Allon Sihiri Book 4HAUSA NOVEL

Allon Sihiri Book 4

Al’amarin
daya kara bashi mamaki kenan,kuma yaji ya
kamu
da tsananin sonta fiye da koyaushe.Cikin
kankanin
lokaci ta gama shirya masa dukkan kayansa
sannan
suka yi bankwana ya saba jakarsa a kafadarsa
bayan
yayi shigar bad-da-kama irin ta fatake sannan ya
koma can kofar gidan sarautar.A wannan lokaco
tuni
Sarki Sailur ya gama shirya komai,domin a samu
cikakken shiri dangane da wannan tafiya Tasu
Ruhaisu saida aka sauya masu gadin kafor gidan
sarautar gaba daya a cikin daren aka zuba
wadanda
ya tabbatar da cewa masoyansa ne na gani
kasheni,kuma ya gargadesu akan cewa duk
abinda
suka gani ko sukaji a wannan dare su barshi a
cikin
zukatansu kada su kuskura su sanar da wani.D
isowar Barde Ruhaisu bakin kofar gidan sarautar
sai
ya iske sarki Sailur tsaye a gaban wadansu
dakaru
guda dari suna bisa kan dawakai dauke da hajoji
da
makaman yaki alamar cewa su fatake ne.Tun
daga
nesa Barde Ruhaisu ya fara nazarin fuskokin
wadannan dakaru,koda ya shaidasu sai ya kamu
da
tsananin farinciki da mamaki.Ba komai ne ya
haddasa hakan ba face ganin cewa gaba daya
sa’anninsa ne kuma manyan abokansa wadanda
ya
aminta dasu a cikin dakarun yakin kasar.Koda
sarki
Sailur ya hango tahowar Barde Ruhaisu sai ya
tafi
gareshi cikin murna yace,yakai dana an gama
shirin
komai dama kai kadai ake jira saboda haka sai
kayi
haramar tafiya.Koda jin haka sai Ruhaisu ya
kama
hannayen sarki guda biyu ya sumbacesu kawai
sai
ya sake rungume junansu suka dan jima a
kankame
da juna.Al’amarin daya karya zukatan sauran
dakarin
kenan suka kamu da tausayinsu saboda sunsan
irin
shakuwar dake tsakaninsu.Nandai Barde Ruhaisu
da
Sarki Sailur suka rabu bisa dole sunayin kwallah
badon suna so ba,aka kawowa Barde Ruhaisu
wani
farin INGARMAN DOKI wanda ya fita dabam da
dukkan dawakan abokan nasa ya kama ya
hau.Take
ya kada linzamin dokinsa ya fice daga cikin
gidan
sarautar ba tare daya yarda ya sake waigowa
ba.Ai
kuwa sai sauran dakarun guda dari suka rufa
masa
baya da sauri shi kuwa sarki Sailur sai ya bisu da
kallo kawai,bai bar wajen ba har saida suka kule
ya
zamana cewa ko kurarsu baya iya
hangowa,sannan
ya juya ya koma izuwa cikin gidan sarautar yana
mai
zubar da hawaye.
