BAKAR WASIKANOVELS

BAKAR WASIKA 6

“Ai dole kace na yi hakuri kam, ban da hakuri me kake da shi da zaka ba ni Faruq? Yanzu dan na samu kudi na siye nama na ci ya zama laifi? Ka san ina da ciki ina kwadayin abubuwa amman kai zargina ma kake, ni wannan cikin ma zubar da shi zan yi Wallahi, dan ba zan haihu ba ka yanka min bunzuru, wata kila ma ba zaka yanka min komai ba ka bar ni kyari da ido kamar kwaruru baki salab kamar Salamatu ina kallon yan barka ayi ta mana tsigumi”

“Allah da yai masu kudi be manta da ni ba Rafi’a, ban san wace irin macece ke ba, idan na fita waje ina cikin damuwa da bakinciki a maimakon idan na dawo gida na samu nishadi sai na tarar bakinciki gida yafi na waje yawa, har fargabar shigowa nake”

“To ka sake ni mana, ko zama da ni dole ne? Kai wai kana ganin Allah ba zai hukuntaka yadda kake azabbatar da mu da yunwa?”

“Kika sake furta wata magana sai na mareki Wallahi”

Ya fada cikin bacin rai, da muryar dake nuna da gaske yake. Ganin hakan yasa dole tai shiru domin ta san halinsa idan ya fusata be iya ba.

TALBA POV.

Zaune yake saman carpet yaran na zagaye da shi, sai kallonsu yake yana murmushin. Farincikin yara musamman marayu na daga cikin abunda yafi komai faranta masa rai, hakan ne yasa shi bude gidan marayu, kuma yana kai ziyara lokaci zuwa lokaci, wani lokacin kuma yana zuwa gurin ya wuni tare da su, ko ya dauke su ya fita da su zuwa gurin shakatawa.
Ya kalli agogon hannunsa sannan ya daga yarinya dake cinyarsa da bata wuce 5 years ba ya mike tsaye. Sai yaran ma suka mike tsaye suka bi bayansa har zuwa gurin motarsa, ya saba musu idan zai tafi yana raba musu kudi ko alawa wani lokacin kuma chocolate. Sai da ya shiga cikin motar sannan ya mika hannunsa baya ya dauko ledar sweet ya bude ya fara raba musu, hannu biyu suke sakawa suna karba kamar yadda ya koyar da su, hayaniyar yaran yasa Ali dake driver side ya bude ya fita yana waya. Da dai daya Talba ya bisu yana basu, idan ledar ta kare sai ya bude wata, har sai da ya raba musu duka sweet din da ya zo da shi, sannan ya kwantar da kujerar motarsa ya kwanta yana jiran Ali dake waje yana waya.
Bayan Ali ya kare ya dawo cikin motar ya rufe yana kallon abokinsa.

“Ka gama da su?”

Talba ya kalleshi kamar be ji abun da ya tambaya ba.

“Har yanzu tunanin abun da kai ma Leila kake yi?”

“Saboda Daddy da Momy na yi, kuma zan cigaba da yin hakan matukar hakan zai faranta musu rai”

Yana rufe baki sakon Leila ya shigo wayarsa.

“Ka zo ka kai ni shopping yanzu”

Ya dauke idonsa bayan ya gama karantawa.

“Leila tana ganin hakan ba zai saka na tsane ta ba? Ina son girmamawa Ali, ai ya kamata tace Yallabai, but look how she text me kamar wani direbanta”

“Tana da gaskiya, ya kamata ka koyi girmama mace”

“Ba macen da take kasa da ni ba, wannan ranar ba zata taba zuwa ba, ba zan taba zama wawa akan mace ba, sauke ni gida”

Ali yayi murmushi yayi ma motar key, har suka isa gidan idon Talba a rufe, hannyensa kuma rumgume a kirji. Harabar gidan Ali yai farkin Talba be ce masa komai ba ya bude motar ya fita ya nufi kofar falon, kananan kaya ne a jikinsa, sai kamshin turare yake. Yana isa ya danna door bell din ya tsaya jikin kofar, cikin kankan lokaci aka bude masa kofar domin yanayin yadda yake danna door bell din dabam ne, da yasa ake gane shi ne. Dagowa yai a hankali ya kalli Baaba wanda ta bude masa kofar hawaye na sauko mata. Dan fuskar Mama yai domin ta saba idan ta bude masa zata masa sannu da zuwa angona, sai yai mata murmushi ranar da yan kwarai suke a kai kuma zai soma taba wasa da ita ko ya amsa mata. Shigowa yai cikin falon yana kallon Leila dake tsaye kusa da sofa ranta a bace, sai kuma ya juyo ya kalli Baaba.

