AZIMA DA AZIZA COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

AZIMA DA AZIZA COMPLETE HAUSA NOVEL

????????????????????

Yau ce ta kama ranar da zasu tafi zaria, gaban Aziza ke dukan uku-uku tun farkawarta bata da kuzari,ganin haka yasa Mom cewa Aziza meke damunki ne?
“Ba komai Mom”
“A’a Aziza karya ba halinki bane, karki fara meke damunki?” a sanyaye ta ce
“Kaina ke ciwo Mom”
“Subhanallahi! Idan ba zaki iya tafiyar ba ki bar shi ki huta abunki ita mai biki sai ta tafi” nan Sultana ta yi tsalle ta dira da cewa wlh Aziza bata isa ba,kawai dai son mutane ne da bata yi, Mom ta ce
“A’a Sultana baki zo da gaskiya ba, yarinya tace miki bata da lafiya kice bata isa ba,kinga wuce ki tafi kawai Allah ya kiyaye hanya” Sultana tace ita kuwa idan har Aziza ba zata je ba itama ta fasa, Aziza ta ce
“To ba kin riga da kin gaya mata yau kina hanya ba?”
“Sai na ce mata na fasa????, kuma ai ba ina hanya nace mata ba muna hanya nace mata”
Aziza ta yi murmushi ta ce
“A’a ba za ayi haka ba Antyna ta kaina tashi mu tafi” Mom ta ce
“Ki biyewa Sultana ki kashe kanki”
“A’a mom ai nasha magani, ciwon kan zai sakeni”
“To Allah ya kiyaye hanya, a gaida su Hajiya Habiba, ai da ace zaku biya ta kano da na baku sako wa su Hajiya Lawiza” haɗe rai Sultana ta yi ta ce
“Gaskiya Mom ba zamu kano ba, daga zaria sai kaduna In sha Allahu” ganin yadda Sultana ta haɗe rai yasa Mom dariya ta ce
“To shikenan Allah ya kare” ta faɗa tana rakosu har jikin mota, ta ce
“Ina dai ba zaku wuce kwana biyun ba ko?”
“In sha Allah Mom ba zamu wuce ba,ai ba zamu je mu zauna mu barki ke ɗaya ba” daga haka driver ya jasu ,Mom tana ɗaga musu hannu.

     Kasancewar tsakanin kaduna da zaria ba nisa nan da nan suka isa aka hau shagali dasu, haka sauran ƙawayen amarya Sulaiha suka ja Aziza a jiki, amma matsalarsu daya da ita shine rufe fuskar da take yi, sai da Sultana tace musu ai ko a gida ma haka take wuni fuska a rufe kasancewar tana da matsalar ido, daga haka suka fara yi mata fatan sauki, sai yaba kyawunta sukeyi da dogon gashinta,ita dai Aziza nata murmushi da godiya, dan duk tunaninta ya raja'a a ta hanyar da zata bi ta gudu, dan suna isowa zaria bata yi kasa a guiwa ba ta duba amma bata ga Azima ba, yanzu garin da take hari taje shine garin da Mom tace zata aiki Sultana idan har zasu je, wato KANO.


   Ranar da suka zo anyi party da washe gari asabar aka ɗaura aure, bayan an daura aure da daddare akwai dinner daga wajan dinner za a wuce da amarya gidan mijinta da washe gari kuma sai su koma kaduna, a daren yau idan suka je dinner shine Aziza tasa a ranta zata gudu.

@@@@@

     Sun sha makeup dinsu, suka cakare cikin net dinsu kalar sky blue sunyi kyau sosai,ita dai Aziza taƙi yarda ayi mata makeup har amarya Sulaiha take fadi cikin wasa ai ita da kyau ɗinta ba sai an mata kwalliya ba tunda bata so a barta.


   Suna can babban hotel din da aka kama ana ci gaba da gudanar da abunda ya tara jama'a, Khalil ya kira Sultana a waya kasancewar bata ji a ciki yasa ta fito waje tana wayar.


  Wasu maza ne su uku a wajan gate din hotel din suna cikin mota sai aikin busa hayaki suke yi, wani ne ya daga ido daga cikinsu ya sauke a kan Sultana dake waya, sai da ya kara goge idanunsa kafin ya ce

“Kaii Ɗan Gidan Alhaji? Wa nake gani a can kamar kanwar Doctor Nawaz?” wanda aka kira da sunan Ɗan Gidan Alhaji ya dago yana ƙarewa Sultana kallo ya ce
“Jar Uba! Ita ce wallahi! To me ya kawota zaria?” ɗayan ya ce
“Ko ma me ya kawota, lokaci ya yi da zamu rama abunda Yayanta ya mana a kanta” Dan Gidan Alhaji ya ce
“To yanzu ya kuke ganin zamuyi?” dayan ya ce
“Ah mu kwamusheta kawai,muje mu huta da ita, ya ɗanɗani abunda mukaji sadda yasa aka kullemu a kan wasu banzan talakawa!”
“Lallai Shaho ka kawo shawara, kuma dabadin Baban Ɗan Alhaji ba wlh da mun ƙare rayuwarmu a kurkuku” Dan Gidan Alhaji ya ce
“Yanzu ku daina wannan maganar tunda ba mutane yanzu a kusa ku fita ku dauko mana ita” sai da suka leka suka leka kafin suka fito daukar Sultana wanda hankalinta ya yi nisa sosai a wayar da take yi da Khalil.

