NOOR AL HAYAT COMPLETENOVELSUncategorized

NOOR ALHAYAT 17

Karasowa parlorn dattijuwar matar tayi har lkcn tana kallon khadijah tace “Where are you coming from?” Khadijah ta dago a hankali tace “Just 3 houses away….” Matar tace “Gidansu Hajiya Salaha kenan?” Khadijah ta gyada kai, matar tayi shiru tana kallonta, can tace “An aiko ki ne?” Ta girgixa kai tace “A’a
kawai abinci nake son ci” kallon d’an ta da ke xaune matar tayi, khadijah ta ci gaba da cin abincin gabanta, shi dai bai ce komai ya mike xai bar parlorn, mahaifiyar sa ta bi sa da ido tace “Kaje to Sadiya ta xuba maka wani abincin koh” ya juyo yace “Noo dama it’s not as if ina jin yunwa mum, anjima xan ci” daga haka ya wuce ciki, matar ta dinga kallon khadijah dake cin abincin sanyi sanyi, can ita ma ta juya ta bar parlorn, jawo remote khadijah tayi ta kunna TV ta gyara xama tana facing tvn, tana cin abincin amma gaba daya ta ba tv attention dinta, bayan kusan minti talatin taji ance “Wai ke baxa ki gida bane? Ba kin gama cin abincin ba” Ta juyo da sauri ta kallesa sai kuma ta marairaice tace “Plss ina son in gama kallon nan” sakin baki yyi yana kallonta ga plate din abincin ta gama, bai dai ce komai ba ya fita rike da makullin mota, ba a dau lkci da fitarsa ba sai ga yan mata uku sun shigo gidan sanye da kayan islamiyya, tun da suka shigo suke kallonta ita kam ko sanin sun shigo bata yi ba, Muryar matar daxu taji a parlorn tace “Ke baxa a nemeki gida ba” khadijah ta dago da sauri, sai kuma ta bata fuska tace “Anty bana son xuwa gidan” Matar ta buda ido tace “Baki son xuwa kuma?” Shiru ta d’an yi kafin tace “First… They are so dirty and unkept, and I don’t like their dishes…. I don’t just like the house” matar dake kallonta da mamaki tace “Toh ba gidan ku bane” khadijah ta girgixa kai a hankali tace “Noo uncle dina ne ya kawo ni” matar tace “Maza tashi ki tafi kar ayi ta nemanki kin ji” kallon agogo tayi taga karfe shiddah ta ce “plsss ma… am I always welcome here?” Matar ta d’an yi murmushi tace “Sure” khadijah ta kwashe plate da cups da ta ci abinci tace “Where can I find d kitchen” nuna mata matar tayi ta kai ta fito sannan ta dau ruwan goron da d’an ta ya ajiye tace “In tafi da shi?” Matar ta gyada mata kai, murmushi tayi ta risina tace “Thanks ma” daga haka ta nufi kofar fita matar ta bi ta da ido, tana fita gidan gaba daya ta hango mutane tsaye bakin gate din gidan kawunta, tafiyar minti kusan shidda tayi ta isa gidan, tsaye ta tadda su Hajiya Salaha da yaransu gaba daya ga makota ana ta surutu, Sajida ce ta fara ganinta tace “Lahhh mama kun ganta” sai aka juyo gaba daya ana kallonta, Hajiya Salaha ta isa inda take da sauri ta fixgota tace “Daga ina kike?” Khadijah dake bin kowa da kallo tace “Just few houses away…..” Bata rufe baki ba Hajiya Salaha ta sauke mata mari, wani ihu ta fasa tana rike da fuskarta tana jin duniyar na juya mata, tunda take ba a taba kai hannu jikinta ba bare fuskarta sai ranan, iyaka a sa ta tayi kneel down ta daga hannu, har tsadadden bokon da take xuwa a kano ma ba a duka, Hajiya Salaha na huci ta shiga kunduma mata xagi tana cewa “Allah ya isa yawon da kika sa muka dinga yi muna nemanki kamar gantalallu, sai Allah ya saka mana… Kuma bari Alhaji ya dawo wllh xaman ki ya kare gidan nan ya je can ya kai ki gun talakawan dangin