NOVELSUncategorized

YAR SADAKA 11&12

???????? *’YAR SADAKA..*????????
*STORY & WRITING BY…*
         *BY*
*MOMN SULTAN*
*DEDICATED TO…..*
*MMN AMATULLAH*



*SPECIAL GIFT TO…*
*HAJJA FATI…*



1⃣1⃣&1⃣2⃣


Ashe Baka da kirki mashkur,mahaifiyar tamu kakesan kashewa” Anya ko kanasan albarka a karatun naka”
Aunty me kuma nayi,uwarka kayi Dan bantan ubanka,, mashkur ni kake tambaya abinda kayi Dan qaniyanka???
Sanin halin aunty ladeefah da fada yasashi cewa ah ah,,Amma aunty” Amma me Ka rufemin Baki, ko kanaso kagayamin karatunka da zuwa wannan mugun kauyen yafi mummy daraja,,dasauri ya Shiga girgiza Kai kama tana kallanshi…
Au rainin hankalin naka harya Kai ina magana kayimin shiru”
Haba aunty bafa Nina Kai kaina wannan rigar ba,kaini akayi kuma wallahi bantafi ba Saida Mummy ta amince yafada cikin sanyin murya.
To yanzu tace bataso Dan haka Ka tattara kayanka Ka dawo kafin nazo har garin naci maka” 

Amma aunty kinsan ko rabi banyi a aikin nan ba,, sai dagamin hankali kuke”inye mashkur nikake gayama haka,,ba laifinka bane laifin mummy ne datake daure maka gindi”
Kiyi hakuri aunty amma”Amma me to wallahi Ka sani a yau nakeso Ka dawo gida kafin gobe, Nima a gobe Zan zo qasar nida yaya saika gayamana dalilin dayasa kakesan dorawa uwarmu hawan jini??

Aunty yanzu yamma yayi bazan iya tafiyan dare ba,,kaika sani nidai magayama karka Bari mu riga zuwa qasar Dan jirgin asuba zamu hau..!  Shiru yayi Yana sauraranta batare daya iya magana ba..

Cigaba da magana aunty ladeefah tayi tana cewa, Banda shashanci irin naka mashkur kafi kowa Sanin halin mummy tinda Kai kake zaune da ita Amma Ka take Sanin Ka tafi gurin da tafi tsana a zuciyanta” kana kallo tin muna yara mummy batasan zuwa kauye balle harta rabi Fulani,,kodan lokacin bakada wayo…

Zuciyarsa na quna tare da tilin Dana Sanin zuwanshi wannan kauye yace aunty kiyi Insha Allahu goben Zan zo kafin kuzo,,ni inaga dakun hakura da zuwa nizan ba Mummy hakuri..

Bazamu fasa zuwa ba,,ok kanaso kaje ta lallabeta taqi nuna damuwanta akai bayan Ka dagamata hankali muma Ka dagamana”cikin sanyin jiki da tinanin irin tashin hankalin daze tarar a gida yace shikenan aunty..kit ta katse Kiran tanajan dogon tsaki tare da cewa yaro besan komai ba sai bin talakawa kaskantantu wulaqantantu wadanda Basu San komai ba sai yawo a jeji da shanaye..


Tinda mashkur ya Gama waya ya zauna a gindin bishiyar dafe da kansa Yana ji kama ze fado qasa sabida sarawan dayake masa” dakyar ya iya daga qafafunsa yafara tafiya Yana hada hanya harya Kai dakinsu” 
Kan katifanshi ya kwanta hannunsa dafe da kansa yanajin zuciyarsa na azalzalasa akan abubuwa da dama,,rintse idonsa yayi yanasan bacci ya daukeshi sedai abin ya gagara Dan a yadda yakeji bacci baze taba daukansa duk kuwa da irin sunan dayayi gurin satar mutane,,runtse Ido yayi Yana hango kyankyawar fuskar nijlah,, qirjinta yake hanqe yaga Babu komai a jikinta danko qirgan danqi Bata fara ba,,sedai nijlah akwai iyaye dasan ado da kwalliya Duk da Bata da kayan kirki Amma kullum saita chanza Koda Bata samu sabulun wanki ba,,sosai ya zurfafa cikin tinanin yarinyar tare da yaban halayenta,,abu daya yakeji tare da ita shine rigima,,yasani Idan tafara rigima bataji Bata gani saita kwana tana kuka” oh Allah ya fada a Fili,,yanzu Idan nijlah tafara wannan kukan yaya zeyi da ita,,wanne irin mataki mummy zata dauka akansu gaba daya,,Rasa amsa dayayine yasashi saurin Tashi ya fita.
Alwala ya daura nan ya dawo Daki ya shinfida Sallaya..
Sallah yayi Har raka’a biyu nan ya dungura kanshi a qasa Yana neman dauki a gurin Allah..


