayan ya gama cin abinci tashi yayi yana fad’in yau a gajiye yake, kai tsaye bedroom yayi domin yana bukatar ya kwanta ya huta
Mum tashi tayi itama tabi bayan mijinta inda ya rage daga Zarah sai ibtisam Ahmad ya koma skul
Zarah sai faman d’aukan hoto take da wayan ibtisam din, ita kam ibtisam abinci take ci abunta
Najeeb ne ya fito inda yazo ya zauna a kujeran dake kallon na ibtisam
Zarah tace bros shine ni baka siyo min wayar ba, nima in fito gari ba
Kallon ibtisam yayi wacce akai Sa’a itama shi take kallo gira ya d’aga Mata alaman Yadai
Da sauri ta juyar da kanta tare da ajiye spoon din abincin da takeci
Najeeb ganin haka yasa yayi murmushi, lokaci d’aya kuma ya kalli Zarah tare da fad’in, wace waya kike ri’kewa??
Tace Bros iPhone 7 cefa
Yace ok saiki bari in munje saudiya in siyan miki
Tace Bros plz kaban kud’in gobe muje mu siya mana..
Yace ke dawa zaki goben??..
Tace ni da ibtisam, ta k’arasa maganan cikin dariya
Najeeb yace ashe ba zaki ba, ni daga yanzu babu inda zata dinga zuwa
Kallon ibtisam yayi da take sauraransu yace plz yunwa nakeji bani abinci Inci
Ibtisam kallonshi tayi cikin ranta tace Wlh wannan ya iya abu, kalla yanda yake wani abu kaman irin mun saba dinnan, tashi tayi tare da d’aukan plate ta zuba Mai sannan ta kai mishi gabanshi ta ajiye
Gaba tayi zata wuce yace heey come back Ina zaki??
Ibtisam tsayawa tayi cak, ta kasa magana bata ma san mai zata ce mishi ba
Janyo mata hannu yayi tare da janyota ta fad’o ya ri’keta tayi jikinsa….. Ganin haka zarah yasa ta tashi tabar wajan tana murmushi cikin ranta tana fad’in sai aukin fad’in basa son juna…..
Ibtisam data tsorata domin sai taga kaman zata fad’i ta lumshe ido da sauri, jin bata fad’i ba yasa ta bud’e ido wanda suka sauka akan na najeeb, gaba d’aya kallon idon juna suke…..
Sunyi wajan minti biyu a haka ibtisam ta rufe ido domin bazata iya juran kallon idon nashi ba, dan wani abu takeji tun daga kafarta har tsakiyar kanta
Najeeb ganin haka yasa ya kura ma fuskanta ido yana kallonta, lokaci d’aya ya d’agota tare da tashi daga kan kujeran ya mi’ke tsaye, hannunshi yasa a kugunta ya ri’ke mata su, lokaci d’aya ya janyota ya matseta da jikinsa, yana son kamshin jikinta, gaba d’aya najeeb wani irin mugun sha’awa yakeji sosai, ido ya lumshe yana shafa mata baya
Ibtisam kam gaba d’aya gabanta sai faman dukan uku uku yake, ga zuciyarta dake faman bugawa da karfi fat fat
Sun d’auki lokaci a haka Kafin ta Fara k’okarin ta kwaci jikinta…… A hankali yace don’t move…..
Kaman ya danna remote haka ta tsaya ta daina kokarin fita daga jikin nasa
Sakinta yayi tare da juyata ta baya ya kama kugunta ya matse tare da fad’in did you miss me???
Ibtisam data juya Mai baya taji tambayar tashi tazo Mata a bazata, tare kuma dajin mamakin tambayar tashi da yayi mata…..
Katse mata tunani yayi da fad’in answer me? Did you miss me?? Tunda na tafi kin taba tunani na koda sau d’aya??
