KWARATA 24

Muna fita gidan biki Baba ƙarami ya ɗauki wayarshi ya fara kiran Babana abin alfahari na , mai nunamin soyayya ta zahiri da gaskiya , wayayyan mahaifi mai tafiya da rayuwarshi daidai da zamani…
Bayan Babana ya ɗauka suka gaisa , bayan gaisuwa Babana yayi masa ya taro tare da addu’ar Allah ya bada zaman lafiya wa ma’auranta , Baba ƙarami yace ameen ,
Bayan Babana ya gama addu’a Baba ƙarami yayi gyaran murya tare da cewa wato Aliyu ɗiyarka dai ta zama cikakkiyar karuwa , ka shige ka ɓoye kabarma dangi baƙin ciki su gani…
(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9704, ‘t’: ‘160 by 600’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());
Rabbi annee massaniyadh dhurru wa anta arhamur rahmeena , Abdullahi Uwar masu gida baza ta taɓa zama karuwa ba ban haifi karuwa ba akanta amma karuwai suna zuwa kuma zasu tabbata akan duk wanda yake dangana min ɗiya da siffar karuwanci , ban gudu ba kuma ban ɓuya ba tunda har kuna nema na ku sameni ku bugo kuma in ɗauka muyi magana , na ƙauracewa zaman ne saboda duk duniya babu hawaye mafi ɓakin ciki inga suna gudana tsakanin idanuwa zuwa saman kumatu irin na Uwar masu gida,
Duk kuwa ranar da naga kukanta tou tabbas shekarar mutuwa tane ya tsaya , ɗiya ɗaya tak a cikin taron yuyuyun “yan uwa , saita tallafeni sai ta tallafe ka sai ta taimakeni sai ta taimake ka sai ta taimakesu sai tayi ma kowa taimako kuma ko bana raye wallahi ka riƙe wannan maganar karka sake ka manta ta uwar masu gida cikakkiyar mai arziƙi ce ,
Idan ina da rabo inci idan banda rabo dangi su amfana ko ƙasa ta rufemin ido nasan nabar baya mai amfani , burin duk uba yabar baya jaruma ba lusara ba , idan kalmar karuwan ta sake fitowa bakinka akan Uwar masu gida na rantse da girman Allah gaba ɗaya zuri’ar ka sai sun zama karuwai…..
Zufa ta ketowa Baba ƙarami tare da cewa Allah ya baka haƙuri Aliyu ban faɗi wannan maganar dan in ɓata maka zuciya ba , jarumin uba kenan murmushin “yan duniya yayi Babana tare da cewa nima ban faɗa maka dan zuciyarka ta ɓaci ba ina tunatar da kai dai ko waye Aliyu Binna dan naga tafiyana yasa ka manta me binna ɗin take nufi, haƙuri dai Baba ƙarami yaci gaba da bawa Babana saida ya tabbatar daya sauka sannan sukayi sallama…
Wata irin ƙuna mai kartar zuciya Babana yaji wacce tasashi zaman dole , saida yasha kuka harya godewa Allah sannan yace ki yafemin Uwar masu gida ƙaddara tayi makauniyar waiwaya , an cuceni anci amanata banso ƙaddarar rayuwarki tazo miki a haka ba , amma na rantse da Allah daga Dikko har yaronshi Alhaji sun shiga uwatar bala’e duk wadda yaci yaciwo ma kanshi masifa ,
Abinda Bello ya guda kenan shi yasa shi baiba , amma yakaiki inda akayi nayiwa Dikko uzuri kuma na yafe mishi saboda nayi imani da yasan waye ubanki ko a santa ya ganki tsirara baya kallonki bare har yayi sha’awarki , duk abinda kike ciki na sani kuma ina da labarinshi , daga Dikko da Alhaji babu namijin da zai sake keta miki mutunci har abadan duniya , idan tsafin ne ba’a fini iyawa ba , cikakken ɗan caca manemin matan aure za’a nunawa iya sihiri ? Gaki nan zakiyi yawonki tare da rayuwarki cikin “yan ci kamar yadda ko wace ɗiya mai gata zata yi amma wallahi babu namijin da zai sake kwanciya dake sai mijinki na sunna in Allah yadda…
Murmushi kasan dai Dikko yafi ƙarfinka duk wani ɗan ƙaramin tsafinka baya tasiri akanshi, kaine kaɗai halakakke ɓatacce wadda baka dogara da Allah ba ka dogara da tsafe tsafe, duk wanda ya riƙe Allah kuma ya dogara dashi Allah zai isar mishi duniya da lahira….