Bayan an fidda Alhaji  ya’u,,Liman yafara Magana kama haka” Malam inaga yakamata mu qarasa gida Domin ayiwa yakumbo bayanin abinda Ke faruwa tare da gayamata wannan aurin aure..

Hakane Liman sedai Ina tsoran yadda yakumbo zata riski wannan labari,,bansan yadda zata dauki rabuwa da nijlah ba,,Malam yaqare maganar da cikin kuka Wanda baza’a kirashi Na bakin ciki ba,,Sai Dai Ko farin ciki..
Haba Malam yaya da kuka,kaida zakayi farin ciki gashi yarinya tayi dacen Miji bame San hayaniya ba..

Kwarai dagaske cewan Nasir,, Ai Liman Idan kaga mashkur yayi Magana to ba qaramin Abu akeyi ba,,bashida San hayaniya,wallahi tinda muka taso da mashkur bantaba ganin abokin fadan Saba kowa yabansa yake,,shiyasa nazabawa nijlah Shi Duk da nasan wasu zasuyi tambaya Shin Ni meya hanani aurenta nasa abokina yayi?
Nan mutane sukafara surutu Suna fito da tambayan dankuwa sunga lokacin da Nasir Ke gayawa mashkur yazo ya taimaki nijlah” wasu nacewa shimeya hanashi taimakonta indai Dan Allah take..

Kuyi hakuri yanzu Zan Baku amsar tambayoyinku” wallahi Ni Nasir Zan Iya auren nijlah Duk da Babu shaguwa tsakanina da ita Kamar yadda ta Shaqu Na mashkur,,sedai banqi amsar aurenta sabida komai ba sedai, Ni inada zafi Bani da rigima sannan abu kadan Ke batamin Rai nayita jibgar yara,,Idan Ko sa’anane Daga lokacin Ina Iya Dena abota dashi..
Nan ya numfasa yace mashkur kadai Ke Iya Zama Dani sabida miskilanci irin nashi da hakuri Wanda Koda nayi Abu sedai yace Allah ya shiryeka koya girgiza kai,,Idan Ko fada Na tsokalo shike Bada hakuri Har adawo daidai.
Natabbata wannan dalili nawa ya isa kugane nijlah ba sa’ar aurena bace Duba da yanayin rigimarta ta Babu gaira Babu dalili..

Sosai Yan gurin sukasa dariya,Bello yace ainaga alama shiyasa Daga zuwanka garinnan kafara Dukan yaran gari” Aina nasan haka halinka yake da rufdugu zamuma” nan ma dariya akayi kafin Liman yace.
Babu shakka Nasir munji dadin kalamanta akan abokinka Kuma muna fada abinda ka fada ya Zama gaskiya” insha Allahu Nasir yafada kanshi a qasa.

To Malam yakamata mu tafi Ko,,nan suka Tashi suka tafi gidan Malam.
Yakumbo dake zaune nijlah nakan cinyanta tana rigima Taji sallamar Malam,,amsawa yakumbo tayi tana kallan nijlah tace.
Toga malam yazo Naga Yana murmushi ga dukkan alamu yayi samuwa inaga Yau zakici shinkafa da miyar dakiketa mafarki”turo baki nijlah tayi tana kallan Malam kafin ta kurma uban ihu tana cewa.

Wallahi yakumbo Babu abinda yakawo bakiga hannunsa Babu komai ba,,nidai Allah saikin siyamin burodi…
Qarasawa Malam yayi ya cewa kinga Yar albarka Tashi kizo kiji Abu Wani Na tabbata Zakiyi farin ciki kinji Yar gidan kaka..

