HAUSA NOVELINTEESAR 4

INTEESAR 4

INTISAAR BOOK 4

 

Inteesar tayi shiru a dan tsorace bayan ta

hadiye maganin tana jiran jin me xata fara ji

a jikinta, har na kusan minti goma bata ji

komai ba hkn yasa ta mayar da hankalinta

ga TV dake ta aiki shi kadae tana kallo, taji

ta fara jin bacci amma har lkcn bata ji ko da

ciwon kai a jikinta ba, hkn yyi mugun daga

mata hankali, tace na shiga uku kar dae

cikin baxae xube ba, ta dauko magungunan

ta shiga balla su kuma xata sha yanda ta sha

daxu hankalinta a tashe, ta ciro su knn ta

jawo kofin ruwanta xata sake korawa taji

wani matsanancin ciwo a mararta da bata

taba ji ba, tayo waje da ido a tsorace

gabanta na faduwa, a hankali cikinta ma ya

fara ciwo ya hade da na maran, tunda take

bata taba jin irin wnn ciwon a jikinta ba,

kankame cikinta tayi ta shiga mutsu mutsu

daga xaunen da take tana buga tiles da

hannunta, taga xama ya gagareta ta kwanta

kasa tana rike da cikin tana juye juye, ita nn

tana ga xata iya jure ciwon har ya gama

cikin ya fita, da marar ta yyi wani irin murda

mata ta daura hannu a ka taji kmr

mutuwarta ce ta xo, bata san lkcn da ta fasa

wani axababben ihu ba tana rike da cikin,

lkci daya ta hada xufa, ta shiga kwala ihun

axaban da take ji a gigice, a tare Aliyu suka

fito da Safeena ya karasa kusa da kofar a

rude ya murda yaji a rufe, bubbuga kofar ya

shiga yi yana kiranta, ta fashe da wani

matsanancin kuka da kyar tace “wayyo

mutuwa xanyi ya Aliyu,” ya koma daki a

rikice ya shiga neman spare key, safeena

kam da gudu ta koma dakinta ta dinga

tsallen murna shknn ta sha ruwan, ya

karaso jikin kofar jikinsa na rawa ya bude

kofar ya afko cikin dakin yana kalle kallen

inda xae ganta, can kusa da gado ya ganta

kwance tana juye juye ya karasa gabanta da

sauri ya durkushe ya dago ta a rude yana

tambayarta me ya faru, kasa cewa komae

tayi sae juye juyen da kawae take a

hannunsa, a rikice ya shiga cewa “don Allah

kiyi min magana fateema me ya same ki,”

duk da mugun axaban da take ji hannunta

na rawa ta shiga tura kwalin magungunan

karkashin gado tana mayar da numfashi da

kyar wae kar ya gani, ya lura da abinda take,

ya rike hannunta da sauri yana kallon

kwalin yace “meye wnn,” girgixa masa kai ta

shiga yi tana neman xamewa daga jikinsa

ya daga kwalin tabs din yana kallo baki

bude, a rude ya jefar ya shiga cewa

“innalillahi wa inna ilaihi raji’un meye wnn,”

wani ihun ta kuma fasawa ta kankamesa

tace “wayyoo ya Aliyu, cikina, mutuwa xanyi

wllh,” yana jijjigata cikin tashin hankali ya

shiga cewa “ki gaya min shi kika sha

fateema?” kasa cewa komai tayi sae jujjuya

kanta da take cikin axaba, ya ga farar

takardar scan din dake gabanta ya dauka da

sauri hannunsa na rawa ya bude, jefar da

takardar yyi ya fixgota cikin mugun tashin

hankali yace “wayyo fateema ki gaya min

magungunann nn kika sha? Plss kiyi min

mgna,” a rude yake maganar, ita ko da kyar

ta shiga gyada masa kai tana jawo

numfashi kmr me shirin suma, ya dafe

kansa yana kallonta yace “nashiga uku, oh

my God,” saketa yyi da sauri ya fice daga

dakin, ta dinga ihu tana birgima cikin

axaban ciwo tana kiran Abbanta, ya dawo

dakin da sauri rike da allura, kwance ya

ganta cikin jini, yyi wani kara a rude ya jefar

da alluran hannunsa ya karaso kusa da ita

da sauri yace “ya salam, innalillahi wa inna

ilaihi raji’un, fateema fateema” kuka take

ssae tana juye juye kmr ranta xae fita jini

sae malala yake ta kasanta, ya dagota ya kai

mata wani wawan mari a gigice ya shaketa

yace “kika kashe min yarana, yhu kill my

kids” ta kankamesa tace “wayyo mutuwa

xanyi na shiga uku,” wani marin ya kuma

kai mata ya dagota ya buga ta da bango,

tunda take bata taba ganin yanayin da Aliyu

ya shiga ranan a tare da shi ba, idonsa ya

kada yyi jajur muryarsa na rawa yace “ki

gaya min ubanwa ya baki maganin nn, wani

asibiti kika je,” ya wurgar da ita ya buga

bango da hannayensa biyu yace “ya salam,”