   Aziza na zaune cikin kawaye da ta waiga ido bata ga Sultana ba ta tashi a hankali tana fadin

“Ki yafeni Anty Sultana zan tafi, ba zai yu ba rayu daku ba danni ba mutum bace,zanje neman yar uwata dan mu koma duniyarmu!”

 Da wannan tunani zuciyarta babu dadi kamar karta tafi dan an saba, ta fito saɗaf-saɗaf.

 Fitowar Aziza ya yi dai-dai da lokacin da su Shaho suka roɗa ma Sultana katako a bayan kai a kan idon Aziza,ihu Aziza ta saka tana fadin

“Antyyyy Sultanaaaa!!!” ganin haka yasa Ɗan Gidan Alhaji Faɗin su haɗa da Aziza su kwamuso.

   ????????????????????

MOMYN AHLAN✍????
[4/13, 10:13 AM] Mom Ahlan: ????????????????????????????????????????

    ????✨ AZIMA DA AZIZA????✨
    (???? Macizai ne????)

    MALLAKAR.

ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)

SAHIBAR KAINUWA.

Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.

Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.

بسم الله الرحمن الرحيم
________________________

????KAINUWA WRITERS✍???? ASSOCIATION????????
{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan????????

https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association

________________________

MARUBUCIYAR.
1- HALITTA DAGA ALLAH NE.
2- GUDU A JEJI.
3- SHUHADA.
4- NIDA ƘANNEN MIJINA.
5- WA’YA KASHE ZAHRA’U?(#200).
6- COLONEL UBAIDULLAH.
7- ITA CE ZUCIYATA(#200).
8- SAMIMA (MACIJIYA CE.
9- GAWURTACCEN SOJA(#300).
10- DA NA SANI NA.
  11- BADAWIYYAH
12- DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)
Now
13- AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE????)

Follow me on wattpad,@Fateemah’0

   ????????????????????

GOOD MORNING???? ☕☕????????

PAID.
????️=4️⃣9️⃣↪️5️⃣0️⃣

Dan haka suka bugawa Aziza katako a kai sau daya,jiri ne ya ɗibeta amma bata suma ba, ta hau kokawa dasu dan ta kwace Sultana daga hannunsa, Shaho yasa katako ya dinga sauke mata shi a gefen kai har ta suma kanta ya fashe yana zubar da jini, sannan suka daukesu suka saka a mota.

 Basu zarce ko ina dasu ba sai wani gidan Ɗan Gidan Alhaji da Babansa ya gina masa, suna zuwa su Shaho suka fito dasu Sultana da Aziza wanda suke sume, suka shige dasu, suna shiga dasu suka kwantar dasu a parlour, D'an Gidan Alhaji ya ce a bari su farka, Shaho yace ba sai an jira sun farka ba dan babu lokaci, a yayyafa musu ruwa kawai su farka, ga wannan yarinyar ba mamaki ita ma kanwarsa ce dan naji ta kiran wannan da Anty, wai cakwai kenan gata kirjinta a cike yake,yaran dai za a shana fa" Dan Gidan Alhaji ya yi murmushi yana lashe baki tare da binsu da kallo, Shaho ne ya kawo ruwa cikin bokati ya shekawa su Sultana da Aziza tun daga kansu har kafarsu, a firgice Sultana ta farka ita ce ta fara dawowa hayyacinta tana riƙe bayan wuyarta dake mata tsami, ware idanunta ta yi a kan Ɗan Gidan Alhaji, tayi saurin ja da baya tana girgiza kai,tana juya idonta ta sauke shi a kan Aziza wacce bata riga da ta farka ba, a razane Sultana ta hau jijjiga Aziza tana kuka tana kiran sunanta ganin yadda jini ke b'ulb'ula a kan Aziza, cikin kuka Sultana ta ce

“Wlh idan Yayana ya sani dukkanku babu wanda zai tsira” D’an Gidan Alhaji ya ce
“Kafin nan Ubana ya min biza na bar kasar, kuma ko da zai sani sai mun miki mummunar tab’o,ko nace sai munyi muku mummunar illa!” Ya fada yana sa hannu zai damki Sultana Aziza ta cafki hannunsa gam tana daga kwance dan duk taji abunda yake fadi, cafka bana wasa ba Aziza ta yiwa hannun Ɗan Gidan Alhaji, da mugun mamaki Sultana ke kallon Aziza wacce take kwance idonta rufe ga jini, cikin rawar murya Sultana ta ce
“A….ziii…..zaaa…! dan Allah ku kai min ƙanwata asibiti kar ta mutu, baku da imani!! Ku azzalumai ne!!” Shaho ya yi kan Sultana yana zuwa zai kai mata mari Aziza tasa kafa ta tokaresa sai da ya yi sama kafin ya bugu da bango ya faɗi kasa, da sauri Dan Gidan Alhaji ya ce
“Kai wannan yarinyar fa na ga alama tana ji da kanta, ga shi ta riƙe min hannuna kamar zata b’alla, ke dan uwarki da Ubanki! Sakar min hannuna” ya fada yana jan hannunsa da karfi amma Aziza ta ƙi sakewa, Sultana kuwa tana takure a jikin Aziza tana kokarin yadda zata tsaida jinin da ke fita akan Azizan.