Maqe kafada tayi tana birgima a qasa,,nan Malam ya Kalli yakumbo yace,,kinga yakumbo dauko tabarma ki shinfida a rumfa ya fada Yana nuna yaloluwar rumfar Kara dake maqale jikin Dakin daba lallai ya wuci damuna ba,,
Shinfida tabarma yakumbo tayi tana cewa Ikon Allah suwa muka Samu,,Malam kodai Yau zakka ta biyo ta gidanmu.
Kedai ki shinfida kafin nayimiki albishir,,nan Malam ya juya Yana cewa ku shigo Daga ciki..


Liman ne a gaba Sai Nasir da Bello tare da sauran mutane dake tayasu murna,,wasu Ko yan uwan mahaifiyar nijlah ne…
Tinda suka shigo yakumbo tabisu da kallo tana mamakin abinda ya kawosu adaidai wannan lokaci Kuma gaba dayansu,,kowanne ta Kalla fuskanshi dauke da annuri,,nan ta zauna Kan buhun dawa tana binsu da kallo..
Kinga yakumbo ruwa Zaki Basu ba wannan kallanba,,gaba daya suka Hada baki gurin cewa ah ah alhamdulillah ta zauna kawai muyi abinda ya kawomu..

Gaisu yakumbo tafara nan Taji suna yimata Allah ya Sanya alkairi” Seda suka gama ta juyo tana kallan Liman tace,,Liman me Kuma ya faru Naji ana yimin addu’a..
Eh yakumbo Yau Dai Allah yayi an daura auren yarinyarki” wacce yarinya Liman??, yakumbo ta tambaya mejin faduwar gaba,, nijlah dake kwance a qasa tana sharar hawaye tayi Shiru tana sauraransu tasan Dai ita dayace yarinyar yakumbo Dan haka ta Maida hankalinta gaba daya Kan Liman tanajin amsar dayake bawa yakumbo..

Yakumbo yarki nijlah,yanzun nan,Bayan idar da salla malam yabada aurenta ga…..Ai nijlah Bata jira Jin wane angon ba ta Tashi da gudu sabida Jin Kunya ya kamata,,Daki ta Shiga ta dauko dakalmin Danko Wanda yasha dinki da zare da allura tasa ta fita da gudu ta Bayan gidan,,kasan cewar gidan bashi da danga Babu Wanda ya Ganta.

Mashkur” zabura yakumbo tayi ta miqe tsaye cikin rashin hankali da dimuwa tace,,badai wannan yaran mashkur ba,da naira hamsin bashi masa wahalan badawa???
Eh shifa Malam ya fada Yana Kallan yadda yakumbo ta haukace ta tubure masa..

To Wallahi Baze taba yiwuwa ba ,Akan me Zaka auran da nijlah ga Bako Wanda bamusan asalinsa ba,hasalina karatun arnane ya kawoshi ruga…

Haba yakumbo be kamata kina fadar hakaba,,kinga Nasir yabamu labarin mashkur bashida Wani matsala ki kwantar da Hankalinki.

Cikin kuka yakumbo tace haba Liman yanzu shikenan nijlah zata tafi ta barni” Bazan iyaba,kugayamasa wallahi ki warware wannan aure aba Dan gari yadda koya na juya zanga marainiya,,Anya Ko Malam ka riqe amanar da danmu yabari,,kaico mutuwa kinyiwa yarinyar shigar sauri,wayyo niya Allah Na,,nan fa yakumbo ta juya tana fillanci Niko nayi zugun tare sauraranta sedai banji abinda take gayaba,,ta jima tana kuka kafin Daga bisani sukayi nasaran shawo hankalinta..
Haba yakumbo meyasa Zaki haka,,kinsan bakisan auren Kika yadda naje naba,,kaga Malam niba aureni Bani so Wanda Kaba auren nijlah Baze taba Zama kusa damu ba nijlah zatayi nesa damu bamusan rayuwar dazatayi ba.

Insha Allahu nijlah zatayi rayuwa me kyau ku kwantar da Hankalinku cewar nasir cike da tausayin yakumbo..

To Amma Dai ba yanzu Ze tafi da itaba ko??eh saimun gama service nan da wata 9 insha Allah” gaskiya yayi wuri yadai Yi hakuri Sai nijlah ta qara wayo nan shekara biyu saiya dauketa,,cewan yakumbo tana hawaye.
Shiru Nasir yayi ganin yadda tsohuwan ta Shiga Wani Hali yace to shikenan,,nan sukayi Mata sallama kowa ya tafi gida..

Nasir da Malam Sai Liman suka tsaya Suna tattaunawa..