juyowa taga ya sake yi ta fara kkrin fita

daga dakin ya fixgota ya shaketa yana huci

yace “me yarana suka maki kika kashe su

fateema,” ta rike hannayensa biyu cikin

kukan tashin hankali tace “no plss kayi min

rae ya Aliyu cikina xae kasheni,” bugata yyi

da bango da karfi ya fice daga dakin tasan

be gama da ita ba, tayi karfin hali ta rarrafa

ta fito daga dakin da kyar tana neman inda

xata safeena ta fito da sauri ta ja ta suka

shige dakinta ta rufe kofar da sauri, inteesar

ta xube kasan dakinta tana mayar da

numfashi har lkcn jinin dake xuba jikinta

bae tsaya ba

.

Aliyu ya fito kmr wani mahaukaci daga

dakinsa ya shiga nata a rikice bae ganta ba,

ya fito ya shiga buga kofar Safeena da karfi

ganin trace din jini tun daga kofar Inteesar

har nata, alamar nn inteesar ta shiga, cikin

tsawa yace “baxa ku bude min kofar ba”

cikin sanyin murya Safeenah tace “haba

dear ka sa ma xuciyarka ruwan sanyi mana,

so kke kayi kisan kai, ka bar ta da halin da

take ciki mana xaka dinga dukanta kuma,”

ya daka mata wani raxanannen tsawa yace

“na rantse da wanda numfashina ke

hannunsa idan ban hada dake ba kada Allah

ya bani abinda yake nema, baxxa ki bude

min kofa ba” ya karasa maganar yana huci,

ta bude baki da mamaki tana kallon kofa,

A’aaah lallai abun babba ne yau, to fa, ta dan

tabe baki tace “to ni ko sae dae kar ya baka,

don baxan tsaya hka kawae ina ji ina gani

ka kashe yar mutane gabana ba,” bae sake

cewa komai ba ya juya da sauri kmr xae

tashi sama ya koma dakinsa yana huci,

inteesar kam na durkushe dakin sae kuka

take tana juye juye kmr ranta xae fita, kila

karshenta ne ya xo yau, gashi har lkcn jini

bae tsaya mata ba sae bulbulowa yake, duk

kayan jikinta ya baci da jini hka ma dakin

safeena, safeena ta dauko Zaninta da sauri

ta mika mata a xuciyarta tana cewa “yau ai

sae dae jininki ya tsiyaye ki mutu yarinya

baxan bude kofar ba bare ya taimaka maki,”

inteesar ta kasa karban xanin, sae cewa

take mutuwa xanyi, safeena tace “baxa ki

mutu ba,” key suka ji Aliyu ya saka a kofar,

Inteesar ta fasa ihu jikinta na rawa taji kmr

ta sume ynxu ta samu saukin abubuwan

dake faruwa ynxu “wayyo kayi min rae ya

Aliyu wlh yau mutuwa xanyi, don Allah kaji

tausayina” ya afko dakin rike da kwalin tabs

din da ta sha yana huci, idonsa ya koma

jajur kmr gauta, kanta yyi ya fincikota da

karfi ya dago ta, muryarsa na rawa yace

“wllh wllh baki gaya min wanda ya baki

magungunan nn ba, sae na kashe ki kema

yau,” jikinta na rawa ta shiga girgixa masa

kai hawaye na bin kuncinta, ya shaketa da

karfi, cikin tsawa yace “baxa ki gaya min

ba,” ta yo waje da ido a tsorace, da kyar

muryarta a shake tace “xan gaya maka,” ya

watsa mata mari yace “uban me kike jira,” ta

fashe da wani matsanancin kuka ta juya

tana kallon safeena tace “ita ce ta kaini aka

bani,” Safeena ta yo waje da ido ta dafe

kirjinta tace “na shiga uku yarinya xata min

sharri, a ina kika ganni,” cikin kukan Axaba

Inteesar tace “ita ce ya Aliyu, ka tausaya min

cikina kasheni xae yi wllh,” a hankali Aliyu ya

saketa ta sulale kasa ya juya yana kallon

safeena da ta xama kmr mara gskyar gske,

duk ta rude, sae rawa bakinta yake ta kasa

cewa komai, ta fashe da kuka tace “wllh

wllh sharri tayi min Aliyu, a ina ta gan ni yau

da har xan kai ta a bata magani,” wani kara

yyi ya karasa kusa da safeenar kmr xaki ya

shaketa hawaye cike idonsa yace “ku ka

kashe min yarana, me suka maku safeena,”

bae jira me xata ce ba yyi wani irin buga

1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button