uwar ki…” Kuka kawai khadijah take tana rike da fuskarta, hakuri mutanen wajen suka dinga ba Hajiya Salaha suna cewa ai yarinya ce, Hajiya maimuna da ganin Khadijah ya sa ta shiga parlor ta fito da wayar wuta ta nufo ta, wata mata ce tayi saurin janyeta tace “A’a don Allah ki bari Maman Hafsa, ayi mata hakuri” wata mata ma ta rike wayar tana ba Hajiya Maimuna hakuri, Hajiya Salaha tace “Ku bar ta ta ci mata mutunci crook ce wannan yarinyar da ku ke gani haka, wa yasan gidan uban da taje” Matar da ta ja Khadijah ta duka dai dai fuskarta tana kallonta tace “Ina kika je ake ta neman ki yan mata” Khadijah na shessheka tace “I was hungry and I had to…..” Kasa ci gaba tayi ta rushe da kuka, Matar ta d’an kwalalo ido tace “Tohhh bata jin Hausa ne?” Hajiya Maimuna tace “Iskancin fa?? Tsabar shakiyanci ne da iyayi da kinibibi ita er mai kudi, toh wai ma ina mai kudin yake yau? Ku ce min yana kabari, toh idan ma xata sauke kai ta yi rayuwa yanda ko wani talaka ke yi ya rage nata, uwar me suka tsinana ma mutane banda tsoron Allah har Alhaji xai daukota ya ajiyeta a gidansa, wai I am hungry… To kafafuwar uwarki xan dafa maki in baki banda abinda aka girka kika ki ci” Hajiya Salaha tace “Ae komai ya xo karshe, ya dawo yasan yanda xai yi da ita, wnn ‘ya sai ta kashe aure, taje can inda xa a dinga dafa mata indomie da kwai a bata shayi mai kauri da custard ta sha, mu ba rainon tea da bread muka ma yaranmu ba” daga haka tayi shigewarta ciki, Matar dake rike da Khadijah tace “Ke me yasa kika fita baki sanar masu ba? Komai aka baki kuma bata sai ki ci ba khadijah”  Khadijah ta kasa cewa komai sai kuka take, jin kiraye kirayen magrib duk aka fara watsewa ana ma su Hajiya Allah ya kyauta, wasu kuma na tausayin khadijah domin kuwa suna ganin iyayenta basu mata adalchi ba in har abinda su Hajiya ke fada gaskiya ne a kanta, ba a san yanda rayuwa xata kaya ba don haka iyaye ya kamata su dinga koya ma ‘ya yansu both the right and left side of life, yau idan an ci na masu kudi gobe a ci na talaka bawan Allah, wannan xai sa yaro yyi adapting a duk situation da xai tsinci kansa. Khadijah ce kadai tsaye tsakar gidan duk sun shige ciki da yaransu, ta share idonta a hankali ta bude kofa xata shiga, a tsawace Hajiya Salaha tace “Ki shigo ki mana me? Maxa koma sai Alhaji ya dawo gidan nan, maxa fita kar in sumar dake annamimiya kawai” juyawa tayi da sauri ta bar wajen bayan ta rufe masu kofa ta nemi wani waje ta xauna ta daura kanta bisa kneels dinta, har aka kira Isha tana wajen ga sauro sai cixonta suke, Kawunta bai dawo gida ba sai wajen karfe goma, bayan ya gama parking xai shigo ciki ya ga kamar mutum a wajen ya haske waya, tana nan yanda take bacci ya dauketa a hakan, da mamaki yace “Ke!!” Firgit ta farka ta mike tsaye da sauri, yace “Me kike a nan” tana kallonsa da idonta da yyi bulu bulu yyi jajir, shatin hannun Hajiya Salaha a gefen fuskarta hankali tace “Aka ce in tsaya a waje” yace “Saboda me?” Tayi shiru bata ce komai ba, shiga gidan yyi ya tarar da su gaba daya da yaransu ana xaune parlor ana kallo ana shewa, duk suka fara cewa “Abba sannu da xuwa…” Bai bi ta kansu ba yace “Me wancan yarinyar take yi a waje?” Hajiya Maimuna ta tabe baki tace “Xaman jiran ka dawo” Hajiya Salaha ta kara da cewa “Tun kafin la’asar ina jin yarinyar can da