DAMA TA BIYU HAUSA NOVEL

On the other side Kuma fajz na zuwa kofar gidan su Amira ta fita daga cikin Mota ya kwankwasa gate din Maigadi ya bude, gaisawa sukayi ya saka hannu cikin aljihunshi ya fiddo Yan dari biyar biyar bundle guda ya mikawa mutumin wato Maigadi, idanuwa tsohon ya zaro Yana kallon kudin
“Tambaya nakeson maka…nayi maka alkawarin babu Wanda zai San ka fada min komai…Kuma in har na samu bayanin da nake son sani Zan Karo maka irin wannan…” Yafada Yana nuna mashi kudin hannunshi,
“Allah yasa na sani…” Tsohon ya fada Yana tura kudin aljihunshi.
Alhamdullilah
3/13/21, 7:58 AM – Ummi Tandama: 60
Idanuwa faiz ya lumshe as he knows if har ka fiya bincike at Long last you will be the one to be hurt, zaka Sha wahala ne a banza don yawan bincike Haram ne, Amma ya zame mashi dole
“Ina sauraron ka…” Mai gadi ya fada mashi don shima Yana son ya San abinda yasa wannan bawan Allah Zan bashi wannan makudan kudin don zai tambayeshi, ajiyan zuciya faiz ya saki before yace
“Dan Allah…Ina son sanin wani abu game da Yar gidan Nan ne…Ina rokan ka Kar ka boye min komai…Kuma duk abunda ka fada min a tsakanin mu ne kawai babu Mai ji…” Fajz ya fada mashi
“Toufa…babu damuwa kayi tambayar ka…” Mutumin ya fada mashi
“Dan Allah wannan Yaron Nasir…” Yanda Mai gadi yayi da face yasa faiz ya Dan dakata da maganr shi, Yana da wani irin blank look a face dinshi, irin Bai taba jin sunanshi ba
“Waye Nasir…Anya da akwai Nasir gidan Nan?…” Mai gadi ya fadawa faiz
“Wannan karamin yaron….”
“Oh na gane…na gane ban San sunanshi ba…shi yasa…kawai Ina ganinshi ne…” Ya amsa mashi
‘”ok…pls yaron waye….wacece mamanshi.. ” faiz ya tambayeshi Cikin matsiyacin faduwar gaba, bands tsoron gaskiya babu abinda yake, he seek for the truth now he is scared of the truth,maigadi Shuru yayi kaman Yana tunanin wani abu sai Bayan minti guda yace
“A magnar gaskiya wannan Yaron….tou…” Sai Kuma yayi Shuru, faiz da hannunshi ke rawa tun Bai San abinda zaice ba hannu ya saka cikin aljihunshi ya sake dauko wani kudin ya Mika Mashi sai gashi ya Fara cewa
“Wannan yaron dan Amira ne…” Faiz jingina yyai da gate din for support, this is how it is,now he knows the truth and he is broken to hear it, I wonder what happened to kou kina da yaro I will still marry you,
“Ba Wai nagan ita ya Haifeshi ba…Amma Ina da yakini itace…”
“Toufa…ya zaayi kace Haka…bayan…nasan aure tayi…kou dai baka Dade gjdan Nan ba…”faiz ya fada sounding so calm,
“Ai tun suna Yara nake aiki gidan Nan…Amira Bata taba aure ba…. kaddara ya fada Mata…don sai da ta kusa shekara hudu Bata fita…nasan ranar data haifi wannan Yaron…don ihunta sai da ya cika gidan Kuma baa kaita asibiti…” Mutumin Bai karasa ba faiz that abinda yaji is worst than what he expected cewa Yayi
“Oh my God….Bata…taba… aure…ba…” Ya fada kaman numfashi zai yanke mashi,
“Eh Bata taba ba….”
