BAKAR WASIKANOVELS

BAKAR WASIKA 14

“Ki tausayawa zuciyar nan tawa ki kira wayata ko zata samu sukuni”

“Karka damu zan kiraka, na gode sosai”

“Nine da godiya yau zan yi kwanan farinciki”

Ya fada sannan ya rufe mata motar Ramlee yaja suka bar gurin.

“Ina kika san shi? Baturiya Allah ya miki farin jini”

Dariya tai kamin ta labarta mata yadda akai ta sanshi, sannan ta dora da na ganin da Nura tai mata abokin mijinta kuma amininsa.

“Ke kar ya dame ki, idan ma ya fada masa ki bururuce ki ce ki kam sam ba ke bace, idan ya dage ke din ce kice tare da yayanki kika je siyen waya”

“Kuma fa kin kawo shawara, idan ba haka ba kam zai iya fusata sosai domin dazun na ci mutun mai mana maganar kudin haya na san kuma za su fada masa”

“Saboda me? Ai ba haka ake ba, nawa ne kudin hayar?”

“80k”

“Just 80k? Yanzu zan baki 100k da mutumen ya baki sai ki nemi inda mai hayar yake ki bashi gaba daya, wayar da ban siya miki ba zan baki kudin daman na yi niyar kashe miki 50k akan wayar dan haka zan baki su a hannu, gobe kuma zan kawo miki kayan mata masu kyau ki fara shirya kanki kamin lokacin da saku gana da Alhajin”

“Har da wani shan kayan mata?”

“Eh mana, kuma idan kika fara sha karki yarda ki bar Faruq yaje kusa da ke”

“Ni daman bana shan kayan mata ai, mutum yana fama da talauci ko a sha kayan mata me zan samu? Shiyasa ba ruwana da shan su, kuma ba kullum nake barinsa yana damuna ba”

“To ki dai kiyaye, yanzu kina isa gida ki fara neman mai kudin hayar ki bashi hakuri ki bashi kudinsa, kin ga idan ya dawo zai rage jin zafin tun da kin biya kudin hayar”

“Haka zan yi Inshallah na gode sosai kawata”

“Allah dai ya bar mu tare”

“Ameen”

A inda ta faka motarta dazun ta sake tsayawa, ta ciro kudin ta bata sannan sukai sallama, Baturiya ta fita ita kuma ta juya ta hau titi.

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button