Comment on YANCIN KI Page 41 to 50 by Anonymous

” hello my bby How are u doing ?
“Am fine dady .
“Ina momy’nki take ?
“gata a kusa dani tana kuka,Jimmmmm yayi da ransa sannan yace “okay bata wayar…..
nasreen ta miko mata wayar “momy dady yace nabaki..
Me’ad taki kallon inda take ballanatana ta amsa wayar hannunta ,”momy plz now ki amsa wayar dady’na.
Sam me’ad taki, ” ta amsa tace masa me byn cutar da yayi mata ?
“Me zatacewa mayaudarin irinsa?
“Mayaudari maci amanar kauna ……”Har abada wata kalma bazata sake shiga tsananinsu ba, kowa yaje yayi rayuwarsa ….
yana jin yadda nasreen ke mata nacin ta amsa wayar Amman taki , tswon minti biyar wayar na tafiya sannan nasreen ta meida wayar zuwa kunnenta tana sauke numfashi “dady……..
“taki amsa ko ya fad’i hkn Dan yasan abinda zata ce masa kenan ?
“Don’t worry bby, yanzu kuna ina, na dawo hospital doctor yace yayi discharging naki ,na dawo gida bangan bbynah ba,gashi nayi missing dinki ,I want to see ur beautiful face, tayi murmushin jin dadi sannan tace “ai daga hospital gidan grandpa muka wuce nan tashiga koro masa duk abinda ya faru akan idanunta ,fu’ad ya samu guri ya zauna yana mai runtse idanunsa yana jin wani irin zallar ‘bacin rai da tunda yazo duniya bai ta’ba jin irinsa ba, wani irin tafarfasa zuciyarsa ke masa “why me’ad ? Ya furta a raunane.
“Me yasa zata masa hk.? Ahankali ya hau sauke numfashi cike da takaicin dabbancin abinda me’ad tayi masa, ya d’auka iya shekarun da sukayi tare shi daita sun zama abu daya, sannan sun wuce wannan nevel din ,tazama shi shima yazama ita, sun chakud’e guri daya ta yadda duk runtsi duk wuya babu wanda zai ji kansu balle mahaifinta, daya fito ya nunawa duniya bayason zamansu tare, Sautin muryar nasreen dayaji cikin dodon kunnenshi ne yasa yayi saurin bud’e idanunsa “dady da gaske ne zaka auri aunty sajida da najma me aiki Dan kayiwa momy’na kishiya dasu?
Yayi shiru kawai ya kasa bata amsar tambayarta, sai ma d’aura hannunsa da yayi ya dafe goshinsa dashi yana shashshafawa ahankali ahankali ,while kirjinsa na bugawa da sauri sauri.
“daddy matukar da gaske zaka auresu ne ,plz change your mind, dan banason kayiwa mamana kishiya saboda banaso ganita cikin damuwa, saboda nima zan shiga cikin damuwa yanzu haka kirjina ciwo yake min dady tak’arasa mgnr kmr zatayi masa kuka …..
Muryarsa a matukar kasalance yace “bby kina bukatar kulawa wanda momynki ta kasa tsayawa ta baki, ni kuma amatsayin na mahaifi ba hurimina bane ,wannan hanyar kad’ai ce zatayi min maganin matsalata saboda nasan idan na auresu zasu kula dake shine dalilin….
” Amman ki za’bawa dady’ki mutun daya acikin auntynki sajida ko najma wanda kike son na aura ta zauna tare dake amatsayin second momy dinki, wace zata cigaba da kulawa dake da dady’nki..
“ni banason dukkansu ,ni banason kowa ni nafi son mummy’na kawai ……….
ya sake runtse idanunsa gam” yanzu kuna ina?
” zanzo na sameku na dawo daku gida, ta d’aga kanta tana duban yanayin gurin ta cikin mota, idanunta ya sauka akan wani green sambod da aka rubuta *main land bridge* Dan hk ta sanar masa a matukar firgice ya bud’e idanunsa ,gabadaya ya gigice ya kid’eme muryarsa na rawa yace “main land bridge?
“Yes dady shine abinda nagani ,yace “ki sa wayar a handafree.
Aiko take nasreen tayi abinda dadynta ya umarceta cikin d’aga murya yace”me’ad kina hauka ne, dazaki kai min yarinya har main land bridge?
“Wai meyasa kike son meida kanki wawiya ne akan yar kankanuwar matsala?