Dariya nayi adaidai wannan lokaci na daki sitiyarin mota ta domin fira mukeyi tunda muka taho , kallon Amisty nayi tare da cewa yaufa nasan na daki zuciyar maƙiya , mutumin dana burge a wurin bansan iyaka ba , tou dole ince mana ,
Kinga Sultana ga mota Sultana ga wayewa ga iskanci uwa uba karuwancin nan yamin kyau domin yasa na zama wata babbar hajiya da mutane ke ganin girmana , kuma nayi musu hauka da kuɗi zaki ga ikon Allah makwaɗaita sai sun biyoni saboda wannan zamani mai badawa shi ake mannemawa,
Haka dai rayuwarmu taci gaba da tafiya ! Kullum iskanci na da lalacewa na gaba yakeyi amma har zuwa wannan lokaci ban samu wani cikakken namiji kwatankwacin Dikko ba , mijin Zalifa kuma har yanzu baizo ba da nayi masa magana bai zo ba saidai ya toshe ni da kuɗi tun abun baya damuna har ya fara tsaremin rai…
Tsaye da kyau zaune da kyau babu inda Allah ya rageni amma mazan bariki idan sunzo basu tayani saidai idan nayi kawalci in samu kuɗi abunfa ya fara damuna na rasa inda zan saka raina dan ba irin wannan sana’ar na zaɓa ba gaskiya nafi so a nemeni ayi kuma a bani kuɗi ,
Amisty ta lura da halin da nake ciki ta tambaye ni abinda ke damuna , ban wani ɓoye mata ba na sanar da ita , dariya Amisty tayi tare da cewa wallahi hannu aka saka miki ,
Cikin rashin fahimta nace ina aka saka min hannun ? Na tambayeta ina kallon jiki na ! Dariya Amisty tayi sosai sannan tace haba uwar ɗakina bafa a jiki ake saka hannu ba , abinda ake nufi da sa hannu magauta zasu je wurin malaman tsubbu su biya kuɗi suce a toshe musu samunki a rufe duk wani ci gaba naki….
Tsoki nayi tare da cewa aisai suje suyi ta fama can su Allah ya azamawa , Amisty tace tou ai sai anyi maganin matsalar sannan zamu barsu suyi ta fama , kallon Amisty nayi tare da cewa wallahi kun cika canfe² babu wani jarabta na rayuwa sai asiri , an saka miki hannu , tou idan sun gaji da sa hannun zasu goge da kansu ,
Daga ƙofar ɗaki Nana tayi magana cewa Mother zamu ɗan shiga maƙota , daga inda nake zaune nace me akeyi maƙotan ne ? Nana tace Mother baƙi ne suka bayyana a cikin daren jiya anguwar nan , kinga matar wayayya ? Daga tsakar gida Saude tace matar kodai mijin ? Zamu shiga muga halinsu idan munga da lasa zamu yankawa mijin kati zai dawo gidan nan uwar ɗakinmu…
Murmushi nayi irin namu na “yan duniya sannan nace tou ku dawo lafiya , saboda ni dama Allah baimin shige² ba ina nan inda Allah ya ajiyeni duk wadda nake tare dashi shine yake zuwa ya sameni dan gaskiya bana san raini shi yasa na tsare mutunci na a gidana…
Gyaran murya Nana tayi tare da cewa ko zakije ne ? Cike da izza nace ku dawo lafiya , Amisty tace nima kam zanje , murmushi nayi amma ban sake magana ba , gaba ɗaya suka ɗinguma suka tafi gidan amma ni banbisu ba….
