Zee Baby Book 1 Page 5

Page 5
*…..asalinsu* Alhaji Hasheem Almahadee magawata haifafan garin tahoua ne cikin Niger sun gaji sarauta GABA da baya mahaifinsa ne kan kujera mulki shidayane gun iyayansa rana tsaka aka riske gawar iyayansa lokacin yana kasar waje karatu labari na zuwar masa, ya dawo gida domin ahalin yanzu shine Wanda zai hau kan mulki anshirya komai aka hada yan mata biyu rana daya aka aura masa, amma sai me ana gobe nadin sarauta aka nemesa sama da kasa aka rasa, Abu kamar wasa, saida aka shafe shekaru biyu babu labarin Hasheem Almahadee Wanda suka kulla manakisar kuwa tuni sun hau kan sarautar suna zuba mulkinsu matan da aka aura mishi kuwa tuni an kashe auran shikuma baisan ya akayiba ya tsinci kansa a daura Nigeria yana yawo garari wani bawan Allah mai suna Alhaji Nuhu haifafan katsina ne amma mahaifiyarsa ce ta daura shi ya temakesa yana ganinsa yasan aikin jifane cikin ikon Allah ya dawo haiyacinsa yasha mamaki da ya gansa a Nigeria Katsina Nuhu ya tambayesa ko shi na wani garine dan ya ganshi jajur ga kyau tamkar balarabe bai boye komaiba ya labarta masa koshi waye Dan kasar niger ne buzune na Tahoua yagaji sarauta gaba da baya saboda itane aka fito dashi an kashe masa iyaye amma yace baya shawar komawa gida indai akan sarauta aka fito dashi yawon duniya ya hakura zai zauna ana Allah yasa haka yafi Alkhairi shikenan mafarin zaman sa tare suke hada hadar kasuwanci shida Nuhu tamkar uwa daya uba daya haka suke bayan shekaru kusan goma hasheem da nuhu sunyi aure sun zama wasu sunyi arziki shakaru na tafiya arzikinsu na bunkasa kuma har lokacin bai taba jin son komawa gidaba hasheem yanada yara hudu Abdulmutallab sai mai binsa Hauwa’u sai Faisal sai Salmanu daga kansu haihuwa ta
Tsaya sun taso cikin gata da kulawa Hasheem da zainab sunba ‘ya’yansu tarbiya sun sami karatun boko da na Addina Allah ya kara bunkasa dukiyar Hasheem dan haka yace yaran sa kowa ya zabi kasar da yakeso ya tafi ya biyawa kowa yaje karatu lokacin Faisal yanada shekaru sha bakwai yace saudia nuhu ya tsaya masa kan komai saboda Hasheem yafi sonsa a yaran Nuhu akwai yayarsa acan madina Faisal ya tafi yake karatunsa cikin kwanciyar hankali da nasarori gidansu na Katsina abin kallone dan babu abinda babu aciki Hasheem na kula da yaransa shida zainab Abdulmutallab ne ya matsa masa saida ya gayamusu garunsu ya nemi izininsa ya tafi Tahoua gun dangin mahaifinsa cikin ikon Allah yasami tarba maikyau amma banda mai martaba ana Allah ya hadasu da Khadija suka kulla soyayya kafin ya dawo yana dawowa magana tayi karfi Dole hasheem ya tafi shi da Nuhu aka sanya ranar aure khadija yarinyace kyakyawa itama buzuwace GABA da baya farace tas kama Abdulmutallab sunyi aure cikin so da kaunar juna da mutum ta juna bayan bikinsu da shekara biyu ta haifi danta namiji yaci sunan Nuhu bayan shakaru hudu ta haifi Mahabeer shima sai bayan sharu hudun ta haifi mace mai sunan maijidda ko yayeta batayiba cikin ikon Allah tasake samun cikin ta haifo zankadeden danta namiji kyakyawa ajin karshe jajir dashi yaron
Akwai farin jini tamkar ba’a taba haihuwa ba shine yaci sunan Almahadee wato Faisal tun yana karaminsa akwai son gaskia da son girma bayason raina ko kadan ga miskilanci da jiji da kai bai fiye fara’a ba idan ba yana tare da khadija ba wacce suke kira Ghaisha Kakansa hasheem ya saka masa Sardauna saboda yaron kana kallinsa kasan jinin sarautane ba karya sunan ya bishi tun yana karami yace karatun likita zaiyi ya temaki mutane to fah tun yana karami sukece masa Dr Sardauna kyawunsa ya fits daban agidan Dan sak kamar Hasheem ya fito yanada kanne hudu shima Najib ke bimasa sai Zainab sai hafeeza da auta Nawwara bangaran Mariya Amarya da Abdulmutallab ya aura saida ta kwashe shekaru biyar ta haifi yarta daya nana khadija sunan uwar gidansa sai mareniyar yarta da tazo da ita Khalisat idan ka ganta bazaka taba cewa ba yar gidan bace babu banbanci yarinyace kyakyawa amma ba canba batada laifi dai farace saidai batada hayaniya shiru shiruce suna zaune lafiya bazaka taba cewa ghaisha da Mariya kishiyoyineba sai Hauwa kanwar Abdulmutallab tana aure itama cikin Katsina da yaranta hudu sai salmanu shima yayi aure da yaransa biyu wannan zuri’ar Allah ya hada kansu suna kaunar junansu yaransu sun taso cikin hadinkai da kaunar junansu Faisal ne kawai da baya kasar rashin auransu ya damesu sunata Addu’ar Allah ya janyo hankalinsa gid