“Subhanallah…”faiz da yaji wani irin zafi ya keto mashi ya fada Yana juyawa, he didn’t want to hear more, he have heard enough,
“Inna lillahi waina ilaihi rajiun…” Was abinda ya fada, Yana tafiya zuwa wajen motar shi, he is feeling so dizzy, he feels so broken, Maigadi tsayawa yayi Yana kallon shi, yanda yake tafiya ya nuna Yana cikin damuwa sosai, har ya Kai wajen motarshi ya rike handle din ya tsaya, he feels so hot inside that he have to pour tears, shi Vai ma San he is crying ba sai da yaji dumin hawaye a face Dinshi
“Ba aure….with a child.. with…all the innocent face.. subhanallah… Ya sake fada Yana tsaye wajen, now it’s kind of clear, hakan yasa mama ahmed ta hanashi aurenta, shima yasan in shi yana iya aurenta…his family especially his father will never allow it,… sannan siblings Dinshi especially Maryam will not allow it, she’s someone data iya Shiga ta fita ta Bata Abu muddin baiyi Mata ba,. Ahankali ya juya ya sake takawa zuwa wajen Maigadi dake tsaye bakin gate Yana kallonshi, hannu yasa ya goge face dinshi Yana cewa
“Dan Allah ka San…Habib…” Ya tambayeshi,
“Sosai…ai Habib Dan gidan Nan ne…tare suka tashj da su ismail…” Mai gadi ya fada mashi,
“Ya suke…dashi pls…” Faiz ya sake asking Yana kokarin controlling kanshi sosai
“Kakanninsu Daya…Amma shi tamkar San gida yake…'” maigadi ya fada mashi
“Bastard…” Fajz ya fada Yana juyawa da sauri, he knows Dole Habib is responsible for the pregnancy,he is the father of that child, now he knows why ahmed ya dinga balai Daya gan Habib, sannan yasan family Basu San abinda ya faru ba, lokacin that Ahmed was busy Yana karyar sabida shi ta kusa commiting suicide it was all because of Habib, he is the reason she cries always, he is the main reason of her pain shi yasa dayace Habib is here hankalin ta ya mugun tashi, now he knows, Amma why Bata Fadi a gida ba don yasan inda ta Fadi a gjda an San abinda ya faru da Babu yanda zaayi Habib ya samu guts din zuwa wannan bikin, cikin Motar shi ta koma ya zauna Yana imagining abubuwa, wato what he is having with bintu Habib have had it with Amira, who knows how many times, sukayi sex sai Kuma ya Fara tunanin what raping dinta yayi,bayan ta bashi yardan ta, Bayan ta yarda dashi ta saki jiki dashi, so Amira ta San na Miji , now he knows why Taki sakin jikinta da suka je Malaysia, she knows how dangerous men can be,
“Allah ya Isa…” Fajz ya fada as he thinks of what might happen between Amira and Habib,Bai taba jin he needs somewhere to cry ba kaman yau, he wants to cry and cry har sai yaji sauki a ranshi, in har baiyi kuka ba bazai ji Dama dama ba, he is going so insane tada motar yayi Yana aduar Allah ya kaishi gida lafiya, Bai San Yana da yawab hawaye ba sai yau don the more he cleans his face the more wasu na rushing out, now he knows why she’s so stubborn, she have seen it all, Yana tuki Yana kuka, instead ya nufi gidanshi say ya nufi gidan iyayen shi, she’s the only one he will lay on her legs and cry to his Satisfaction.
Amira Kam Bata kalleshi ba ta sake cewa
“The seat is taken…with due respect ka tashi..” ta fada face dinta babu walwala at all, Habib was just staring at her Yana mamakin yanda akayi wannan Yarinyar da kou kallon idanuwan batayi ta Zama so bossy, she’s so elegant and classy yaga Alaman tana Kashewa jikinta kudin ta don her skin glows like crazy, fadin yanda ta hadu is a waste of time, he is just looking at her mouth as she talks with total control, Yana son ya gan reaction dinta when Shee sees his face, he believes it won’t be difficult to lure her heart back tunda yasan he is her first, yasan shine na farko when it comes to sex and love, yasan he is unreplaceable tunda ya bar Mata tabon da har ta mutu Bai taba goguwa, yasan he is the only person that deserves her, job shuru Wanda ya zauna baice Komai ba yasa ta daga Kanta ahankali, duk cikin mutanen wajen babu Kai kallon inda suke like ahmed da tunda yaga Habib ya nufi wajen ya maida duj attention dinshi wajsn, he was just looking at them with a boiling heart, kawai Yana tunanin Anya zaa samu Dan duniya irin Habib, ya rasa Gane irinshi, wato kayiwa yarinya abu Kuma kou kunya or remorse bakaji ba ka sake nuna kanka a inda take, he should be glad Babu Wanda ya sani don family Dinsu ba daya baya ba wajsn cin uban yara, rufa mashi asiri datayi Bai isheshi ba, Amira na Kallon shi tava it’s Habib.
