
Julde cikin nutsuwa da kuma 茩arancin kuzari taci gaba da jefa 茩afafuwanta,
A haka ta isa dab da ga蓳ar kogin, cikin rashin fahimtar inda take sanya 茩afafuwansa ta 蓷aga 茩afarta damanta da niyya ci gaba da tafiya,
Babu zato bare tsammani taji.
DAN ALLAH DAN ANNABI KIJI TSORAN KADA KI KARANTA MIN LITTAFI BA TARE DA KIN SIYA BA, 08119237616
An sanya 茩afa tare dayin ball da ita gaba 蓷aya tayi baya zata fa蓷i ya sanya 蓷aya hannunsa ya daga tsaye ya ri茩o gaban rigarta, wahalalliyar ajjiyar zuciya ta sauke tana mai zare manyan Idanunta,
Ta gaba sanya ran cewa taje 茩asa, 茩uri tayiwa wani waje hakan ya sanya Abu Maleek yin tsaki tare da sakinta gaba 蓷aya ta fa蓷a saman,
Ji茩a茩茩en yashin dake wajan, gani yake kamar tana sani take zare masa ido, a fili kuma ya lumshe idanunsa tare da fa蓷in.
“Kamar wani tafi ido”
Ya fa蓷a yana mai 蓷aukan babban kifi tare da yin gaba Sweet ma kifi 蓷aya ta 蓷auka ta biyo bayansa.
Dafe kai Julde tayi abinka da kai babu gashi, Idanunta ne ya cika da hawaye sosai taji zafin fa蓷uwar da tayi ko kuma tace ya yar da ita,
Baki ta murgu蓷a a fili tace.
“Wayyoooo kai na”
Ta fa蓷a tana runtse idanunta, ganin zaman sam ba zai mata ba ya sanya ta mi茩e tare yin alwala duk ba wani iyawa tayi ba,
Sallah tayi kana ta zauna a wajan tana mai jin yunwa ga kuma ciwon da 茩irjinta yake mata.
Bayan yayi kyasto, ya ha蓷a dotsen wuta da wani a saman 蓷an busassun itacen daya samu, nan da nan wuta ta tashi,
Fa蓷a蓷a fuskarsa yayi da Murmushi yana bala’in son tsuntsaye da kuma irin wannan halittun, kifin daya suke a cikin wani 茩aton sanda ya 蓷auko,
Kana ya 蓷ura saman wutar ya fara gasawa,
Almost 20minutes kafin kifin ya gasu sai tiriri yake yayi jajir dashi, gashi 茩ato mai tsuka da yawa,
A saman wani 茩aton ganye ya ajjiye kifin kana ya fara ci cikin nutsuwa, sweet ma baki ta sanya ta fara yagar wanda ya sanya mata,
Sai da yaci sosai yabar raguwa kafin yaje yasha ruwa,
Gyara tsaiwa yayi tare da 蓷aukan sweet ya fara duban hanyar da zaibi domin ya isa cikin Rugar Mahinjo a yau 蓷in nan,
Motsin da yaji a bayansa ya sanya ya juya da sauri ganin Julde tsaye fuskarta cike da hawaye,
Ya sanya ya 蓷auke idanunsa da sauri yana mai ta蓳e bakinsa,
Julde kowa 茩ara banza hanci tayi saboda 茩amshin data ji ya sanya cikin siririyar muryarta tace.
“Zanci kifi, zaka sammin ko?”
Zare ido yayi yana mamakin yadda take iya fahimtar wani abun Kamar ba Makauniya ba, tsaki yaja yana Lumshe idanunsa kafin a ransa yace.
“Witch”
Ya fa蓷a a taushashe cike kuma da gajiya, ganyen ya 蓷auka ta cilla mata saman 茩irjinta, da sauri ta 蓷auka tana sauke numfashi da kuma Murmushin jin da蓷i,
Zama tayi tare da tan茩washe 茩afafuwanta, ta fara yagar tsukar kifin tana kaiwa 蓷an 茩aramin bakinta,
Janye idanunsa daga kan guntun bakin nata, wata dabara ce ta fa蓷o masa, a hankali yayi baya yana mai shafa 茩irjinsa magana yake sunyi amma sam ya gaji da surutun wannan mai bakin akun,
Yana lumshe idanunsa tare da motsa bakinsa da 茩yar yace.
“Heyyy blind ina ne Mahinjo!!!?”
Ya fa蓷a yana mai 蓷an 蓷aga Murya tare da lumshe idanunsa,
Ambaton sunan Mahinjo da yayi ne ya sanya ta tsaya da cin kifin Jikinta ya 蓷an 蓷auki rawa,
Sai kuma a lokacin ta tuna da shanun da aka bata kiwo,
Cikin sauri ta mi茩e tana jujjuya Idanunta kafin a hankali ta sulale 茩asa cikin Muryar kuka kuma tace.
“Na buni, dan Allah ba kaga shanuwa ba? Wayyoooo Madibbo shikenan zasu kashe ni an kwashe masu shanu”
Da mamaki yake binta da kallo ko kalma guda na maganarta bai fahimta ba,
Tsaki Yana cikin 蓷aga murya ha蓷i da tsayawa ya koma Abu Maleek 蓷insa wanda yake na asali bawai yanzu da aka sanya ya zama mahaukaci ba yace.
“Noi inde wuroman?” (Ya sunan garin ku).
Ya fa蓷a in a serious tone.
