AZIMA DA AZIZA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

AZIMA DA AZIZA COMPLETE HAUSA NOVEL

    ????????????????????

Kuka Hajja keyi yayinda Inna Wuro da Yawuro suke ta aikin bata hakuri suna rarrashinta,amma pinaa Hajja kamar ba da ita ake yi ba, idonta ya kumba ya yi him sabida kuka fuskarta ya yi jaa! Baffa ne ya duka a gabanta ya ce
“Jumala? Kiyi hakuri,In sha Allah idan anyi duniya DAN MANZON ALLAH S,A,W, Azima da Aziza zasu dawo garemu In sha Allah,kuma yaranki zasu dawo mutane ko da kuwa zan rasa raina na miki alkawari!” ita dai Hajja bata ce komai ba, tun daga wannan rana Hajja bata um bata um-um, idan ta zauna idonta na kan bakin kofa,ta ajiye idanunta har izuwa ranar da yaranta zasu dawo gareta.

   ????????????????

Fitan Azima yawatawa ta ci gaba da yi,dama ita ba sallah take yi ba balle ya dameta, idan kuma wani mai kararren kwana tsautsayi tasa ya shiga hidimarta ta kashesa ta yi gaba, yau kwananta uku da shigowa garin kano bata damuwa da wajan kwana idan dare ya yi duk babbar bishiyar da ya mata zata zama macijiya ta hau ta kwanta tayi bacci ko ta huta, yau ta fito tana cikin tafiya taji ƙaran mota ƙiiiiiii! da sauri ta juyo ta ga wata matashiyar budurwa ce wacce zata kai shekara ashirin da biyar,fitowa tayi tana zazzagawa Azima zagi, yayinda take binta da ƙaramin kallo
“Ban da hauka taya zaki rufe fuska ki dinga tafiya a kan titi! Sakarya kawai bagidajiya!!” cije baki Azima tayi meyasa ake son ce mata bagidajiya? duk da bata san ma’anar kalman ba amma taji ta tsani kalman, lankwabe murya ta yi ta ce
“Dan Allah ki taimaka mini, ni yar gudun hijira ce an kashe dukkan yan uwana a rigarmu ni daya ce kawai na rage,ban san kowa ba ban san inda zanje ba, dan Allah ko aiki ne a gidanku ki nema mini zan dinga yi” yatsine fuska ta yi tana fadin
“Kuma fa kamar naji Hajiya na neman mai aiki,to amma gaskiya sai dai na sakaki a cikin both dina dan ba zaki shiga mini mota ba”
“Ina ne shi hakan bat din?”
“Banza jahila both nace, nan kenan zo ki shiga” ta fada tana mata nuni da both tana budewa,Azima ta shige tana murmushi tare da fadin
“Matakin farko!” tana rufe murfin both din Azima ta koma Macijiya, shiga motar tayi ta ja tana tsaki.

  A kwana ukun nan Aziza ta fito daga bakin titi ita ma,tana fitowa ta zube a kan titi tana sakin kuka tana kiran sunan Hajjanta da Baffanta, Inno Fandi ce ta taimaka mata ta fiddota bakin titi sannan ita ta koma, kuka sosai Aziza ta yi kafin ta tashi ta hau tafiya, tana ganin kamar ta shigo wani sabuwar duniya ne, bata ma san a inda take tafiya ba, shi kuwa da sauri yake jan mota,yana driving yana duba tym, wayarsa ce ta yi kara yana dubawa ya ga Friend 4 Life, dagawa ya yi, ya ɗan yi shuru tukunna kafin ya ce

“Hey Dude bazan maka karya ba,wlh bazan je na dubasa ba,guy din nan ya raina min hankali, jiya banyi niyyar kwana a garin yola ba amma ya sakani kwana, yanzu haka ma nikam gani a hanya ko kwana zanyi sai dai na kwana amma yau din nan sai na kasance a cikin garin Kd in sha Allahu!” yana magana a waya ransa a b’ace sai ji ya yi, ya yi sama da mutum, wani mahaukacin burki yaja ya fito da gudu, yana isowa gareta tana lumshe ido, duk da bai ga fuskarta da kyau ba gashi ya rufe amma daga ganinta a jeji ta fito, kallon gabas ya yi,ya kalli kudu,ya kalli arewa,ya kalli yamma bai ga wani ɗan adam ba, shi a tunaninsa sun fito kiwo ne yan uwanta suka tafi suka barta, to amma idan haka ne shi ya zaiyi da ita? Ga kanta ya fashe yana zubda jini, “No dogon tunani ba nawa bane i need to save her lyf first” ya faɗa yasa hannu yana shirin daukarta, wani mummunar faduwar gaba ce ta riskesa inda yaji dukkan wata gab’a ta gangar jikinsa ya sake, saurin kauda abun a ransa ya yi ya dauketa ya sakata a mota ganin bata motsa, yana addua Allah yasa dai bata mutu ba.

  ????????????????????

MOMYN AHLAN✍????
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: ????????????????????????????????????????

    ????✨ AZIMA DA AZIZA????✨
    (???? Macizai ne????)

    MALLAKAR.

ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)

SAHIBAR KAINUWA.

Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.

Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.

بسم الله الرحمن الرحيم
________________________

????KAINUWA WRITERS✍???? ASSOCIATION????????
{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan????????

