DOCTOR HAJAR COMPLETE HAUSA NOVEL

Saida ,Dr Samir ya d’anyi jim kad’an sannan yace .
“Ciwo ne Junaid bayan tafiya na Turkey da kwana hud’u na kwanta rashin lfy da naje asibiti .
Doc…ya dubani sosai ya kuma gano cutar Cancer d’in da nake mafa dashi ,wanda ni ban sanar dashi ba.
Yace ina da wata d’aya ‘anan gaba idan har ba’a cire kidney d’ina ba tow zan iya rasa raina.
Yace duk kidney d’ina sun lalace saka makon ciwan dayake jikina ,
Bani da kowa da ze iya magan cemin wannan damuwar sai Ummi na , kuma itama kedney d’aya gareta .
Har idan Ummi tasan meke faruwa dani zata iya sadaukar da rayuwan ta sabo dani, kuma ni bazan so hakan ba Junaid shiyasa kawai kaga na bar komai ku….”
Cikin b’acin rai Captian ya tsaida shi ,idanuwanshi sunyi jazur alamun b’acin rai .
“Me matsayin abotar mu Samir ,da zaka dinga tunanin baka da kowa mud’in kenan baka d’aukemu yan uwan kaba kenan?
Samir ina jinka ,kamar d’an uwana kuma jinini!!
Babu abinda bazan iyayi makaba ‘a rayuwa matsawar wanda nasan zan iyayi ne.
Idan har ka d’aukeni d’an uwanka ba ‘abokin kaba, ka yarda zan baka ,kidney d’ina guda ,d’aya matsawar zesa ka rayu”.
Daro ido Dr Samir yayi ,yanajin wani dad’i cikin zuciyar shi ,da irin karamcin da ,Junaid yayi mishi.
Yasan babu ,abinda Captian bazai yi masa shiba ‘arayu don yaga ya samu lfy , Amman idan har ya bari aka cire kodar Junaid tow ya tabbata, yaso kanshi da yawa.
Hawan da tun d’azu suka ciko idon shi ya barsu ,suka fara fita.
Murmushi yayi wanda iya kanshi fatar baki ne yace.
“Junaid nagode ,da karamci nagode bani da ‘abunda zance maka dayafi haka,
Amman kayi hak’uri bazan iya bari a cire k’odar kaba idan ,nayi haka naso kaina da yawa.
Mutuwa bata salama koda anyi mun bashe ze hana ,na mutuba idan har kwanana ya k’are ,
Junaid yanda ,nakeji yanzu ya wuce kwatance ina ganin mutuwa ita kad’ai ce hutu a gareni.
Shine k’arshen k’addara ta , Allah ya nuna min jarabobi da, dama ‘a rayuwa ta, Hakan yana ,nuna shine k’adaddara ta,
Rubutu ne wanda ‘akayi kamar akan dutse wanda baze tab’a gogewa ba sai dai , ya wuce Amman tarihin sa baze wuce ba har abada”
A wannan lokacin Captian kasa jurewa yayi ,wasu Zafafan hawaye ,yaji sun zubo mishi.
Dafa kafad’ar Dr Samir yayi zuciyar shi na k’una yace.
“Idan har baka yarda ba Samir nasan matsayina ‘a gurin ka kuma……..”
Saurin katsashi Samir yayi , ya mik’e ya tako har inda Junaid yake ya tsuguna gaban shi.
“Na yarda ‘Abokina ,nagode da wannan karamcin dakayi mun Allah ya saka maka da mafificin Alkairi.
Samun aboki ‘irinka sai an tona Junaid ba kowa ze iya, yimun abunda kamun ba?”
Murmushi Captian yayi ,yace.
“Is ok babu god’iya tsakanina daikai Ana tare ,tashi mu koma ‘asibiti”.
Babu musu ,Samir ya tashi suka tafi
Tun jiya takejin bugun zuciya ta rasa dalilin hakan , kawai tana tunanin akwai abubuwan da zasu faru da ita cikin kwanakin .
Tun safe data, tashi bataji komai ba, babu yanda Khadee batayi da ita, taci abinci ba ‘Amman tace ta k’oshi bata jin cin komai a ranar.
Haka ,Khadee ta hak’ura ta rabu da ita.
K’arfe tak’as da kusan rabi Hajar ta shirya cikin wani daguwan riga na material ruwan madara, da zanen fulawa ruwan ganye ,
Ba tayi kwaliya ba mai kawai ta shafa , tad’an goga hoda ,ta yane kanta da wani mayafi ruwan ganye ,
Duk ,da rashin kwaliyan dake fuskar ta be hana kenta fitowa ba.
“Khadee kiyi sauri mutafi pls kinga ina so na biya hospital ,akwai abunda zan d’auka ‘a office d’ina “.
Kadee ,dake jikin mirro tana kwaliya tace.
“Sorry na gama barin saka, kaya ‘Amarsu “.
Hajar batace da ita komai ba sai murmushi data saki ,har yanzu tanajin bugun zuciyar ta me ,makon ya ragu k’aruwa ma yayi..