Ibtisam hannunta tasa a nashi Tana k’okarin cirewa daga kugunta da yasa nashi
Ganin tana son cire Mai hannu yasa ya k’ara matseta Sosai a jikinsa tare da fad’in idan kina tare dani ki daina k’okarin cewa zaki kwata kanki, domin….. Juyo da ita yayi yanda zai dinga kallon fuskanta ganin haka yasa ta rufe ido da sauri
Murmushi yayi tare da hura Mata iska akan fuskanta, K’ara matse idonta tayi
Ganin haka yasa yaci gaba da fad’in ko da yaushe Indai kika bari na ri’keki kaman haka, just surrender ur self….
Bud’e ido tayi a hankali ya sauka akan nashi inda shima ya kura mata ido, a hankali ta Fara zame jikinta Lokaci d’aya taja da karfi tayi baya……
Dariya tayi wanda bata san tayi ba, sannan tace gashi na kwaci kaina….. Tana fad’in haka tayi gaba da sauri
Najeeb kam idonshi na kanta harta bace yana murmushi ganin ta bace yasa ya lumshe ido tare da K’ara sakin wani murmushin
Zama yayi amma yau najeeb ya kasa cin abinci domin gaba d’aya ji yayi bazai iya ci ba, dan sai yaji ya gundureshi, dan gajeran tsaki yayi tare da tashi yayi d’akinsa inda yayi toilet yayi wanka sannan yazo ya kwanta…..
Ibtisam kam bayan ta shiga dak’i Zarah tace har an Gama soyewa?
Ibtisam tace uhm Kedai kika sani
Zarah tace a’a kudai kuka sani keda bros, gaba d’aya ku dukanku babu komai a idonku sai Son junanku…..
Ibtisam dariya ta saki tare da fad’in ki daina wannan maganan, na tabbata abunda yasa kika ga najeeb na haka saboda abunda Granny tace ne, hawaye ne ya zubo mata a ido tare da fad’in nima inayi ne saboda ita, Allah sarki Granny Allah yaji k’anki inama kina Raye
Zarah tayi dan murmushi tare da fad’in rayuwa kenan, Allah yasa mu cika da imani
Ibtisam ta amsa da Ameen
Zarah tace Wlh Ina tuna irin abubuwan da akayi da Granny, abun ban dariya koda yaushe burinta taga kowa cikin farin ciki, kai duniya kenan, gashi yanzu bata cikin ta
Ibtisam hawaye ya silalo mata tare da fad’in Wlh kuwa, koda yaushe da tunaninta nake kwana nake tashi, yanda naji mutuwar Granny banji ko Ummi ce ta rasu zanji irin yanda naji, Wlh nafi shakuwa da Granny akan ummi data haifeni
Zarah tace hakane, Nima Nasan haka, yanzu abu d’aya za kiyi ki nuna kina son Granny dagaske…..
Ibtisam ta katse zarah da fad’in Mai kenan??
Zarah tace Kibi magananta na karshe, ki kama mijinki hannu bibbiyu, wlh Granny na matukar son ku tare, ki duba shine magananta na karshe, ibtisam wannan shine za kiyi ki tabbatar kina Sonta dagaske
Ibtisam kuka mai sauti tasa tare da fad’in Zarah Wlh Ina k’okarin yin hakan amma daga naga najeeb abunda ya aikata wanda har yau na kasa fad’ama kowa shike dawo min ciwo cikin rai, na kasa mantawa….
Zarah tace ibtisam kiyi hakuri, Nima bance ki fad’amin ba, ina so kiyi hakuri, ki cire komai a ranki, kiba mijinki second chance, wlh najeeb ya canza sosai, ki mishi uzuri ki d’auka komai yayi miki a baya rashin sani ne, yanzu Alhmdlh ibtisam najeeb ya fara karatun addini, idan kika lura ya canza ba kaman da ba, ko ta yanda yake magana dasu Mum zaki fahimci hakan yanzu….. Shuru Zarah tayi na wani lokaci sannan taci gaba da fad’in “ibtisam Wlh najeeb yana sonki, koda bai furta miki ba ni naga sonki a cikin idonsa…..