“Miya faru?”

“Babu komai ranka ya dade”

Baaba ta amsa masa sannan ta fara tafiya. Binta yai da kallo kamin ya maida dubansa gurin Amal dake tsaye upstairs tana zayyana masa abun da ya faru.

“Ya Leila ce ta mareta”

Talba ta kalli Leila.

“Baaba ta ho dan Allah”

Baaba ta juyo ta dawo kusa da shi ta tsaya cikin damuwa.

“Bata hakuri”

Talba ya fada yana kallon Leila, wani irin kallon mamaki tai masa, Momy na jin haka ta fito daga kitchen.

“Ita fa tai min laifi”

“Kin sani sarai bana maimaita kalma”

“Baka san abun da ya faru ba”

“Bana son na sani”

Ya fada yana matsawa kusa da ita, kana kallon cikin idonsa ka san ransa ya bace. Sai da ta kalli Momy sannan ta kalli Baaba ta ce.

“Ki yi hakuri”

“Babu komai ya wuce”

Baaba ta fada sannan ta nufi kofar fita falon zuwa BQ inda dakinta yake. Sai da ta fice sannan Momy ta karaso inda Talba yake tsaye tana fadin.

“Wannan be kamata ba sam, taya zaka wulakanta yar’uwarka a gaban yar aikin?”

“Be kamata ta dauki hannu ta mareta ba Momy, no matter what Baaba tai mata, ta yi jika da ita”

“Gaskiya ka ci mutunci Leila, ka tauye mata hakki Talba, na yi shiru ne kawai saboda bana son na yi magana a gaban Baaba”

“Kin san inda na fito Momy? Gidan marayuna, yaran da suke can basu da uwa ba su da uba, wasu ma a titi aka dauko su aka kawo su nan, wasu kuma danginsu basa iya kula da su, amman Leila Allah ya ba ta komai, kudi, uwa, uba, ilmi, dukiya, sai dan na saka ta ba da hakuri ne zai zama cin mutunci?”

“Wannan kuma ai dabam ne, akwai tazara mai fadi mai tsawo tsakanin mai kudi da talaka, akwai abun da be kamata ayi agabansu ba, ko kuma a saka ayi musu, musamman inda muke da gaskiya”

“Wannan zarar da kike magana, ban tana ganinta ba, kuma ba zan taba ganinta ba, ban taba jin na fi wani dan yana talaka ina da arziki ba, sai dai na ji nafi shi saboda yana kasa da ni a aiki ko a shekaru, ko kuma saboda ni ina miji ita tana mata, amman ba zan taba iya cin mutuncin wanda ya haife ni ba, wasu talakawan sun fi mu a gurin Allah”

Yana gama fadar hakan ya nufi kofar fita a fusace. Momy ta bishi da kallo tana kada kai.

“Finally, gatan Daddynka ya saka har ni kana iya tsayawa ka fadawa magana… ”

Be juyo ba dan be ji akwai abun da zai sake ce mata. Balle kuma ta kuma ya kula Amal dake zayyana masa abun da ya faru daga can inda take tsaye.

“Ya Leila ce ta kawo mata ruwa shi ne, gurin mika mata carpet ya tadeta ruwan ya zuba a jikin Ya Leila sai ta mareta…Shi ne abun da ya faru Ya Talba ko baka tsaya ba na fada maka, Ya Leila ce bata da gaskiya”

Ta karasa ita da Leila suna watsawa juna harara, daman can haka suke kamar ba yan’uwa ba, basa shan inuwa daya.


Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe.
Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo.

Previous page 1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button