DIJA_WAZIRI
[18/12 7:33 pm] Dija Waziri: ????????????????????
DR HAJAR????????
????????????????
Chapter 41
Suna cikin mota Hajar tace wa Khadee.
“Nifa yau tunda natashi ,nakejin ,jikina babu dad’i Khadee.
Sai bugun zuciya da fad’uwar gaba nakeji ,sai ,ina tunanin akwai abunda ke shirin faruwa dani”.
Khadee dake tuk’i tace.
“Kiyi ta innalilahi insha ‘Allah babu ,abinda ze faru dake”.
Yanda Khadee ta fad’a hakan tayi tayi har suka k’arasa hospital.
Sai dai suna shiga taji bugun zuciyar nata ,na k’aruwa da fad’uwar gaba, Addu’a take tayi har ta k’arasa ciki.
“Hajjo barin shiga office dina zan ,zo na sameki”.
Cewar Khadee
Dak’er Hajar ta iya ce mata .
“Don Allah kar ki jima Khadee kinga bamu da isashen lokaci”
D’aga mata gira kawai Khadee tayi ,ta wuce ,
Itama Office d’inta ,ta nufa da mamaki taga Captian ,na tahowa hanun shi d’auke da ledan magani da ruwa ,shi ko kula da ita beyi ba har zai wuce tayi saurin tsaida shi da fad’in.
“Captian lfy na ganka ‘a nan waye ba lfy baka fad’a mun ba?”.
Sai lokacin ya juyo ,ya kalleta da fara’a.
Gani tayi ,ya k’ara kyau da haske hancin sa ya k’ara tsayi .
“Hajjo sanun ki ,kinyi kyau “.
Ya fad’a yana murmushi.
“Tnx me kake anan ?”.
Ta tambaya fuskar ta babu fara’a.
“Wlh k’anin Dr Samir ne yayi hatsari har dashi cin wainda sukayi hatsrin jirgin samman”
Magan ganun Captian ,ne suka fara yawo a kwanyar kanta dama Dr samir yana da k’ani ?.
Tambayar da takeyi wa kanta kenan a fili kuma tace.
“Allah sarki ae daka ,kira kagaya mun, damur Doc…ae tamuce duka, kodon mutuncin sa.
Bari idan ,nafito daga office zan shigo na duba shi “.
“Ok babu damuwa muna room 15”.
Yana gama fad’ar haka ya wuce ,
Itama office d’in ta shiga tare da tunanuka bar katai.
Abunda ta zo daniyar d’auka shi kawai ta d’auka ta fice daga office din don sauri takeyi,
Dakin da su Dr Samir ke ciki ta nufa dede kofar dakin taji fad’uwar da gabanta yake, ya sake tsanta ,taji wani ‘irin ciwan kai da bata, tab’aji ba , subhanallah kawai take ta furtawa har ta shiga d’akin.
A zaune ta samu ,Ummi kan darduma tana jan cerbi ga dukkan alamu idar ,da sallah tayi gefen ta Dr Samir ne ya kifar da kanshi ,cen gefe guda kuma Captian ,ne zaune , bata kalli gadon da ‘akram ke ,kwance akaiba ba.
“Asalamu alaikum “
Shine abunda ta furta, gabaki d’aya hankalinsu ya koma, kan ta su duka saku ‘amsa da
“wa’alaikum salam”.
K’ara sawa tayi ,inda Ummi ke zaune ta durk’usa.
“Ina wuni Ummi yame jiki?”.
Hajar ta, tambaya
Ummi da fara’a tace.
“Lfy qlau jiki da sauk’i ya shirye shiryen biki ?”.
Akunyace ta amsa da.lfy qlau ,sai alokacin ta kali Dr Samir suka gaisa ta, tambayeshi me jiki sannan ta maida ,duban ta kan Akram.
Wani fargaba da tashin hankali taji na ruskar ta, lokaci guda taji komai ya tsaya ,mata wani ,irin dokawa taji zuciyar ta, tayi.
Ko a mafarki bazata ,tab’a mancewa da wannan fuskar ba, ta kasa gasgata shid’inne kuwa gaban ta yau rana tsaka.
K’afafun ta, taji sun fara rawa lokaci guda taji zuciyar ta na wani ,irin dokawa.
Kallon Dr Samir tayi ,tana son yi mishi magana, yayin da take nuna ‘Akram da ,d’an yatsan ta sai dai kalma ko d’aya ta kasa fita daga bakin ta.
Lokaci guda taji wani jiri na d’ibar ta, lu ta ,tafi zata fad’i Junaid yayi saurin rik’ota yana .
“Lfy Hajjo” .
Sai lokacin Dr Samir yayi saurin tashi daga inda yake zaune ,han kalin shi a mugun tashe ,
Ummi ,ma ,mik’ewa tayi, tayi kan Hajar tana jijiga ta.
Da Sauri Captian ya fita kiran Doc… Yana fita kuwa yaci kara da Khadee, hankali a tashe yace.
“Khadee pls muje ki taimake mu Hajjo ta fad’i “.
Wani yawu me d’aci Khadee ta had’iya cikin tashin Hankali tace