2gnovel
4medicals
Smidris
Ibtisam tace zarah kenan Wlh najeeb baya so na, kawai yana zama danine badan so ba, kaman yanda nima bana sonshi…..
Zarah murmushi tayi tare da fad’in aiko k’arya kikeyi, domin kaman yanda najeeb ke sonki haka kema kike son sa, ibtisam Wlh kina son najeeb amma zan iya cewa baki gane cewa kina son shiba, domin har yanzu kina d’auka son kabir shine a ranki, which kin dad’e da daina son kabir ko ince da ba so kikayi ba, duba da yanda kabir shine kika fara soyayya dashi amma baki aureshi ba….. Na tabbata Idan kika zauna kikai nazari ki tuna da Idan kinga KABIR ya kikeji?? Sannan Idan kinga najeeb ya kikeji?? A nan ne zaki gane wa kike so…..
Ibtisam wani kukan tasa Tana fad’in Zarah ban sani ba, nidai abunda na sani shine bana jin kabir kaman da, kwata kwata yanzu bana tunaninsa har sai najeeb yayi min wani abu da naji haushi, sai in tuna dashi …..
Zarah tace kinga alaman so na Farko kenan, karki manta kince sai najeeb yayi miki Abu kike tunawa da kabir, kenan in najeeb bai baki haushi ba bazaki tuna dashi ba?? Ibtisam son najeeb ya kamaki amma kin kasa fahimta, nidai shawarata shine ki ri’ke mijinki hannu bibbiyu ki manta da komai, ki d’auka kaman ba’ayi ba
Ibtisam shuru tayi tana nazarin maganan zarah Wanda ita da kanta tasan gaskiya ne, ido ta lumshe tana tunanin maganan Granny da sukai baya akan tayi hakuri da mijinta, domin in kince zaki kashe auren baki San wanda zaki aura ba….. Da sauri ta bud’e ido tana hawaye, tabbas hakane Allah ka bani ikon yimai biyayya
Tashi tayi Kai tsaye tayi toilet wanka tayi ta fito d’aure da towel, kayanta ta bud’e ta d’auko rigan bacci tasa ta kwanta
Gaba d’aya suna shirin tafiya saudiya, Mum tana ta gyara ibtisam Sosai
Ibtisam da zarah na zaune a bukka suna firan skul, ibtisam tace ni bani number din kubra bani da number din kowa a waya na yanzu
Zarah tace bani da number d’inta sai dai in tambayi aysha ta turomin
Tsaki ibtisam tayi tare da fad’in batta Dan Allah ni banson hulda dasu balle har ki tambayeta Abu
Dariya Zarah tayi tare da fad’in akan wani dalili?? Maita miki??
Ibtisam tace hakanan kawai ni haushi take bani
Zarah tace kodan tana son najeeb ne??
Ibtisam tace ina ruwa na taita sonshi mana, nidai kawai bana sonta batai min ba kawai naji bana son hulda da ita ne
Zarah tace kawar taki?? Kawai kice yanda take kuzanta mijinki ne bakya so.
Ibtisam tace koma dai Mai nene ke kika sani, tare da fad’in mubar maganan plz
Zarah dariya ta saki tare da fad’in najeeb Dai ya gama da zuciyarki
Kafin ibtisam tayi magana suka ji muryan najeeb na fad’in naji Ana kiran sunana….
Idonshi nakan ibtisam dake kwance a k’asa kanta Nakan tum tum
Da sauri ta tashi tare da zama
Zarah tace yauwa bros zo kaji wani abu
Ibtisam hararan Zarah tayi alaman tayi shuru
Zarah ganin haka yasa ta kwashe da dariya, najeeb zama yayi kusa da ibtisam a k’asa tare da kallon zarah yace inaji
Zarah ta kuma sakin dariya tare da fusge wayar dake hannun ibtisam ta Fara d’aukansu hoto tana fad’in Kai nice couple, najeeb d’aura hannunshi yayi akan kafad’an ibtisam tare da janyota kusa dashi Sosai…..