Gaba ɗayansu a palon matar suka sauka , kowa ta kama kujera ta haye kamar baƙon namiji a harkar mata , bayan gaisuwa kowa ta faɗawa matar sunanta tare da cewa sune maƙotan gidanta , itama sunanta ta faɗa musu Asma’u sannan ta kora da cewa bata taɓa aihuwa ba ,
Gyara zama Amisty tayi tare da cewa shekararku nawa da aure ne ? Asma’u tace gaskiya munkai shekara 8 , tou kina da abiyar zama ne ? Amisty ta tambayeta , Asma’u tace Eh mu biyu ne ? A ` i ta anshe da cewa tou kun taɓa neman maganin aihuwa ko itama abiyar zaman taki bata taɓa aihuwa bane ba ?
Asma’u tace kai tana haihu sosai ma , Amisty tace tou matsalar daga wurinki take idan mun fahimta , Asma’u tace gaskiya , daga haka dai suka tsaya domin sun shiryo barikinsu wa Asma’u zance yau iyakarshi haka….
Miƙewa sukayi gaba ɗayansu cewa zasu tafi , Asma’u tace haba tun yanzu ? Murmushin “yan duniya A ` i tayi tare da lumshe idanuwa ita mayyar mata tace ai zamu sake shigowa , rakiya tayo musu har bakin get tayi godiya sosai ,
Tunda suka fito faɗa ya kaure tsakaninsu , yayin da A ` i ke cewa ta kama matar Saude kuma ta kama mijin , Amisty tace A ` i dani zaki haɗa hanya ? Bayan ni na fara isar da saƙo na zakice kin kamata ? Nana tace kai matar fa tana da mazauna sosai gaskiya , rikici dai sukeyi sosai , dan haka Amisty ta taka musu birki da cewa duk abinda zasuyi suyi shi a waje kar su bari naji wannan labarin domin sun san babu abinda na tsana irin harkar mace da mace….
Tun a waje sukayi ma Hafsa waya suka sanar da ita sun samu lafiyayyar mace kuma daga gani zatayi shan mai domin yarinyar da zafinta , Hafsa tace gani nan zuwa , Amisty tace karki zo yanzu kina zuwa uwar ɗakinmu zata gano wani abu kinsanta da saurin fahimta , duk satin nan karki zo ki bari sai cikin sati na gaba , Hafsa tace wallahi bazan iya ba sai nazo na ganta ,
Amisty tace saurara kiji yarinya , ba’a garaje ya kike abu kamar baƙuwar harka don Allah ? Ki natsu ki kwantar da hankali wallahi babu mai yarinyar nan sai mu , ki dai bari mu ɗorata hanya ita da kanta zata riƙa kawo kanta , dakal Amisty ta lallashi Hafsa ta haƙura,
Tsakar gida suka sameni kowa tayi dabur ² murmushi nayi tare dabin Amisty da kallo sannan na kalli idon A ` i na kalli na Nana saboda sune “yan lesbian a cikinsu , da kinga sunayin kame² mace suka gani , sai kuma Hafsa itama manemiyar mata ce , jinjina kaina nayi sannan na tsare Amisty da kallo idanuwanta sunyi wani irin ja kamar taci tsidagu,
Ƙafafuwan Amisty na kalla sannan na ɗago idona zuwa daidai saitin cibiyarta sannan na dauke kaina , ɗaki ta wuce Nana ma ɗakinta ta shiga yayin da A ` i ta samu wuri ta zauna , kallon inda A ` i take zaune nayi sannan nace sannun ku kwarata daga zuwa maƙota har hankalinmu ya tashi ko ? Duk yadda akayi matar gidan ta burgeku , Allah ya tsallaketa daga kaidinku….