¤¤¤ ¤¤¤ ¤¤¤
A CAN BIRNIN Sarki Alkasu kuwa tun da aka
gama
wannan gasa ta neman Auren YAZARINA
tsakanin
YARIMA LUBAINU da YARIMA MANGUL suka
dawo
gida sai sarki Alkas ya sanya hijabi tsakaninsa da
Yarima Mangul.Suna dawowa gida yayi masa
korar
kare daga fada kuma ya gaya masa cewa idan ya
sake sa kafarsa a cikin harabar gidan sarautarsa
zai
yanke masa hukuncin daurin rai da rai a gidan
kurkuku.Koda jin wannan batu sai mamaki da
bakin
ciki ya turnuke Yarima Mangul ya dubi dungulmin
hannunsa a lokacin da hawaye yake zubo masa
sannan ya dubi Sarki Alkas yace saboda mezaka
kyamaceni alokacin dana fi bukatarka?Ka dubi
yadda
na zamo musaki ka tuna cewa nine fa kadai
danka
guda wanda zai gaji karagarka?Ka tuno da irin
tsananin son daka keyi min saboda me yau zaka
bari zuciyarka ta rinjayi soyayyar danka?Kafin
Yarima Mangul ya gama rufe bakinsa tuni sarki
Alkas ya daka masa tsawa a lokacin da shima
hawaye ya zubo masa ya dubeshi yace,karka
sake
kirana da matsayin ubanka domin tuni nasaka
TAKOBI na datse wannan
alaka dake tsakaninmu kamar yadda ka datse
wacce
ke tsakanina da Abokaina kuma manyan
masoyana
sarki Sailur da Attajiri Abu Yazarina.Ka sani cewa
ka
jefa wadannan masoya nawa a cikin bakin cikin
da
har abada babu abinda zai gusar dashi tunda ka
rana Yarima Lubainu da lafiyarsa ka sanya masa
cutar da bata da magani kuma a sanadiyyar
hakan
yayi rabuwar doke da masoyiyar tasa rabuwar da
ba
lallai bane su sake saduwa ba.Kaga keknan ka
raba
iyaye da ‘ya’yansu kuma ka raba MASOYA.Ka
sain
cewa a yau idan na rasaka a gobe daya daga
cikin
matana zata iya sake haifa mini wani dan,amma
aminaina daka rabamu dasu bazan taba samu
kamarsu ba.Yarima ka cuceni cutar da har abada
ba
zan iya yafe maka ba.Koda jin wannan batu sai
Yarima Mangul ya zube kasa a gaban sarki Alkas
ya
fashe da kuka kuma ya kama tuba yana rokon
gafara.Maimakon sarki Alkas yaji tausayinsa sai
ya
dubi wadansu dakarunsa su shida dake tsaye a
gefe
daya yace dasu su kama Yarima Mangul su fitar
dashi daga cikin gidan sarautar kuma a kulle
kofar
gidan.Nan take kuwa dakarun suka kama Yarima
Mangul Suka fitar dashi daga cikin gidan
Sarautar da
karfin tsiya yana kuka da ihu gami da turjewa
kuma
yana kwallawa sarki Alkas kira mma sarki Alkas
ko
waigowa baiyi ba bare ya dubesi ya tausaya
masa.Ana fitowa da Yarima Mangul daga cikin
gidan
sarautar sai akayi wurgi dashi a wulakance
tamkar
bai kasance dan sarki ba,aka janyo kofar gidan
sarautar aka kulleta bam,aka zuba mata
sakatu.Cikin
tsananin bakin ciki da takaici Yarima Mangul ya
mike tsaye yana kuma.Nan taje yaji ya tsani
sarki
Alkas yadda ya tsani mutuwarsa.Kawai sai ya
takarkare ya bushe da dariyar mugunta iska ta
dauki
sautin dariyarsa takai har izuwa kunnen sarki
Alkas
gami da muryarsa yana mai cewa yakai Abbana
ka
saurari ranar da zan dawo gidan nan nine zan
zama
sanadin AJALINKA kuma saina hau kan
KARAGARKA.Koda jin wannan batu sai bakin ciki
ya
turnuke sarki Alkas zuciyarsa ta kama
tafarfasa.Har
ya zare takobinsa da nufin ya juya da baya da
gudu
yaje ya kashe Yarima Mangul sai zuciyarsa ta
daka
masa tsawa tace dashi so kake kabarwa kanka