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

________________________

MARUBUCIYAR.
1- HALITTA DAGA ALLAH NE.
2- GUDU A JEJI.
3- SHUHADA.
4- NIDA ƘANNEN MIJINA.
5- WA’YA KASHE ZAHRA’U?(#200).
6- COLONEL UBAIDULLAH.
7- ITA CE ZUCIYATA(#200).
8- SAMIMA (MACIJIYA CE.
9- GAWURTACCEN SOJA(#300).
10- DA NA SANI NA.
  11- BADAWIYYAH
12- DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)
Now
13- AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE????)

Follow me on wattpad,@Fateemah’0

   ????????????????????

PAID.
????️==3️⃣7️⃣↪️3️⃣8️⃣

Murmushi ya mata ta zo ta rungumesa tana yi masa sannu da hanya, ya amsa da “yawwa sannunki,ina Mom kar dai har tayi bacci?”
“Kai anya kuwa, da muna zaune da ita a nan bata jima da tashi ta hau sama ba”
“Okay bari na dubata” ya faɗa yana maida dubansa ga tv’n ya ce
“Ke da kallon horror ko, sai kin fara ganinsu a gaske zaki sani” murmushi Sultana ta yi ta koma tana zama shi kuwa ya hau sama,dakin Mom ya shiga da sallama tana zaune tana waya, zama ya yi kusa da kafarta har sai da ta gama wayar ta ajiye kafin ta kallesa cikin kulawa ta ce
“Nawaz sai yanzu? Ya hanya an dawo lafiya?”
“E wlh Mom, Alhamdulillah! ina wuni? Ya gida? na sameku lafiya?”
“Alhamdulillahi Doctor, fatan dai lafiya ko? Ko dai gajiya ce dan fuskarka ta tuna,yanzu haka ma da Amminka muka gama waya wai ta kiraka wayar bata shiga nace ba mamaki hanya ce ba netwrk”
“E hakane zan kirata gobe yanzu dare yayi zan shiga part dina,kunyi waya da Son dinki ne Mom?”
“E dazu ya kirani dan albarka”
“Mom muna cikin waya da shi dazu tsautsayi tasa na buge bafulatanan yarinyar mutane”
“Subhanallahi!” Mom ta faɗa tana zabura
“Kwantar da hankalinki Mom tana hospital dina” nan ya bata labarin yadda hatsarin ya kasance har izuwa shawaran da ya yanke na tahowa da ita kaduna idan taji sauki sai a maidata gida, Mom ta sauke ajiyar zuciya ta ce
“Shawaran da ka yanke mai kyau ne Nawaz, Allah ya bata lafiya, ma je mu dubata gobe idan Allah ya kaimu ni da Sultana”
“Allah ya kaimu Mom” ya faɗa yana duba agogon hannunsa
“Dare yayi Mom zanje na kwanta na huta akwai gajiya a tare dani”
“To Allah ya tashemu lafiya a huta gajiya,Allah ya yi albarka” Nawaz ya amsa da amin yana tashi ya fice a dakin, yana saukowa ya kalli Sultana ya ce
“Idan baki kashe tv’n nan kinje ki kwanta ba Allah sai na zaneki” da sauri Sultana ta miƙe ta kashe tv’n kasancewar tasan halin Yayan nata, sai da ya ga ta hau sama kafin ya fice ya nufi part dinsa, wanka ya yi ya gabatar da salloli har da nafila ya jima yana addua kafin ya tashi ya koma gado ya kwanta,har ya lumshe ido ya buɗe ya dauki wayarsa ya kira Amininsa suka hau ɗan taba hira inda yake ba shi labari ya buge bafulatana, Allah ya kiyaye gaba ya masa,sannan ya ce
“Yaushe zaka dawo america?” Nawaz ya sauke ajiyar zuciya ya ce
“Nan da 2wks In sha Allahu,but idan nazo ina shekarar karshe zamuyi mu dawo gida gabadaya?,dan gaskiya na gaji da zaman outside”
Daga can bangaren ya ce
“In sha Allahu, duk da ni bana son zaman nigeria gaskiya”
“To ya zaka yi dole ka dawo,duk lalacewa kasarka kasarka ne, sannan karka damu da abinda Momma take maka, ka ci gaba da yi mata biyayya a matsayin uwa,wata rana zata gane In sha Allah” ajiyar zuciya ya sauke, nan Nawaz ya gane damuwar dake damunsa dan haka ya kau da hiran ya jawo musu wata, sun kai biyun dare kafin suka yiwa junansu sallama, yana ajiye wayar bai jima ba bacci ya kwashesa,yana cikin bacci ya hau mafarkin yarinyar da ya buge da mota, suna cikin wani ƙasurgumin jeji sai faman ihun take zabgawa tana fadin ya taimaketa ya taimaki rayuwarta, tana ihu tana gudu yana binta a baya, da haka har suka je jikin wata babbar bishiya taja ta tsaya kanta a sunkuye tana sanye da kayan fulaninta,ta ƙanƙame jikinta tana ihu, shi kuwa yana riƙe da fitila a hannunsa yana haskawa sabida tsananin duhun jejin, yana shirin matsowa gareta ya ga mummunar tashin hankali dan kuwa gani ya yi ta koma wata zabgegiyar macijiya???? fara sol sai ƙyalli take yi,tana ci gaba da ihun ya taimaketa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button