Ɗaki na shiga Amisty na samu kwance saman katifa tayi ruf da ciki , tsoki nayi tare da halbinta da ƙafa nace tashi ki fitarmin daga ɗaki ni gaskiya bana san irin wannan ɗabi’ar ,
Allah ya baki haƙuri uwar ɗakina , tana faɗin haka ta miƙe tabar ɗakin ta nufi ɗakin Nana , da yake itama Nana naga yanzu taɗan waye tana wanka tana shafa turare , har akayi sallah magrib Nana da Amisty da A ` i suna ɗakin bansan abinda sukeyi ba gaskiya….
Kuma ban damu da sanin halin da suke ciki ba danni Allah baimin sa ido da bin diddiƙin abinda wane yakeyi ba , sai bayan isha’i Amisty ta shigo da ɗaurin gaba da alama wanka tayo ,
Ko inda take ban kalla ba , itama bata kalleni ba kuma batamin magana ba taci gaba da shiri saida ta gama abinda takeyi tsaf sannan tace min dame² za’a siyo ne ?
Can zaki kwana ne ? Na tambayeta , tace ba’a can zan kwana ba wurin 1:00 zan dawo , indomie da madara kawai zaki ƙaro mana , kallona tayi sannan tace ke babu abinda kike so ne ? Ba abinda nake so na bata amsa tare da cewa Allah ya bada sa’a a dawo lafiya , da amin ta amsa sannan ta fice daga ɗakin…
Kwanciya nayi bayan Amisty ta fita dan banda inda zanje , Nana ta shigo ɗakin da sallama ta ɗauki magunguna ta fita saboda mu yanzu garin “yan gidanmu ya waye ,
Ganin Nana ta ɗauki magunguna na tashi na feshe jikina da turaruka masu ƙamshi na ɗaukar hankali , doguwar riga ta shadda na saka nayi ɗaurin ɗan kwali irin namu na karuwai dan banda daurin ɗan kwalin daya wuce ture kaga tsiya…
Tunda na fito daga ɗaki su Karima suka rufamin baya dan ko gyale tuni na daina sakawa , cikin isa da nuna ni wata shegiya , cike da izza nayi gaba sai baƙin rai nake na tun kari ƙofar gida su Nana duk suna biye dani , tsayuwa nayi a ƙofar gida nabi motocin dake ajiye a ƙofar gidan da kallo kamar anayin wani taro.
Murmushi nayi yayin da aka ajiyemin kujerar roba na zauna , ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora sannan mazan bariki suka fara kawo gaisuwa kamar yadda suka saba a duk lokacin da wani zai ɗauki wata domin nice uwar ɗakinsu , suna bani girmana basu rainani ba shi yasa duk wani kwarto yake ganin girma na…
Duk namijin da yake zuwa wurin matan waje babu samari manyan mutane ne masuji da kansu wani ma wallahi yayi ɗiya da wacce zai kwanta da ita , ko me yasa suke baro matansu na gida suzo na bariki ? Gaskiya ina san insan wannan dalili …
Bayan na gama samun kuɗina na miƙe na koma ciki ,ɗakina na shige nabar musu filin tsakar gidan dansu ji daɗin harkokinsu , mace ɗaya tana iya kwanciya da namiji biyar saboda tsabar haɗama ,
* *
Safiyar yau gidan Asma’u su Amisty suka sauka , acan suke baje kolinsu ranar da suka fara zuwa banje ba kuma yauma da zasu koma banbi su ba , gaba ɗayansu suka tafi ni kuma na fita ƙofar gida nayi zamana a saman dakali…
Wayata na ciro na fara kiran mijin Zalifa , bayan ya ɗauka yace ina gida idan na fito zan kiraki , jinjina kai nayi tare da cewa ka fito lafiya ranka ya daɗe ina faɗin haka na kashe wayata….
A gidan Asma’u kuwa ga yadda lamarinsu ya kasance a yau ,