abin
gori a wannan masarauta?Ka kyale Yarima da
Halinsa ai duniya makarantace zata koya masa
darasi.Daga wannan rana Yarima Mangul ya bar
cikin birninsu gaba daya ya koma daji da zama
saboda bakin ciki.A sanadinyyar haka ne ya hada
kai da ‘yan TAWAYE gami da ‘YAN FASHI suka
fara
shirye shiryen yadda zasu kawar da mulkin sarki
Alkas ya dane KARAGAR MULKINSA,amma
kullum
idan ya dubi iya yawansu da iyakar makaman
dasuka tanada sai takaici ya kamashi saboda
yasan
cewa ko kasa daya cikin kaso goma na shirin
sarki
Alkas basu kai ba don haka dole ne ya cigaba da
hakurin jiran lokaci.A haka dai Yarima Mangul ya
cigaba da jagorantar wannan runduna ta yan
fashi da
tawaye suka rinka kai harin SUMAME izuwa
kauyukan dake sauran kasashen ketare suna
kwaso
mata,dukiya da kudi suna kamo bayi da karfin
tsiya
suna basu horon yaki domin kara yawan
dakarunsu
kuma suna siyan mugayen makaman yaki suna
tarasu.Ana cikin wannan hali ne wata rana
Yarima
Mangul na zaune a cikin sansaninsu yana shan
giya
ga mata a gabansa suna ta fama tika rawa anayi
musu kida saiga wani DAN LEKEN ASIRINSA ya
rugo
da gudu bisa kan doki.Da isowarsa kusa da
Yarima
Mangul sai ya tsaida dokinsa ya sauko kasa ya
fadi
a gaban Yarima Mangul yace ya shugabana ga
wani
AYARI can na BAKIN FATAKE kimanin su dari da
doriya dauke da HAJAH mai tarin yawan gaske
sun
nufi hanyar dazata kaisu Birnin SARAUNIYA
AKISATUL SAUWARA.Koda jin wannan batu sai
Yarima Mangul yayi jifa da kwalbar giyar dake
hannunsa ya mike tsaye zumbur cikin tsananin
farin
ciki yace,tabbas yau zamuyi babbar farauta mai
inganci.Maza a kawo mini dokina da kayan
yakina.Dakaru dubu daya kacal nakeson suyi min
rakiya.Nan take kuwa cikin gaggawa aka kawowa
Yarima Mangul kayan yakinsa ya sanya sannan
ya
hau dokinsa ya zabureshi da gudu dakaru dubu
suka rufa masa baya.”Ashe wannan AYARI na
fatake
ba wasu bane face su Barde Ruhaisu wadanda
suka
fito neman Yarima Lubainu a cikin shiga ta bad-
da-
kama domin a sada Yazarina da Mijinta Yarima
Lubainu.
kuyi hakuri yau Ansamu delay din post hakan
yafarune sbd bansamu time bahALLON SIHIRI
Littafi na Hudu (4)
Part E
TUNDA WANNAN Ayari nasu Barde Ruhaisu suka
baro birnin Zamrul sukayi ta ratsa
dazuzzuka,kauyaka da kananan Birane basu
fuskanci
matsalar komai ba har tsawon kwana tara.Kuma
a
duk tsawon wadannnan kwanaki Barde Ruhaisu
bai
taba yarda ya gusa ba daga kusa da Yazarina ba
wacce koyaushe fukskarta a rufe take cikin
mayafi
idanunta kadai ake gani,kuma shigar datayi
mutum
bazai iya gane cewa ba macece ko namiji.Ko
dare
ne yayi har tayi bacci Barde Ruhaisu yana tsaye
a
kusa da ita kuma ya saka Dakaru sun kewaye
yankin
wajen da take.Kai ko wani kyakkyawan motsi
yaji a
kusa da wajen da suke sai ya duba ya tabbatar
da
cewar babu abu wanda zai kawo mata
barazana.A
tsawon wadannan kwanaki da suka shafe suna
tafiya
ko sannu babu wanda ya yiwa wania tsakanin
Barde
Ruhaisu da Yazarina ma’ana basuyi magana da
junansu ba.A ranar kwana na taran ne da
yammaci
sakaliya suka yada zango a bakin wata korama
domin su dan huta kuma dawakansu su sha
ruwa.Bayan an tsaya kowa ya sauka daga kan