Cikin firgici ta tarin tsoro tace “Rugar Mahinjo”
苼oyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke yana mai 蓷an jin da蓷i dan ko babu komai sai ta rama masa taimakon da yayi mata cikin ha蓷e fuska kamar tana kallonsa yace.
“Let’s go”
Ya fa蓷a yana yin gaba, dafe 茩irji tayi tana sakin kuka kafin tace.
“Dan Allah ka barni a nan wallahi kashe ni Ar蓷o zaiyi”
Ha蓷e fuska ya 茩arayi saboda yarinyar ta fara bashi ciwon kai, haushi da kuma takaicin tsayawa inda take ma yake,
Gyara tsaiwa yay kafin cikin kakai murya yace.
“Su kashe ki mana, ni dai ba ruwana saikin raima min abinda nayi maki dan kiji”
Kuka ta sanya masa shi kam ko a jikinsa juyawa yayi ya 蓷auki sweet kana kamar mai ra蓷a yace.
“Muje”
Bata ta蓳a tunanin bashi da kirki ba sai yanzu, da alama shima daga rugar yake saboda taji yayi fulatanci,
Kanta ta sunkuyar 茩asa kafin tace “bani da sanda ai, bazan iya tafiya ba”
Ta 茩are maganar Idanunta na zubar da hawaye,
Ba tare daya kalleta ba domin shi ya 茩osama yabar inda mayatacciyar yarinyar take, wata igiya ya 蓷auka tare da cilla mata yana 蓷an yatsuna fuskarsa yace.
“Tied your hand”
Sharrr hawaye ya 茩ara sakko mata ta 蓷aure hannu kuma? Dabba ce ita da zata 蓷aure hannayenta, ganin tana 蓳ata masa Lokaci ne yasa ya 蓷an 茩ara daka mata tsayawa wanda shima da kansa sai daya dafe kansa sabida tsorata da tsawar da yayi,
Da sauri ta ri茩e igiyar duk Jikinta rawa yake kana ta na蓷a a hannunta idanunta na zubar da waye,
Shima yayi hakan ne sabida bai tsayawa kusa da ita bare har ya yi tunanin ri茩e mata hannu,
Tana gama 蓷aura igiyar ne shi kuma ya ri茩e bakin igiyar tare da fara tafiya da sauri yana janta da sabida igiyar dake 蓷aure a hannunta.
A haka suka fara tafiya domine isa Rugar Mahinjo.
A can cikin rugar kowa Ar蓷o ne da Barkido sai kuma Lami蓷o zaune, suna tattaunawa gyara zama Lami蓷o yayi kafin Yace.
“Na aikata da mutane a sirrince domin su duba min abinda ke faruwa a sakamakonsa harbin da mukaji, sai dai abin mamaki gaba 蓷aya Shanuwanmu suna nan amma an nemi Julde an rasa”
Da sauri Barkido ya kalli Lami蓷o tare da fa蓷in.
“Kamarya an nemeta an rasa? Kana nufin ba’a ganta ba ko mene? Tayaya za’a ga Nagge amma ba’a ga mutum ba”
Kallon Barkido ar蓷o yayi sabida ya gama fahimtar 蓷an nasa cewa ya fa蓷a tafkin soyayyar Julde, shi kam rashin Julden ba 茩aramin da蓷i yayi masa ba,
Rashin nata kuma ya 茩ara tabbatar masa da cewa Tabbas burinsa zai cika koma yace ya cika, dan matsalar sa 蓷aya Madibbo do ya gama da Yakumbo ya gama da Madibbo mai uwa a gindin murhun ma ya gana da shafin ta,
Gyaran murya yayi ka蓷an kafin ya kai dubansa ga Barkido yace.
“Meye damuwarka? Mene tsakaninka da ita, daman ai burinmu ace yau babu ita, domin idan har tana raye Tabbas burinmu bazai ta蓳a cika ba, kafi kowa sanin yadda muka sha wahala kafin mu kawo iya zo, dan haka ina garga蓷inka idan ma wani abu zuciyarka take kissima ta daina, Aradon Allah ina ci maka mutunci”
Ar蓷o ya fa蓷a yana nuna Barkido da hannunsa, kafin kuma ya fuskanci Lami蓷o yace.
“Wane mahaukacin daya Shigo cikin jejin?”
Lami蓷o ya kalli Ar蓷o kana yace “Barkido babu waje”
Tashi yayi zuciyarsa cike fal da tarin ba茩in ciki, tattaunawa sukai kafin ko ya tashi ya nufi makwancinsa sabida dare yayi, gari yayi tsitt.
Ganin duhu yayi sosai ya sanya Julde zamewa a hankali ta kwanta tana sauke numfashin wahala,
Shi kansa Abu Maleek ya gaji tunda suka taho babu abinda yake tsayar da su sai sallah, gashi dare yayi duhu ba zai sanya suci gaba da tafiya ba,
Bisa Dole shima ya nemi waje ya kwanta yana sauke ajjiyar zuciya tare da rufe idanunsa,
Julde numfashi ta 茩ara ja da 茩yar tana ri茩e da saitin zuciyarta dake wani irin harbawa sabida tsananin ciwon da 茩irjinta yake,
Cikin fidda sauti da kuma da kuma tarin wahala da kuma ciwon dake 茩irjinta ta cije bakinta, tana murje 茩irjinta dake mata wani iri zafi da ra蓷a蓷i,
Zame idanunsa yayi daga kanta yana jan tsaki a ransa yake fa蓷in.
“Guntuwar Yarinya sai 茩aton nono mtwss!!!”
Ya fa蓷a yana mai kwanciya a saman wata ciyawa dake ji茩e da ruwa.