NOVELSUncategorized

BARIKI NA FITO (BOOK 1) 20

                     *PAGE 20*
Ta dad’e tana kallon wayan tare da tunanin mai yake nufi? Mai yasa zaice bazai zo gobe ba? Tsinta kanta tayi da kiranshi…..
Yana ganin kiranta ya kashe tare da kiranta baiyi magana ba…..

Tace Yarima lafiya kuwa?
Yace kaman ya?
Tace naga yanda kake magana yau, kaman kana fushi, nd kuma ni naga Banyi maka laifi ba akan maganan Walima ne K…..
Ya Katseta tare da fad’in wannan shine laifinki, you know what? Tunda nake ban taba cewa Ina son ayi abuba ace min a’ah ba, duk abunda na fad’a hakan akemin but I don’t know why ke kike cemin a’ah….
Tace Yarima kayi hakuri dama naga….
Shuru tayi ta kasa magana
Yace Ina jinki .
Tace babu komai zanyi abunda kace tunda kana so inyi.
Murmushi yayi tare da fad’in good haka nake so, in nace abu a amsa min, ban son musu, ni mutum ne wanda ban cika son Ayi ta magana akan Abu d’aya ba, so plz my princess komai nace zan miki just accept it plz
Tace insha Allah daka yau komai kace Indai bai sabama Shari’a ba zanyi na’am dashi
Yaji dad’in maganan ta, yace my princess na kosa In ganki gobe I really miss you alot
Wani irin dad’i taji, tunda goben zai zo, amma saita ce cikin murya kaman namai son yin kuka ba kace baka son ganina ba
Murmushi yayi tare da fad’in ni na isa, ai bazan iyaba dole inzo inga my princess.
Tace Allah ya kaimu goben lafiya.
Ya amsa da Ameen tare da fad’in gobe a ina zan ganki? Gidanku?
Tace a’a inda ka ganni nan zamu sake had’uwa.
Yace but gobe akwai islamiya right? Har zaki iya zuwa ki koma?
Tace insha Allah, gobe ma ba zani islamiyya ba, saboda bama komai sai shirye shiryen Walima.
Yace ok Allah ya taimaka
Ta amsa da Ameen
Yace Mai za’a tanadar min?
Murmushi tayi tare da fad’in mai kake bukata?
Yace kiss…..
Kit Ta kashe wayan tana dariya tare da fad’in lallai Yarima kace wani abu, ai bazan taba nuna maka yanda nake ba…. Kiranshi ne ya kara shigowa wayanta murmushi tayi tare da d’auka
Yace haba my princess ya zaki kashe without giving me answer?
Tace Yarima banda wannan Mai kake so inyi maka?
Murmushi yayi tare da fad’in for now only kiss nake bukata sauran sai an bani ke.
Bariki tace nifa maganan abinci nake maka Tana maganan ne a shagwabance
Yace Indai na sami kiss from you am OK bana bukatar komai.
Tace Yarima good night ina jin bacci.
Dariya yayi cikin ranshi ya gane bata son yana mata maganan kiss dinne shi yasa tace Tana jin bacci, yace ok baby get ready 2moro insha Allah if I came I will get my kiss take care yana fad’in haka ya kashe wayan ba tare dajin Mai zata ce ba, bayan ya kashe wayan hotanta ya d’auko dake manne a d’akinshi yana ta Kare ma fuskanta kallo hannunshi yasa wajan lips dinta wanda ya zana shafawa yayi tare da fad’in sonki ya kamani da yawa, my princess I really love you so much you are my happiness, your love change me, sonki yasa na Fara magana Sosai how I wish Kema ki soni haka, da nace am d luckiest guy in the world.
Bariki kam tunda ta kashe wayan take wani irin murmushi Mai cike da nishad’i wanda gaba d’aya abunda Yarima yace yake sata nishad’i dajin dad’i, lokaci d’aya kuma ta gimtse fuska tare da fad’in kodai dagaske ina son Yarima ne? Kai Anya a’a kawai dai shi yasan yanda ake magana da mace ne kuma shi ba d’an iska bane, tunda yau yace Mata yana son kiss shi kawai yake bukata, sauran kuma sai an bashi ita….  Ido ta lumshe tare da fad’in Yarima na yarda da son da kake min, amma ina tsoran kasan koni wacece na tabbata bazaka aureni ba….
D’an shuru tayi tana nazari Mai yasa zan boye ma Yarima gaskiya? Anya nayi mishi adalci kuwa? Gaskiya gobe Idan yazo zan fad’a mishi gaskiya koda zai barni zan jure duk da kuwa bana son ya barni, gwara in fad’a mishi tun Kafin lokaci ya k’ure da wannan tunanin bacci yayi awon gaba da ita…….
*Yarima ne tsaye cikin fushi, bariki kuma tana tsaye ta bayanshi ya juya mata baya, tana kuka tana fad’in dan Allah Yarima kar kace ka fasa aurena danna fad’a maka koni wacece dan Allah Yarima Wlh na kamu da Sonka sai yasa na fad’a maka koni wacece Nasan zaka fahimc….. Daka mata tsawa tayi tare da fad’in keep quiet, macuciya fasi’ka, Allah na gode maka da kasa ban auri mace mazinaciya ba wacce ko wani dan iska ya gama da ita, tir da irin halinki Wlh I never hate someone in my life kaman yanda na tsaneki yanzu, I hate you bana son ganinki tafi kiban waje…. Nufanshi tayi tare da ri’ke Mai hannu tana kuka tare da fad’in dan Allah Yarima kayi hakuri Wlh bazan iya rayuwa ba tare dakai ba nas……  Tas ya sakan mata wani mari…….*