Dokinsa,dakaru sun kewaye wajen don tabbatar
da
tsaro,Yazarina ta zauna a gefe daya ta bude
jakar
guzurinta ta dauko nama yana ci,shi kuma barde
Ruhaisu yana tsaye a bayanta ya zare takobinsa
yana wasata akan dutse sai kawai suka jiyo
sukuwar
dawakaia daga yamma,gabas,kudu da
Arewa.Sannan
kuma sai suka jiyo kururuwar mazaje mai ban
tsoro
amma saboda su Ruhaisu sun kasance ZARATAN
JARUMAI masu dakakkiyar zuciya ko gezau
basuyi
ba,kawai sai sukayi sauri suka zaro wadansu
manyan garkuwoyi daga kan dawakansu saboda
tsoron kada a fara kawo musu hari da harbin
kibiya.Take kowannen badakare yacake
garkuwarsa
a gabansa sannan ya zare takobinsa,kowa ya
tsaya
a inda yake ba tare da wata razana ba.Yazarina
ce
kadai ta firgita a lokacin data hango wadansu
dakarun sumame su da yawa sun durfafosu a
guje
bisa dawakai rike da makamai tsirara suna ihu da
kururuwa.Har ta yunkura zata mike tsaye a
dimauce
sai Barde Ruhaisu yayi wuf ya kamo hannunta ya
zaunar da ita kasa.A karon farko ya dubeta
yace,ki
gafarceni ya shugabata idan kika matsa daga
nan
koda taku daya ne halaka zakiyi.Abinda nakeso
dake
shine komai RINTSI DA TSANANI kada ki gusa
daga
kusa dani,koda kuwa kinga an karar da dukkan
dakaruna saura ni kadai jal na rage a raye!Lallai
ki
kiyaye wannan umarni dana baki muuddin kina
son
ki sake saduwa da masoyinki dan’uwana Yarima
Lubainu.Koda Yazarina taji wannan batu sai ta
gyada
kai tana nuna masa alamun cewa lallai zata
kiyaye
wannan umarni nasa.Koda jin haka sai Ruhaisu
yai
sauri ya rufe fuskarsa da rawani suma sauan
dakarun nasa sai sukayi koyi dashi.Abinda ya
daurewa Ruhaisu kai shine har dakarun sumamen
suka iso daf dasu ya zamana cewa tazarar dake
tsakaninsu bata wuce taku ashirin ba amma basu
harbo musu kibiyoyi ba.Da isowar dakarun
sumamen sai sukayiwa su Ruhaisu KAWANYA
suka
yi cirko cirko bisa dawakansu.A sannan ne
shugaban dakarun sumamen wanda dashi da
dukkan yaran nasa sun rufe fuskokinsu sai ya
sauko
daga kan dokin sa ya karewa fataken kallo
tsaf,sannan ya bushe da dariyar mugunta,lokaci
guda kuma ya turbune fuskarsa ya dubesu
yace,ni
da yarana mu dubu daya ne da daya,ku kuwa
bakufi
ku dari ba,abin kunya ne mu yakeku ta hanyar
farar
harbo muku kibiyoyi.To waishin kuma menene
amfanin rufe fuskokinmu damu daku mukayi?Ai
kawai kowa ya bude fuskarsa muyi GABA DA
GABA
fada da buya ai tsoro ne.Koda gama fadin hakan
sai
shugaban dakarun sumamen ya kwaye rawanin
dake
kan fuskarsa su Barde Ruhaisu sukayi arba
dashi.Ba
wani bane face Yarima Mangul dan sarki Alkas!!!
Hannunsa na dama na rike da zabgegiyar
takobi,ya
saki daya dungumin hannun nasa.Koda Barde
Ruhaisu yayi arba da Yarima Mangul sai shida
dukkan dakarunsa suka kamu da tsananin
mamaki
gami da tsananin tsoro.Koda ganin haka sai
barde
Ruhaisu ya kwaye fuskarsa shima ya mike ya
matso
gaba kadan ya dubi Yarima Mangul yace,sau tari
Jarumi yakan rufe fuskarsa saboda wata
BABBAR
HUJJA da manufa saboda haka mu bazamu bude
fuskokinmu ba saidai mu gwabza daku a
hakan.Kafin sannan kuma muna son mu san
dalilin
dayasa kuka kawo mana wannan hari na
MAMAYAR
BAZATO.Koda jin wannan batu sai Yarima