Tinda nijlah ta fita da gudu ta Shiga gidan kawayenta tana Kiran su daya Bayan dayan,,bayan sun gama hallara ta fara rawa tana cewa Yau ranar auren nijlah Dan haka kowa ya shirya za’ayi wasa Na kece Raini Yau Yar gidan kaka da Malam zata Hada wasa a dandali..

Yeeeeeeee Yau akwai wasa,,ihu suka sa irin na murna suka sukafara zagaye Dan garin Suna waqa..

*’yan wasa ku fito wasa,Idan baku zoba samarinku suzo Bani Na fadaba angon nijlah ne,,angon nijlah ne me jan baki….*


Haka suka riqa waqa Suna wasa Suna Tara jama’a,,cikin lokaci kalilan nijlah da kawayenta suka cika dandali da jama’a” sosai gurin ya cika yakuma kawatar nan fa dandali me kidan kagane yasaki kalanginsa tare da masu kidan kwarya,,masu Kayan saidawa Suma baa barsu Baya ba sun zo..

Kamar yadda akeyi a kowanne biki haka nijlah da kawayenta sukayi Dan sun cika dandali da jama’a anata wasa irin na Fulani,tare da al”Ada irin ta da..


Liman dake tsaye Suna Magana yace,malam kama kida nakeji a dandali”  eh Liman Nima haka nakeji Kuma Dai yanzu ba lokacin zuwa dandali bane”

Suna cikin haka saiga wasu yammata Suna tafiya,,Malam ne yace ku yara Ina zuwa,, Malam muna wasan bikin nijlah ne,,tafada tana cigaba da tafiya.

Cike da mamaki yace Ina ita nijlah,,tana dandali tabasu amsa ,, murmushi Malam yayi Dan yasan nijlah zata aikata Duba da yadda takesan auren,,a Fili yace yaro yaro ne kajifa Liman bikin aure sukeyi a dandali.

Eh Ai ta birgeni kaga baza’ayi aure irin Na yaseer da fatima ba,,dariya suka sa,,Liman yace Aiko Yau dandali Ze dauki jama’a Nima baza’a barni Abaya ba..
Tinda suka fita aka zo aka Gaya yakumbo nijlah Na dandali,, murmushi yakumbo tayi ta Rasa inda zatasa Kanta,shin me zatayi  farin ciki Ko me..
Ta tabbata Idan tayi baqin ciki ta yiwa Allah butulci Dan haka ta karkata zuwa farin ciki nan itama ta tafi dandali Dan Taya diyar Tata farin ciki..

Bayan tafiyarsu Liman Nasir be bisu dandali ba Dan yace saiyaje ya taho da ango.

Sosai ya riqa sauri harya kai Daki,,nan ya Shiga Yana Kiran mashkur,, mashkur dake zaune Yana Hada Kaya zuciyarsa na quna ya dago jajayen idanunsa ya zuba Nasir.
Dasauri Nasir ya qarasa kusa dashi ,hannunsa ya riqe yace,, mashkur lafiya naganka haka kama Wanda yayi jinya Na wata guda.

Kabari kawai nasir Ina cikin tashin hankali,,ban taba Shiga cikin matsala irin na yanzu ba,,Dana dauki abun da sauqi yanzu Ko magane shayi ruwane,,
Nasir adaidai lokacin da aka dauramin aure Sai gashi a lokacin iyayena da ‘yan uwana sukesan rabani da wannan gari Nasir yaya zanyi..
Haba mashkur Kamar yaya, meyasa Zaka kayawa mummy wannan aure Bayan kasan halin mummy” cikin faduwar gaba mashkur yace.

Ban gayamata ba Nasir kafi kowa sanin yadda mummy take Sona take kaunata,,Na tabbata inda mutuwa zata zo daukana mummy zata Iya fansar Raina da nata” Amma kaga mummy tadau zafi Dani harta Kira manyan yayyena ta gayamusu..

Nasir Bani da yadda zanyi,,yazama Dole a Yau Dinan nabar garin nan indai inasan zaman lafiya.

What! Mashkur me kake nufi,,yaya zakayi da nijlah??

Nasir Zan dauki matata,da ita Zan tafi,,Iya wuya Ina tare da ita..

Niko Nace Kamar yadda muke Kenan lolxx….




Kudaure kuna sharing labarinan, Domin wasu su amfana.


Comments & share.



*Momn sultan ce*✍✍✍

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button