Da sauri bariki ta tashi duk ta had’a zufa, Kalle Kalle ta farayi da sauri ta tashi ta d’auko ruwa cikin karamin fridge din d’akin tasha Tana sauke numfashi dakyar tare da fad’in Allah na godema da kasa mafarki ne ba gaskiya ba…… Lokaci d’aya kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi, Yarima Ina son fad’a maka koni wacece amma yanzu tsoro ya kara kamani na tabbata bazaka iya aurena a haka ba kuka take Sosai Mai cin rai lokaci d’aya kuma ta share hawayenta tare da fad’in bazan iya juran rashinka ba Yarima kaman yanda raina yake fad’amin in fad’a maka gaskiyan wacece niba, dole cikin biyu inyi d’aya….. Ranan dai bariki kasa bacci tayi kawai burinta gari Ya Waye Yarima yazo suyi magana duk da tana fargaba akan abunda zata fad’a Mai a halin yanzu tasan tabbas tana son Yarima tunda har ta tabbata bazata iya juran rasa shiba, haka kuma tana son ta fad’a mishi wacece ita dan tana son tayi aure tsarkakakke.
*******
Hjy Umaima ce zaune a falon hjy habiba Tana fad’in habiba Wlh bazan iya rabuwa da bariki kuke ce mata ko wa? Wlh Ina son yarinyar zan nema mata maganin aljanu Indai ta warke ai Kinga ni shar, Kai yarinyar tana da jiki Mai Kyau ga nono a tsaye.
Hjy habiba dake zaune akan kujera haulat na kwance akan kujeran tasa kanta a cinyar hjy habiba, Hjy habiba na wasa da gashin Haulat, tace lallai Umaima yanzu duk abunda ya faru baki daddara ba.
Hjy Umaima tace naji tsoro amma duk matan da nayi hulda dasu ban taba ganin wacce naji Ina Sonta ba har nake burin muyi soyayya kaman bariki ba, wlh ko nawa zan kashe zan kashe in nema Mata magani sannan in biya bukata ta.
Hjy habiba tace toh Idan aljanun suka ki fita fah?
Hjy Umaima tace dan Allah bar min mugun baki malamai manya zan samu, suyi mata addu’a, nasan komai zai wuce Kinga daka nan saita dawo gidana inda zata yarda Aida na biya sadaki ma munyi aure….
Hjy habiba tace aure? Ke kina da miji ita inta sami mijin fah?
Hjy Umaima tace AI sai yasa nace zan aureta Kinga bata babu namiji saini d’aya zata zauna a gida na kaman y’ata nifa Wlh Kinga habiba koda asiri saina mallaki yarinyar nan Wlh dan tayi min
Haulat dai tana kwance tana jinsu bata ce musu komai ba
Hjy Habiba tace gaskiya In kikai haka baki kyauta ba, taya zaki hanata aure Bayan ke kina gidan mijinki?
Hjy Umaima tace Sonta da kuma kishinta shi zaisa inyi haka, Dan bazan iya juran inga wani yazo inda take ba da Sunan love…
Hjy habiba tace lallai kam amma duk maganan da hjy Umaima take haushi take ji dan itama son bariki take tunda ta ganta kuma itama tayi alwashin saita cita, tunda haulat ta fad’a mata bata da wasu aljanu, sonda take ma bariki shiya hanata fad’ama hjy Umaima cewa bariki bata da wasu aljanu, dan ta tabbata Indai hjy Umaima ta sani Wlh sai tasa an kawo mata bariki kuma sai tayi abunda takeso yanzu tana d’an tsoro ne sai yasa take cewa zata nema Mata magani, kuma tasan hjy Umaima dabin bokaye koda ba’a d’auko mata bariki ba ita da kanta barikin zata kawo kanta dan tana hulda da malamai na fitan hankali
Haulat dai shuru ta musu amma cikin ranta tana fad’in Indai bariki ce maganin ki za tayi dan ta wuce yanda kike zato, nima kaina inda naga dama zan nemeta amma sanin halinta yasa na boye maita ta, in takamarki kud’i bariki bashi bane a gabanta……
Hjy Umaima tashi tayi tana fad’in bari inje gida inada Bakuwa ta taso daka Lagos
Hjy habiba tace kuma? Wai ke Mai yasa baki zama da mace d’aya yau kici wancan gobe kici wancan?
Hjy Umaima tace ai shine yanzu nake son in zauna da mace d’aya inna sami bariki aita isheni
Hjy habiba tace adai rage cin mata Kala Kala Kar ki d’auko Mai warin hq.
Dariya Hjy Umaima ta saki tace haba ai Kema kin San irin wanda nake ci fita tayi tana fad’in Kinga Bari inyi sauri.
Bayan ta fita haulat ta kalli hjy habiba, tace mum Mai yasa baki fad’a mata cewa bariki karya take ba, Aida kin fad’a mata bariki bata da aljanu
Hjy habiba tace kyaleta bata da alkibila
Haulat cikin ranta tace nikam zan fad’a mata danna tabbata zata bani kud’i Sosai dan naga bata da rowa, number dinta yanzu zan nema amma bazan bari mum ta sani ba….
Yau Nayi muku typing din rowa???????????? amma da babu ai gwara babu dad’i koh???????????????? gobe zan biya ku ????
~MARYAM OBAM~

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button