Mangul ya
bushe da dariyar mugunta sannan yace,ai shi dan
fashi bashi da wata hujja takai hari face don ya
kashe rayuka kuma ya kwashe dukiya.Koda yake
nasan ka san ko ni waye tunda ni fitacce ne a
wannan nahiya kuma ada ni ba dan fashi
bane,amma
a yanzu ni UNGULU ne dakan ZABO!Har yanzu
ina
nan akan matsayina na Yarima Mangul dan Sarki
Alkas mai jiran Gado.Yakai wannan jarumi ka
sani
cewa zan iya yi muku adalci guda daya kai da
dukkan jama’arka naki kasheku na karbe
dukiyarku,amma sai idan zaku bude fuskokinku
naga
ko ku su waye?Koda jin wannan batu sai Barde
Ruhaisu ya tari numfashin Yarima Mangul yana
mai
daka masa tsawa yace,ba zamu taba bude
fuskokinmu ba don cika umarninka kuma kaidin
nan
baka isa ka iya kashemu ba ko ka karbe
dukiyarmu.Ina mai shawartarka daka janye
jama’arka
ku bar wannan wuri idan ba haka ba kuwa sai
kayi
nadamar kawo mana wannan hari.Idan ka
kuskura
ma sai na sake guntule maka daya lafiyayyan
hannun naka!!Koda jin wannan batu sai Yarima
Mangul ya fusata ainun ya zare takobinsa kuma
ya
daka tsalle daga inda yake ya dira a gaban Barde
Ruhaisu ya kawo masa wawan sara aka.Cikin
bakin
zafin nama barde Ruhaisu ya kare saran.Nanfa
suka
ruguntsume da azababben yaki,ya zamana cewa
suna kaiwa Junansu SARA DA SUKA cikin
tsananin
bakin zafin nama,juriya da bajinta,sauran dakarun
kuwa na kowanne bangare sai suka zuba ido
suka
zama yan kallo tunda ba’a basu umarnin suyi yaki
ba.
WAYE ZAI SAMU NASARA A WANNAN
AZABABBEN
YAKI DA AKE KWABSAWA TSAKANIN YARIMA
MANGUL DA BARDE RUHAISU?
INA LABARIN YARIMA LUBAINU DA BAKON
JARUMI
DASU SARAUNIYA AKISATUL SAUWARA DAKE
CIKIN
GIDAN BOKA DARBUSA?
SHIN YARIMA LUBAINU ZAI CIKAWA ALJANA
BADI’ATUL SARIRA ALKAWARIN DAYA DAUKAR
MATA NA KWANCETA DAGA DAURIN DA BOKA
DARBUSA YAYI MATA ITA KUMA TA TAIMAKA
MASA?
WANE NE BAKON JARUMI DA TARIHINSA?
YAUSHE BAKON JARUMIN ZAI SAMU NASARAR
YADA ADDININSA NA MUSULUNCI A NAHIYAR?
SHIN YARIMA LUBAINU YANA SAMU LAFIYA
DAGA
LALURAR DA YAKE CIKI?
YAUSHE YAZARINA ZATA SADU DA MASOYINTA
YARIMA LUBAINU?
WAYE ZAI MALLAKI ALLON SIHIRI A TSAKANIN
DUMBIN JAMA’AR DA SUKE NEMANSA?
WANE IRIN MUGUN TANADI SU SARAUNIYA
AKISATUL SAUWARA ZASU YIWA BAKON
JARUMI?.
Mu hadu a littafin ALLON SIHIRI littafi na Biyar
(ALLON SIHIRI-5)don jin cigaban wannan
kayataccen,kasaitaccen labari.
1 hr · PublicTARWATSA MAZA-1 TYPE E »««
Nidai a iya yawon da nayi bantaba shiga daji
mai kwarjini da ban tsoro ba, tamkar dajin
shajaril maurud. Ba komai ne yabawa dajin
kwarjiniba, face wasu irin dogayen bishi yoyi
gami da tulun ganyaye a sama da suka cika
gami gami da duhuwa mai yawan gaske, ga
kuma tarin manyan duwatsu masu siffofin
ababan tsoro da kuma jibga-jiggan tsaunika.
Muggan dabbobin daji kuwa adadinsu ya
wuce kima sai dai ka gansu suna ta
gilmawa, in ba don a sama muke tafiya ba,
da sai mu yita yaki da su sai da muka yi
tafiyar sa’a hudu a sama cikin iska a dajin
na shajaril maurud, sannan muka jiyo wani
irin gagarumin gurnani na dodo gurmazu,
koda jin gurnanin wanda ya cika djin gaba
daya sai hantar cikina ta kada, duk da
jarumtaka da dakakkiyar zuciya irin tawa.