Da sauri ta kalleshi ido daya ya kashe mata tare da fad’in camera zaki kalla not me
Da sauri ta juyar da kanta tare dajin wani irin kunya sosai
Zarah tace smile ibtisam
Ibtisam hararan Zarah tayi
Shi kam najeeb sai wani manneta yake a jikinsa
Najeeb ya kalli Zarah tare da fad’in muga pic din
Mi’ka Mai wayar tayi najeeb yace wow tare da nuna ma ibtisam yace wa yafi kyau??
Kallonshi tayi alaman ban sani ba…..
Yace bani zaki kalla ba, d phone
Ido ta lumshe tare da k’okarin tashi
Janyota yayi ta zauna akan kafarshi yana fad’in Ina zaki
Zarah tashi tayi tare da barin wajan tana fad’in naga in Abun ya tashi basa tuna akwai mutane a wajan, nima Allah ya bani Wanda nake so
Ibtisam k’okarin tashi take amma Najeeb ya ri’keta dakyau, tare da fad’in na fad’a miki indai kika zo inda nake harna ri’keki just surrender kawai domin bazaki iya escaping ba
Ibtisam jin dagaske bazata iya kwatan kanta ba yasa ta nutsu, matso ta yayi Sosai ya k’ara manneta a jikinshi, lokaci d’aya yasa hannunshi ya cire mata k’aramin hijab din dake jikinta, gaba d’aya gashin kanta ya bayyana wanda yake a tsefe
D’agota yayi suka mi’ke tsaye yasa ido ya kura mata yana kallonta, ita kam kanta na k’asa domin bazata iya kallonsa ba, wani irin Abu takeji Idan ta kalli idonshi
Lokaci d’aya ya janyota jikinshi tare da d’aura hannunshi akan west d’inta tare da manna kanshi akan fuskanta, ibtisam idonta a lumshe yake gaba d’aya hancinsu a had’e yake suna shak’an numfashin juna
Dukansu biyun wani irin yanayi suka shiga wanda ko wannansu bazai iya misaltashi ba, lokaci d’aya ya saka bakinshi cikin Nata ya fara kissing d’inta tare da tsotsan k’asan lips d’inta yana saki tare da kamo harshenta…..
Gaba d’aya ibtisam jikinta ya mutu ji tayi ta kasa ri’ke kafarta, tana k’okarin tayi k’asa ta fad’i….. Da sauri ya ri’keta tare da saka hannunshi biyu ta bayanta ya ri’keta dakyau tsam a jikinsa yana kissing d’inta
Yayi wajan 8 minute yana haka, Kafin ya barta yana kallonta
Ibtisam idonta a lumshe yake…..
Najeeb ya kira sunanta da ibtisam…..
A hankali ta bud’e ido tana kallonsa ganin yana kallonta yasa ta kuma rufe ido,
Ganin haka yasa yayi murmushi tare da fad’in I miss your lips alot…..
Jin abunda yace yasa ta bud’e idonta da sauri Tana kallonsa
Hancinta yaja yana fad’in Did you miss me???
Kawar da kanta gefe tayi
Ya saka hannunshi ya juyo Mata da kanta yace answer me??
A hankali tace ina son in shiga ciki….
Murmushi yayi tare da fad’in mijinki na nan Mai zakiyi a ciki?? Am hare in front of you…..
Ido ya kuma k’ura mata wani irin Abu yake ji gashi yana matukar bukata, domin a matse yake Sosai dan an dad’e ba’a had’u ba……
Ibtisam k’okarin jan jikinta tayi ya kuma matsota jikinsa tare da fad’in fad’amin kinyi kewa na???..