“Hi beauty…” Ya fada Mata with a smile Kan face dinshi, Amira was thinking tana mafarki don he is the last person she was expecting to see at the moment, idanuwa ta zaro tare da Dora hannu Kan chest dinta,
“Surprise to see me?…” Ya fada yana kallon ta, Yana kallon yanda ta Zama so shocked to see me
“Haba baby… you know am alive so ya Zama Dole mu hadu…”ya sake fadawa Amira da heart dinta ke skipping, kawai seeing her number one enemy sitting right in front of her is something else, babu Wanda sai Gane yanda take ji sai Wanda yasan halin da take ciki, kawai kayi imagining halin da take ciki, she’s so looking at him without blinking, shima Habib kallonta kawai yake
“Kiyi hakuri…” Ai Yana cewa kiyi hakuri Bata San sanda ta dauki kwalban five alive juice dake gabanta ta buga mashi a baki ba, she hit him so hard that duk waynada ke wajen sai da suka juyo gareta yayinda Habib ya dafe bakinshi, da sauri Ahmed ya tashi ya yo wajen da Sauri, Idanuwan Amira was still tough staring at him ya dafe bakinshi ta hannunshi jini ya fara zuba, kwalban fashewa yayi a bakinshi, she cut his mouth in different places, na kusa sai magana suke suna lafiya, Ahmad na zuwa wajen yace
“Tashi…mu fita…” Habib was so much in pain don he was busy saying rubbish da Bai gan sanda tayi gripping kwalban ba, zafin yasa ya rasa inda kanshi yake, it’s like an dauki Abu an soka bmashi unexpectedly, the pain is so unbearable da ya rike bakinshi ya dafe table tare da lumshe idanuwa gam Yana jin wani avu na zuba hannunshi, Amira was Still holding the bottle, abinda yasa ba kowa ba wajsn ya San abinda ke faruwa ba saboda an Fara kiddi, Amma Still wayanda ke wajen was looking at them, hannunshi da ke Kan table Amira ta sake daga kwalban ta shaka mashi, kou ahmed dake tsaye kanta Yana fada Mata ta Tashi was surprised that he didn’t see her move she’s moving faster than anyone, wani irin Kara Habib ya saki ga kwalban a hannunshi, da sauri ahmed ya fixgeta daga inda take zaune, duk hankalin mutane ya dawo kansu, Amira was just going Insane already.
“See another word…” Ta fada tana fixge hannunta daga na ahmed dake kokarin fiddata saga wajen, hankalin mutane High table ne yazo garessu sukaga Amira dake fixge fixge sai, da sauri hajiya ta tashi cikin tashin hankali tare da wasu manya mutane dake nesa da wajen,
“Wallahi sai na kasheka. ” Amira tafada with a very dry and tough eyes while Habib na zaune Yana ihu sabida azaba, duk wayanda ke zaune wajen Mikewa sukayi.
“<Have you gone insane ..kina son ruining ranar nazifa…” Ahmed yayi whispering cikin kunnenta,,
“Yaya… wallahi in ba kashe shi nayi ba hankalina Bai taba kwanciya…kana ganin ha rufa Maja asiri don wani avu ne?, I hide it because I want to kill you myself.. ” ta fada yayinda ahmed ke janta waje da karfi, Yayar habib ce tazo da gudu tana ganin danuwanta cikin jini ta saki Ihu tana Kiran zata
“kashe Mani Dan uwa…the only brother I have…” Ta fada tana ihu sosai, da kyar Ahmed ya ja Amira Wajen ita Kuma ta haukace tana son komawa, she wants this to end today, Sam ta mance inda take ta amnce abinda akeyi yau, all she wants is revenge, she wants to see the cause of her pain dead, she wants to see him in his blood, hajiya da alhaji suna zuwa wajen Habib Suka saki salati, duk babu wnada yayi kokarin cire mashi kwalban hannunshi, Ismail na Ganin abinda ya faru ya fita waje da gudu ba don komai ba sai don ya hukunta Amira don ya lura she’s going crazy, Yana zuwa yaga Amira Tana fadin
“Wallahi kou ba Nan ba sai na kasheshi…sai na Zama ajalinshi…” Hannu Ismail ya daga zai bigeta Ahmed yayi sauurin riketa Yana cewa
“Don’t you dare…” Ya fada Yana tareta yayinda wasu family Suka fito waje, wasu cousins Suka rike Habib aka fita dashi yayinda MC ya cigaban da abinda yake Amma hankalin nazifa ya mugun tashi, she wants to know what is happening gashi Bata iya tashi daga inda take,duk kunya take ji her sister is making a scene a wajen reception dinta. Mutane sai tanbayar what happened suke, duk mutanen da suka fita Bai Hana Amira maimaita abinda take cewa ba Yana ganin an fito da Habib that did expect this From this gentle girl ba ya tsorata sosai, duk Wanda yayi kokarin dukan Amira sai ahmed ya Hana ya dinga Cewa.