Shi kuwa aljani barzila gaba dayan jikinsa ne
ya dume da zafi, tamkar an tsomasi a ruwan
dumi mai tiriri, ya kama karkarwa bai san
sa’adda ya saki fitsarin firgita ba. Duk da
cewa a tsorace nake, sai da dariya ta kwace
mini, na ce, “Haba namijin duniya, ai ka
karya alkadarin jarumtakarka wadda kayi a
baya, domin bai kamata ba ace tsoro har
yasa ka saki fitsari saboda kawai ka ji
gurnanin dodo gurmazu ba”.
Cikin karfin hali, da rawar murya barzila
yace, “Haba ya shugabana, ai bama fitsari
ba, ko kashi na saki bai kamata kayi mamaki
ba, Katuna fa cewa shi fa dodo gurmazun
nan a halin yanzu duk duniya babu wata
halitta mai karfin damtsensa da karfin
sihirinsa. An ce komai kaurin bishiya, idan
ya nausheta da hannu daya, saita ratattake,
ta fadi kasa idan kuwa ya kwarara ihu,
girgizar kasa ake yi, tsawa da walkiya na
amo daga cikin bakinsa. Komai yawan maza
a cikin dakika biyar yake tarwatsasu, walau
rundunar bil’adama ko ta aljanu”. Kawai sai
nayi ajiyar zuciya, nace “Lallai kuwa baka yi
laifi ba, domin tsoro wajibine, amma fani
bana tsoron bala’I dan babu Wanda
banganiba, sai dai na firgita da shi. Ai kawai
muci gaba da tafiya, ina so ka durfafi inda
kake jiyo sautin wannan gurnani”.
Cikin matukar tsoro aljani barzila yace,
“Banki tatakaba ya shugabana, amma dai
katuna cewa, “Riga kafi yafi magani. Bai
kamata mu tari dodo gurmazu gaba da gaba
ba, zai fi kyau mu dunga yin sanda da labiya
har mu isa inda yake, ai shi yaki dan zamba
ne a duk sa’adda abokin gaba ya fara ankara
da abokin gabarsa, to yana iya samun
hikimar da zai iya samun nasara akansa da
wurwuri”.
Batare da wata gardama ba, na amince da
wannan shawara, saboda haka sai aljani
barzila ya sauko kasa ya dira bisa turba,
nima na sauko daga kansa muka fara tafiya
sanda muna leke-leke, wani lokacin ma har
kwanciya muke a kas muna tafiya da ruf da
ciki.
Kaico! Rashin sani yafi dare duhu, ashe duk
wannan tafiyar dudduke da mukeyi dodo
gurmazu ya hangomu tun daga can nesa,
saboda kwarin idanunsa yana iya hango abin
dake tafiyar sa’a shida a bayansa ko
gabansa, sannan duk irin abin da ya jingina
ajikinsa sai kalar jikinsa ta koma irin launin
abin sak komai hasken da ke wajen, ido
bazai iya shaidashi ba.
A wannan lokaci da muke tafiyar ruf da ciki,
dodo gurmazu na can sama bisa wata
gabjejiyar bishiya mai tsananin girma da
tsawo. Ni kam na tabbatar da cewa, wannan
bishiya babu ta biyunta a duniya, domin ko a
tarishi ban taba jin labarin bishiya irintaba.
Haka dai muka ci gaba da tafiyar ruf da ciki
har muka iso gaban wannan narkekiyar
bishiya, amma bamu ga komai ba, kuma
bamu sake jin gurnanin dodo gurmazu ba.
Mun dade a kwance muna kasa kunne ko
zamu ji wani motsi, amma ba muji ba.
Daga can sai muka mike tsaye na dubi aljani
barzila nace, “Abin da zamu yi kawai mu hau
can saman wannan bishiya mu tsaya in dai
muka yi haka zamu iya hango dodo gurmazu
a duk inda yake domin zaton da nake ba a
nan kusa yake ba. Yana nesa da mu ne”.