Kai ta girgiza mishi alaman a’ah
Dan sakinta yayi kad’an tare dayin murmushi yace OH, why will I ask?? Ido ya lumshe tare da cije lips d’inshi lokaci d’aya ya bud’e ido wanda ya saukeshi akan fuskanta da idonta ke rufe
Lokaci d’aya yace just open ur eyes I need to talk to you…..
Ibtisam kasa bud’e ido tayi domin bazata iya ba, dan tasan yana kallonta
Jijjigata yayi tare da fad’in open ur eyes plz
A hankali ta Fara bud’e idonta Wanda yake a lumshe gaba d’aya idonta akan nashi ya sauka Wanda take k’okarin ta kawar da kanta yace plz just stay and watch my eyes
Ibtisam tace plz leave me Bazan iyaba
Sakinta yayi aiko tana ganin haka tai k’okarin ta gudu ya ru’ko Mata hannu wanda yasa dole ta tsaya cak ba tare data k’ara matsawa ba…..
Amma ta baya take ta juya mai baya hannunta yana ri’ke da nashi
Ya fara magana da fad’in ko zamu tafi gidanmu yau
Ibtisam shuru tayi bata bashi amsa ba amma gaba d’aya gabanta fad’i yake Sosai
Janyota yayi tayi baya ya k’ara matseta amma ta baya duka suna kallon gaba, yace you say you don’t miss me right??..
Shuru tayi kirjinta yana bugawa Sosai gaba d’aya jikinta wani iri taji yayi mata
Najeeb yace ni nayi missing d’inki Sosai…..
Jin Kalman bakinshi yasa gaba d’aya jikinta yayi sanyi tare dajin wani iri a jikinta
Yaci gaba da fad’in I know you never love me, Nasan kin fada kince bazaki taba sona ba, but Ina son just for granny ki forgetting komai , and don’t forget d promise that we make for her b4 she die……
Ibtisam kuka ta saki sosai domin tabbas abunda ya fad’a hakane Granny ta tafi kuma ta barsu hannunsu a ri’ke tabar duniya Tana fatan su zauna tare har abada
Najeeb jin kukanta yake har cikin ranshi gaba d’aya baya son jinta Tana kuka, ko ganinta cikin damuwa
A hankali ya janyota tare da juyota ta gaba ya kura mata ido ganin yanda take kuka Sosai abun tausayi
Hannunshi yasa ya fara goge mata hawayen idonta amma yana gogewa Tana yin wani
Yace plz ibtisam stop it bana son kukanki gaba d’aya bana son ganinki…… Sai kuma yayi shuru ba tare daya k’arasa abunda yake son fad’a ba
Cikin kuka tace a kullum Ina tuna wannan alkawarin da mukai ma Granny, ina son inyi yanda take Fata duk da Nasan ni dakai bama son juna, I wish in samu wanda yake so na nake…..
Da sauri ya toshe mata baki tare da fad’in just keep quiet…..
Ibtisam who told you…… Sai kuma yayi shuru tare da lumshe ido yama rasa mai zaice mata, lokaci d’aya kuma ya bud’e idon nashi tare da k’ura mata ido yana kallon fuskanta da take ta faman kuka kaman an mata wani abu
Yace ibtisam just stop this crying plz bana son jin wannan kukan plz ki bari gaba d’aya kina sawa inji wani iri plz for god sake kiyi shuru….
Lokaci d’aya tasa hannunta ta Fara share hawayen idonta idonshi na kanta yana kallonta……
Lokaci d’aya ya janyota jikinshi tare da matseta sosai yana sauke wani irin nishi mai cike da so da k’auna, yanda yayi mata rungumar kaman ance wanine zai kwace mishi ita a hankali yace ibtisam I love you……….
(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9740, ‘t’: ‘300 by 250’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());