  "Shaho, yarinyar nan fa taƙi sakina!!" Shaho wanda ya sha ƙasa ya miƙe a fusace yana fadin

“Wannan yarinyar sai fa mun nuna mata cewa ni cikakken dan iska ne, ban taba kisan kai ba, amma inaji zan fara a kanta, dan naga tana fama da tashen balaga, ko dazu bugu ɗaya nayi wa dayar ta suma amma ita sai da na mata biyar! dan haka ba zata sakeka ta dadi ba,bari ka gani” Shaho ya faɗa yana jan wani karfe a bayan windown labule, ganin haka yasa Sultana fasa ihu dan ta ga gadan-gadan ya nufi Aziza dake kwance, a haukace Sultana ta hau faɗin
“Dan Allah Aziza ki sakesa, ba danni ba Dan Girman Allah, kinga munyi sallama da Mom lafiya-lafiya kar a koma mata da gawawwakinmu, dan Allah Aziza ki sakesa! Ki sakesa nace!!” Sultana ta faɗa da karfi a tsawance, sake masa hannu Aziza ta yi, tana sakinsa ji ya yi tamƙar kashin hannunsa ta tsatstsage,a hankali tasa hannu a tsakiyar gashin kanta ta dafe,da kyar ta miƙe zaune sabida jirin dake dibarta dan ta bugu sosai a kai,inda yake saurin musu illa kenan shine duka a kai, amma duk sauran jiki dan sun bugu aikin banza ne.

 Kanta a duƙe tana riƙe da kai da hannunta daya, dayan hannun ta yi musu nuni da yatsarta manuniya cike da gargaɗi ta ce

“Duk wanda baya so Uwarsa! ta haifi wani, to kar ya kuskura ya sake ya taba mini Antyna, ku maidamu inda kuka dauko mu!” dariya Shaho da ɗan Gidan Alhaji da ɗayan suka yi, ƊAN GIDAN ALHAJI ya ce
“Zamu maidaku bayan mun yaga muku rigar mutunci! Ke kuma mai bamu umarni kar mu tabata, Yayanta ne yasa aka kullemu watanmu biyar a kurkuku da kyar mahaifina ya fiddomu, dabadin shi ba ma da har yanzu bamu fito ba, ai kema bamu san kanwarsa ba ce! Mun daɗe muna neman hanyar fansa! Sai ga shi ta kawo kanta har zaria, abun ya bada kala fa, dan haka ke ki fara zuba ido ki ga yadda zamu mata kafin a gama da ita a zo kanki, Shaho ku banƙaremin ita!” kukan tashin hankali Sultana ta saka tana kokarin kama Aziza su Shaho suka fizgota suka bajeta a kan carpet ɗaya ya riƙe mata hannaye ɗaya ya riƙe mata kafafu, kuka Sultana take yi tana ambatar sunan Allah da Yayanta da Mom da Aziza da Khalil, Aziza sai yunkurin tashi take yi ta kasa, ganin Ɗan Gidan Alhaji ya fara sa hannu yana tattaro doguwar rigar dake jikin Sultana yana yin sama da shi rintse ido Sultana ta yi, ta sadaƙar kawai,ganin haka yasa Aziza ware gashin kanta tasa hannu ta b’alli daya tasa a bakin, wani gurnani ta saki tare da hucin Maciji????, jin hucin maciji yasa Sultana buɗe ido da sauri dan tasan irin wa innan abubuwan tunda tana yawan kallonsu, saurin juyowa suma Ɗan Gidan Alhaji da muƙarrabansa sukayi suna kallon Aziza wacce take tsaye gashi ya rufe mata fuska, kwashe gashin ta yi ta tattare ta maida shi baya ta ƙulle,bata da wani mafita wanda ya wuce haka, idan har ta bari tana kallo aka yiwa Sultana fyaɗe ba zata yafewa kanta ba, dole Sultana tasan asalin wacece ita a yau, tana tsaye jini na kan wanke mata fuska, dama idonta a rufe yake,hannu tasa ta shafe kanta nan take aka nemi ciwo aka rasa, bama iyakar Ɗan gidan Alhaji da mutanensa ba, harta Sultana ware ido ta yi kamar zasu faɗo kasa yayinda zuciyarta ya yi wani mugun tsinkewa, Shaho ne ya yi karfin halin faɗin
“Waike wacece ke!?”
“MACIJIYA????, AZIZA MACIJIYA!!” tana faɗi ta buɗe idonta nan take ta rikiɗe ta sama katuwar Macijiya fara sol sai kyalli takeyi, ba shiri Su Shaho suka saki Sultana wanda ganin Aziza ta koma Macijiya ta saki ihu tana sumewa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button