Koda jin wannan shawara tawa, sai barzila
ya cika da murna, yace, “kwarai kuwa kayi
tunani mai kyau, haka za a yi” nan take na
sake hawa bayan barzila yai sama dani, sai
da muka kure tsawon bishiyar sannan muka
sauka a kan wani katon reshenta guda. Cikin
hanzari aljani barzila ya zaro kwari ya dana
akan wannan katuwar baka tashi ya tabe
bakan ya shiga kalle-kalle ko zai hango dodo
gurmazu ya sakar masa harbi. Ni da Nake
bayan barzila sai na daga wani gatari nawa
sama na tsaya cak! A waje daya ina kallon
gabas da yamma, kudu da arewa, kuma ina
leko kasan bishiyar. A binda bamu saniba
shine, munyi aikin banza domin kuwa mun
kulle kofar gida da barawo a ciki, domin
kuwa tsakaninmu da dodo gurmazu bai wuce
taku uku ba. Ashe shi ma yana kan bishiyar
amma da yake kalar jikinsa ta saje da kalar
jikin bishiyar ko kadan bamu ganshi ba.
Kwatsam! Ba zato kuma ba tsammani, sai
dodo gurmazu ya sauya kalar jikinsa izuwa
ainashin tasa ta gaskiya, ya baiyana daf da
aljani barzila. Koda barzila yai arba da dodo
gurmazu yaga irin kwar jininsa da muninsa
sai ya firgita kuma ya dimauce, bai san
sa’adda ya saki kwari da bakan dake
hannunsaba ya juya da nufin ya bude fuka-
fukansa ya tashi sama, amma sai dodo
gurmazu ya cabo jelarsa cikin zafin nama,
sai ga barzila na reto a sama, tamkar dan
biri na wasa.
A dai-dai wannan lokaci ne na dako tsalle
daga inda nake tsaye na taho a sama zan
kirbawa gurmazu sara a tsakiyar kansa,
amma sai gurmazu ya mangareni da daya
hannun nasa, na rikito kasa, tun asama na
fita daga haiyacina, naji kamar anyi mini
kanshin mutuwa. Ai kuwa ina fadowa kasa
na sume. Nidai ban san abin daya faruba
daga sannan sai farkawa nayi na ganni a
cikin katon keji tare da aljani barzila, da
kuma wadansu aljanu kimanin su dubu biyu,
duk suna ta faman rusa kuka shi ma aljani
barzila sai ya tayasu kukan.
Koda barzila yaga na farfado, sai ya dubeni
a fusace, yace, “Kaga irinta ko, ai dama na
gayamaka bamu isa mukawar da dodo
gurmazu ba, ga shi yanzu ya kamamu.
Wadannan aljanu duk fursunoninsa ne, kuma
sun gaya mini cewa, sudubu arba’in ne ya
kamosu, kullum yana diban biyar yana
cinyewa, yanzu saura su dubu biyu kacal,
kaga kenan muma mun zama abincin sa.
Haka kuma sun tabbatar mini da cewa babu
wani makami ko sihiri da zai iya karya
wannan keji, har mu sami damar fita daga
cikinsa. Abin da zance da kai kawai shine,
ince koka bar wasiyya a gida kafin muyi
wannan tafiya?”.
Yayinda naji wannan tambaya, sai na bushe
da dariya, al’amarin daya baiwa dukkanin
fursunonin aljanun mamaki kenan, domin
gashi su a matsayinsu na aljanu, suna kuka
saboda sun shiga bala’In da babu fita, amma
ni a matsayina na bil’adama ina dariya. Ti
me nake takama dashi? Shin ina zaton zan
iya fita ne daga cikin wannan masifa? Amsar
da basu sani ba kenan, amma dai ai tunda
suna tare dani zasu zuba ido su ga iyakar
gudun ruwana.
sHIN HASANUL MAUZUR DA ALJANI
BARZILA ZASU KUBUTA DAGA HANNUN
DODO GURMAZU, HAR HASANUL MAUZUR
YA KASHE WANNAN GIWA TA DODO
GURMAZU, YA YANKO HARSHENTA?
WADANNE SAMARI Ne ZASU SHIGA GASAR
NEMAN AUREN GIMBIYA SHULAIRA, KUMA
DAGA CIKINSU WAYE ZAI CI GASAR YA
ZAMO MIJINTA.
Muhadu a TARWATSA MAZA littafina biyu
don jin cigaban wannan kasaitaccen labari.

Previous page 1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button