ka gani ta fita muka dinga bin layi layi muna nemanta da makwabta ba ita ta dawo gidan nan ba sai dab da magrib, duk ta Daga mana hankali daxu gidan nan ba masaka tsinke” yace “Shine xa a bar ta xaune waje cikin sauro a jawo min abinda xai sa in kai ta asibiti?” Hajiya Salaha tace “Toh xan iya mata abinda raina ke raya min Alhaji shi yasa nace tayi ta xama a waje” yace “Toh kada warce ta sake turata waje war haka ko uban me tayi… Na gaya maku” juyawa yyi ya kalli Khadijah dake tsaye ta rakube a fusace yace “Xo nan” karasowa tayi da sauri ya wani hade rai yace “Ina kika je?” Hawaye ya cika idonta ta nuna masa waje da hannunta jikinta na rawa, fixgota yyi ya turata ciki yace “Gobe ki kara, saurayen da suka cije ki ma kadai sun isheki” daga haka ya wuce ciki yana cewa “Sai ku bata abincin idan xata ci idan kuma baxata ci ba ta kwana da yunwa” daki ya wuce, Khadijah ta xauna kasa jikin kujera bata yarda ta hada ido da su Hajiya dake ta 6alla mata harara ba, a wani kwanon da yyi tsatsa aka xuba mata tuwo da miyar kubewar da aka girka, ta jawo abincin a hankali tana kallonsa, miyar ta kai baki ta d’an yamutse fuska, ganin kallonta Hajiya maimuna take tayi saurin saita fuskarta, ta tsura ma TV ido tana kallo kamar yanda duk occupant din parlorn suka yi, ji tayi Hajiya Maimuna tace ma Hafsa taje ta dauke kwanon abincin ta kai kitchen, Khadijah bata damu ba don dama ba yunwa take ji ba, sai waje karfe sha daya da rabi kowa ya tafi makwancinsa ita ma ta kwanta a kan tabarmar da aka nuna mata ta dinga kwanciya a dakinsu Sajida wai katifar baxai dauke su su dukka ba. Bayan kwana biya Khadijah na xaune tsakar gida da yamma tana uban wanke wanken da su Hajiya suka tula mata, su kuma suna ciki da yaransu kasancewar ranar Friday ce bbu islamiyya, yi take kamar baxata yi ba tana turo baki an hanata kallo, wanda a kansa kusan kullum sai ta sha mazga amma ta ki hakura, ita dai tayi kallo, duk ta rame ta kanjale, kana ganinta kasan akwai yunwa sosai da wahala tare da ita, ga rashin sabon aiki, ba laifi yanxu tana d’an wanke plates din su fita sai dai ta kan fi awa biyu kan kwanukan wanke wanken, kayan jikinta kuwa yanda aka san ta shiga rafi tsabar jikewar da yake idan tana wanke wanken, yanxu an ma daina sa ta sharan gaba daya tsabar kawai bata iya ba sai dai wanke wanke da jan ruwa wani lkcn a waje idan bbu wuta, tun ranan da ta fita har yau bata sake fita ba sai dai idan an aiketa gun mai kanti ko kuma xata debi ruwa a er karamar bucket da take dauka, har yau bata sake cin abinci mai dadin gidan da taje ba, abincin gidan kawu daga taliya sai tuwo da shinkafa da wake da mai da yaji, gashi duk bata son su hakan yasa take tare da yunwa sosai, Hafsa ta fito ta jefa mata kudi tace “Khadijah wai Mama tace ki je gun mai kanti ki siyo sabulun wanki da Hypo leda biyu, sai ki siyo maggi mai tauraro na hamsin” Khadijah ta turo baki bata ce komai ba, tashi tayi bayan Hafsah ta wuce sanin Hajiya na iya lekowa taga ko ta wuce, ta shiga parlor Hajiya Salaha tace “Aiken fa” ta kalli kayan jikinta tace “Mama xan canxa kaya” dakuwa tayi mata tace fita Ki ban guri, shashasha sshe da gangan kike jike kayan wajen wanke wanke kenan kin san abinda ya kamata” juyawa tayi ta fita, ta sake kallon kayan dake a jike tun daga saman gwiwanta har kasa, gate ta nufa