“Baku San abinda ya Faru ba…” Habib Kam yayi Dana sanin zuwanshi Nan don baiyi tunanin it’s going to happen Haka ba, Yana tunanin he will apologize peaceful, then she will say in har kana son in yafe maka ka fadawa kowa Kaine kayu min ciki sannan ka aureni, Bai San it’s this serious ba, ahmed ne ya Kama Amira ya girgiza ta da karfi Yana cewa.
“This is not the right place ..” Bai Karasa ba Amira da take komawa kaman mahaukaciya tace
“Duk inda San hadu dashi us the right place!!!” Ta fada cikin ihu
“He decieved me… ruined my life….yayi min ciki ya barni dashi….” Wannan maganar da take is very serious and kowa yayi Shuru lokaci guda kaman Babu kowa wajen, hajiya data fito neman faduwa tayi yayinda ismail da hankalin shi ya mugun tashi ya riketa,
“Yaci amanata….I endure all pain kawia don ya dawo ya aureni…Amma sai kace ni ban dace da Kai ba…” Ta fada tana fashewa da kuka, ahmed na rike da Amira dake magana tana kuka, cousin brothers dinta dake rike da Habib Saurin sakinshi Sukayi suna barinshi shi kadai cikin matsanacin wahala as rigar jikinshi ya cike da jini saboda Wanda ke zuba daga bakinshi is much Alaman cut dake bakinshi is much, da sauri sister din Habib dake kuka ta Fara cewa
“Wannan wane irin sharri ne…'”
“Kina cewa sharri nayi mashi sai na hallaka ki.. ” Amira ta fada sounding so crazy,
“Yaisa…kin Fadi abinda ke ranki…now muje in kaiki gida…” Ahmed ya fada Yana kallon family Dinsu dake wajen da duk sukayi shuru, waje Ismail ya samu ya ajiye mum dinshi sannan ya dawo ga Habib da bakinshi ya kumbura sosai Yana cewa.
“Kai da gaske take???” Ya tambayeshi cikin wani irin murya dake nuna he is going to kill him if abimda Amira ta fada is real,
“Tell me!!!” Ya daka mashi tsawa,
“Leave him… somebody should take him to the hospital…” Alhaji Muhammad dake tsaye a Bakin kofar hall din ya fada tare da komawa ciki, duk juyawa sukayi zasu koma ciki babu Wanda yayi yunkurin taimakawa Habib don abinda Amira ta fada ya mugun shocking dinsu,
“Tir… butulu kawai…” Inji Daya daga cikin family Dinsu, da kyar aka samu Daya daga cikinsu ya saka Habib a motar shi bayan Amira da ahmed sun bar wajen, it’s a good thing mum dinshi Bata da lafiya Bata zo bikin ba don yasan inda tana Nan he won’t be free Haka, hajiya na zaune tayi tagumi ta rasa inda zata saka kanta, gashi she can’t cry now,
“Yaya can you imagine…he is calling me beauty…Wai baby…Wai he is sorry…Allah yasa he swallowed some of his tooth…” Ta fada cikin farin ciki as ta mance abinda ya sakata farin ciki irin wannan, seeing him bleed gives her so much joy, she wants more if his bleeding, tana son ta ganshi kwance cikin jini, murmushi kawai ahmed yayi ya kalleta,
“Am so happy kowa ya San abinda yayi min…I even wonder why I hide it in the first place…” Ta fada cikin farin ciki
“Yaya…kawai ka maidani reception din…am ok…am so ok right now…I have never been ok like now.. ” ta fada tana Dariya, murmushi ahmed yayi ya kalleta
“Aa…kawai muje gida…”
” Pls take me back…” Ta fada sounding very serious,
“Aa…muje gida…” Ya fada Mata, nace mashj tayi Kan ya maidata, kawai Sai yace
“Yanzun dai muje gida ki sake Kaya…yanda bazaayi Saurin Gane kece Kika fasawa Mutum Baki ba…Kar a dinga maki kallon Yar daba. ” Ya fada Yana dariya, yanda suke Hira sai ka ranste ba Amira bace, wato ta Dan huce takaici ta samu sukuni.