Tayi masa banza taki cewa dashi komai ,shi km ya dinga zuba mata bakaken maganganun ta inda yake fita bata nan yake fita ba still tana jinsa taki cewa komai, Dan idan tace zatayi mgn zagi ne zai fito daga cikin bakinta da hk tacigaba da sauraransa kawai take tana jin zallar ‘bacin rai na ratsata, hawaye na bin kuncinta ji take a duniya yagama tozartata, ya gama wulakanta da abinda yake son mata,ganin taki kulasa yasa ya sausauta muryarsa,
“Kiyi kokarin dawo min da yarinyata so that ke ki cigaba da zama agurin tunda abinda kika za’barwa kanki kenan .
yana gama fad’ar hk ya katse kiran,Wanda alokacin ita kuma tayiwa motarta key dan tasan Sarai zai iya zuwa ya samesu agurin tunda yaji inda suke.
me gadin gidansu takira taji ko fu’ad din na gida , ya tabbatar mata da yanzu ya fita, hasashenta ya tabbata kenan, zuwa zai yi ya amshi nasreen din ya barta da tarin bakinciki da damuwa, kai tsaye gidansu ta nufa, bata tsaya bata lokaci ba tashiga ta dibi abubuwanta datasan masu amfani ne gareta, dana yarinyarta ta kulle kofarta ta fito tashiga mota tabar gidan.
Yayinda fu’ad Yayi maya tafi sau hud’u akan main land bridge, ya hau ya sauko Amman bai ga alamun tsayuwar motarta ba ko alamun wata motar daban ba ,gashi yana kiran wayarta taki d’auka haka ya hakura ya koma gida yana jin zallar bacin rai yana shiga gidan jikinsa yabashi tazo gidan . Da sauri ya fito ya isa gurin me gadi yana kwalla masa kira ,me gadi ya k’araso ya tsaya agabansa “maman nasreen tazo ne byn fitata?
“Eh yalla’bai tazo bata ma dade sa fita ba wani irin takaici yaji kmr ya d’aukeshi da mari, a fusace ya juya ya komai cikin gida yana huci gabadaya ya rasa meke masa dadi ,hankalinsa ya sake tashi so yake yasoma neman inda najma take Amman bashi da natsuwar zuciya a kalla ya kusan minti goma tsaye yana tunanin mafuta ya duba agogo karfe karfe biyar ta kusan ciki” ina bai ga ta zama dole duk yadda zaayi sai yaga me’ad da nasreen tare da dawo dasu gida sake bazama yayi ya fito harbar gidan kallo daya zaka masa kasan baya cikin natsuwarsa yashiga motarsa aguje ya bar gidan.
*********
A bangaren mahaifiyar me’ad kuwa kuka take a tun fitar me’ad gidan ,taso kiran fu’ad Amman ta kasa saboda a yadda zuciyarta ke cike da ‘bacin rai zata iya gaggaya masa komai yazo bakinta ,abinda bazata so faruwarsa ba kenan atsakaninta da surinkinta ,me mutuntata da ganin kimarta, ita batace kar ya kare aure ba ,”amman meyasa sai sajida da najma?
Tasan zai auresu ne Dan kawai ya kuntatawa zuciyar mead dinta…
gidan yayi shiru kmr anyi mutuwa Dan koda suhailat ta dawo daga makaranta taji labarin abinda ya faru mutuwar tsaye tayi agurin, itama hankalinta yayi mugu mugun tashi..
ta dinga mamakin cin amana irin na sajida a ganinta har gara auren najma akanta…..
Bangaren me’ad kuwa yawo ta dingayi acikin gari, daga wannan titi zuwa wancan titi,tarasa inda zata taji sanyi aranta ,tayi tunanin zuwa dangin momy’nta Amman sai taga kmr zata tonawa kanta asiri ne, a yanzu ta d’auki darasi me girma a zamanta da sajida, bazata sake yarda da kowa ba arayuwarta ,zata koyi rike sirrikanta ,zata bawar cikinta damuwarta bazata sake sharing secret dinta da kowa ba bayan mahaifiyarta, itama Dan tasan bazata gayawa duniya bane ko ha’intarta sai dai ta d’aurata bisa turba .daga karshe zuciyarta ta bata shawarar takama hotel kawai ta cigaba da rayuwarta har zuwa sanda mahaifinta zai sauko ya amsheta ,bazatayi fushi dashi ba ,haka zalika bazata gaji da rokonsa ya yafe mata ba, har sanda zai furta ya yafe mata.
Dan hk Kai tsaye wani had’ad’en hotel ta nufa me suna city hotel, cikin Dan kankanin lokaci ta isa kawataccen hotel din Wanda hotel ne ,na isasu ta d’aki ,daya daga cikin mai’aikatan hotel din yayi gaba rike da key’n d’akin ita kuma tabiyosa abayan rike da hannun nasreen ,byn ya bud’e mata d’akin ta mika masa key’n motarta domin shigo mata da kayanta, ya amsa juya cikin sauri, suka shiga ta meida murfin kofar ta rufe .