kanta sanye da hula don gaba daya Hijabs dinta yaran gidan sun gaje, tafiya ce me nisa xuwa gun mai kanti, tana tafe tana wasa da d’an karamin iccen hannunta, har ta wuce gidan da taje ta ci abinci idonta na kan gate din gidan amma ba daman shiga, tana isa gun mai kanti cikin aiken da aka mata maggi kawai ta tuna, gida ta koma da sauri ta shiga parlor tana kallon Hafsa kamr xata yi kuka tace “Me da me kika ce ma” Hajiya Salaha tayi wani murmushi ta na kallon kishiyarta tace “Me na fada maki” Hajiya Maimuna tace “Kin ji na maki musu? Ko an taba aikenta bata dawo tambayar me aka aiketa ba dama” Hajiya Salaha ta ce “Wllh Ubanki ya cuce rayuwar ki, kishiyar uwarki kuma kiri kiri ta nuna bata son ki tunda har ta sangarta ki haka ta lalata ki saboda ba ita ta haife ki ba, banda haka wannan xabgegiyar budurwa godai godai kullum aka aike ki sai kin dawo wai kin mance, sai shegen turancin iyayi…. ni dai wllh tunda yarinyar nan ta xo gidan nan nake fama da surutu abinda yaran da na haifa ma basu sa ni ba, Allah dai ya isa wllh” Hajiya maimuna ta tabe baki tace “Ke kika ga xa ki iya, ni kinga ina yi? Ai sai dai duka” Kabir ne ya sake nanata ma khadijah Aiken da aka mata ta fita da sauri tana maimaita abinda yace a ranta har ta isa gun mai kantin sannan ta fada masa, yana dariya yace “Ke yar fari ce ko?” Ta wara ido tace “I don’t understand” dariya yyi yace “Aa ni ba bature bane, don nema maki saukin kai wa da dawowa idan an aikeki kawai kice a dinga rubuta maki sakon a gida kinji” tace “Ohk then” muryar da taji yana cewa a bashi kati ya sa ta juyawa da sauri, suka hada ido ta washe fararen hakoranta tace “Good evening” daga sama har kasa ya kalleta yace “How you?” Ta langwabar da kai tace “I shud say fine” yana gyada kai yace “Good” karban card din da mai kantin ke mika masa yyi yace “Doguwa dake baki sa Hijab idan xa ki fito” a hankali tace “Bani da Hijab yanxu” bai ce komai ba yana loda card din kafin yace “Toh me yasa kika jika kayan ki” tace “Wanke wanke nake yi tun da rana” yace “Ina ne gidan ku?” Tace “Our home is 3 house’s away from u people’s” ya kalleta yace “Gidan Alhaji Jibril?” Ta gyada masa kai, yace “Ke yarinyarsa ce” ta girgixa kai a hankali, yace “Yaushe kika xo gidan!” Ta kalli sama kamar me naxari sannan tace “10 days ago” ya gyada kai bai ce 

PLS CLICK ON ADS

(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9740, ‘t’: ‘300 by 250’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());
komai ba, ta amshi ledan sakonta da canji tana kallonsa kafin tace komai yace “Ya sunanki?” Tace “Khadijah” yace “Good” a hankali tace “Ina son in xo in ci abinci gidan ku amma an hanani, kuma I can’t eat the food they are cooking, it’s just concoction” a hankali ta karashe maganar, yace “Me yasa aka hana ki?” Tace “Su mama sun ce xa su kashe ni idan na sake xuwa ko ina kuma ina jin tsoro” ya kalleta bai dai ce komai ba, ta matso kusa da shi a hankali tace “Ko xaka dinga kawo min abincin gidan ku da kanka?” Ya buda ido yace “Ina?” Tace “Gidanmu mana, sai in dinga boyewa a backyard ina ci” tana magana ne hawaye cike fararen idonta, jin yyi shiru ta ci gaba tace “I am always hungry….” Ya sauke idonsa daga kanta bai dai ce komai ba.

*Haske writers association*????

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button