*********
Faisal bayan ya kwashe shekaru tawas saudia yana, karatu bai taba zauwaba gidaba kuma bashida kiyuwa duk da ana aiko masa, kudi daga gida hakan baisaba yazauna ranar da ba karatu fita ya keyi neman na kansa dan yanaso shekarun biyu da suka rage ya koma kasarsa yabasu mamaki dan yanzu haka ya tara uban dukiya taban mamaki amma babu wanda ya sani ranar ya fito zai tafi daidai wani super market wani shahararan mai kudi sun fito da iyalinsa daga, siyaya zai shiga mota yada takarda ta fado aljihunsa da sauri ya nufi wajan daide ya dauka motar ta tafi dan taxi ya gani ya shiga yace yabi waccen motar bayansu sukebi har kofar gidan ya biya dan taxi ya nufi gun mutumin amma har sun shige gida yayi sallama yajima kafin ya fito yake tambayarsa, lafiya ya bashi takardar da ya yada bai saniba ya amsa ya duba saida ya tsorata dan takardun kadarorinsane da ya mallakawa yarsa kwaya daya Raiyan godiya yayi ta masa ya jasa suka shiga ciki yayi masa alheri sosai amma yaki amsa yace yayine don Allah sosai tarbiyar Faisal ta burge Fahad Abbu Rahaman to daganane suka saba ya sama masa aiki a kamfaninsa kullum yana gidan kamar dan gida sai abunda Fahad Abu Rahaman bai saniba Raiyan tun ranar da taga Faisal ta mutu akan sonsa tun tana daurewa har ta baiyana masa kiyawa yayi saboda tsoron balaraban saudia bayaba hausa dansa duk shima ba hausarba ne idan ma ba ance maba ba barabe baneba to bazaka ganeba saidai su suna banbance jansin su Abu kamar wasa Raiyan ta kwanta jinya ciwo hankalin iyayanta yayi kololuwar tashi har aman jini takeyi likita yace sumata abunda takeso zuciyarta takai matakin karshe dab take da bugawa nanne suka tambayeta ta fadamusu damuwar sunyi rantsuwa da Allah zazu mata dan basu taba zaton harakar soyayya ce jin sun mata alkawali yasa, tace Faisal ne takeso ranar anyi tashin hankali sunce saidai ta mutu taya zazu aurar da ita da Wanda basusan asalinsa ba kuma ba hausarsu dayaba, da sukaga fadan bayayi suka dawo lallashi suna rokonta tace ta janyen tunda sun mata alkawali har kuka suka mata amma fur takiya karshema da, numfashinta ya dauke saida, tayi sati bata farfadoba ganin zazu rasata yasa sukace sun yada ta zureshi saboda alkawali amma ba ruwansu da ita kuma yada yasasu bakin ciki taki musu biyayya itama sai ta zubar da hawaye haka akayi bikin Hasheem da Abdulmutallab su ne sukazo akayi komai amma Faisal yace shi yananan bazai komaba saidai ya rika zuwa ziyara. bayan aurene Ashe mahaifin Raiyan kodiri dayawa aransa sosai Raiyan da Faisal soke zuba soyayya kamar ba gobe Ashe shima yana sonta ganin kamar abin bazai yubane yasa da farko yace bayason ta bayan auransu da shekara biyu ya kammala karatunsa
cike da nasarori ya sami aiki a Jeddah Dole sukabar madina koda sukaje sallama gidansu Raiyan ba Wanda ya kulasu haka suka tarkata suka tafi lokacin tana fama da laulayin ciki yana bata wuya saida ya warware sosai ta samu sauki, ranar haihuwa ta zagayo taci uwar azaba amma kasa haihuwa tayi da kanta sai tiyata akamata aka ciro yara ukku maza biyu mace daya kyawawa, masha Allah ranar Faisal ya nuna tsantsar farin cikinsa amma babu Wanda yazo daga gidansu Raiyan sai wata Faisal ya samo take kula dasu, ranar suna ya sakawa mazan Hassan da hussaini macan sunan mahaifiyarsa, Zainab ranar anyi bidira a Nigeria yan uwa sai jin dadi sukeyi suna jinjina al’amarin Ashe rabone tunda Fahad yaji labarin Raiyan maza ta haifa yaji dadi sosai yasan yanzu zai cika burinsa haka akayi ta tafiya rayuwa na gudu yaransu sun girma sosai saide sunfi shagwaba zee baby yarinyar akwai fitina sosai ga mugunta har uwayan bata bariba gashi muguntar ta tafi karfi suma mazan imusu takeyi makaranta mai tsada ubansu ya sakasu ko acan bata barin yaran mutane har malaman sun dukanta to ranar basu ba koyarwa idanu take likewa ta koma gefe tana dariya ahaka saida aka canza masu maranta ukku daide lokacine Faisal karami yazo karatunsa na likitanci Wanda zai dauki tsawon shekaru biyar amma yana madina sai karshan wata yake zauwa jeddah