NOVELSUncategorized

NAJEEB 16

Hanne tace kiyi hakuri Baba, bazan iya auren shiba gaskiya, 

Granny salati ta saki, tare da fad’in oh ni aminatu, waike Hanne kanki d’aya kuwa? Maiya sameki haka? 


Hanne kuka ta saki tana fad’in ita bata san wannan auren, kawai a Mai data yola. 

Mum ganin haka yasa tace kiyi shuru, Kinga kina son saka d’anki kuka. 

Zarah kam murmushi takeyi, domin ita d’aya tasan abunda ta k’ulla,”Wanda ko Najeeb bai sani ba.

Granny tace Hanne ko anyi miki wani abu ne? Janta tayi sukai d’akin da sauran matan suke, “suna ganin Granny suka fara gaidata,  tare da k’okarin boye kud’in hannunsu Wanda Granny ta shigo taga suna kirgawa. 

Granny kallonsu ta tsayayi tare da fad’in “wannan kud’in fah? Daka ina suka fito? 

Nan su duka suka fara kame kame tare da sunkuyar dakai, “Granny tace bada ku nake ba? Cikin tsawa. 

Nan Hanne ta Fara bata Labarin abunda ya faru, tare da fad’in koda kanwarshi ta kawo kud’in ta fad’a mana gwara mu amsa ince bana son auren “dama ni ko batace haka ba, wlh baso nake ba, dan Nasan bamu dace ba, “kuka Hanne tasa tana ro’kan Granny akan tayi hakuri ita Kar Ayi wannan auren dan zata cutu  tunda baya Sonta.

Granny shuru tayi,lokaci d’aya ta Fara magana “tare da fad’in ya isa haka, ku kwanta zuwa gobe, insha Allah zamu yola kunji? “suka amsa da Toh ,”Granny fita tayi daka d’akin.

Granny iske Dad tayi a falo shida Mum, daka gani suna jiranta ne, “zama Granny tayi tare da d’aura hannunta akan fuskanta tana d’an bubbuga k’afa alaman ranta a bace yake. 

Dad yace mama lafiya kuwa? 

Tace audullahi d’anka baida mutunci, “tsorata y’ay’an mutane yaje yayi tare da basu kud’i, akan karsu yarda da auran.

Dad yace mama ban gane ba. 

Nan Granny tace dama yaushe zaka gane? 

Yanzu dai abunda za’ayi gobe zanje yola in maida yaran nan, badai auren bane baya so? Sai musa mishi ido ai. 

Dad yace a’ah mama kar Ayi haka, kaman yanda aka tsara hakan za’ayi, goben zamu a d’aura aure, insha Allah, “kaman yanda muka shirya 

Granny tace ai wannan maganan auren babu shi, tunda ita yarinyar tace bata so,  ” ya tsorata 

Dad yace Wlh mama sai an d’aura wannan auren ko baya so, koda kuwa zai mutu,. 

Granny dai shuru tayi tana nazari, can ta tashi Tana fad’in Allah ya kaimu raida lafiya tare dayin cikin d’aki ta kwanta. 

Washe gari da safe tunda sukai sallah asuba suka Kama hanya su duka,” amma banda Najeeb damin bai tashi daka bacci ba, sai dai Mum ta mishi message akan sun tafi yola 

Sai wajan 10 Najeeb ya tashi Kai tsaye toilet ya nufa yayi wanka, tare dayin alwala, sai a lokacin yayi sallah, Bayan ya gama shiri ya d’auko wayarshi sai a sannan yaga sa’kon Mum, wani irin tsaki yaja tare da fad’in mai suke nufi? 

Kenan sunje d’aura aurena kenan? 

Kai ya girgiza tare da fad’in no no baza suyi wannan mistake d’inba, am sure. 

Kawai sunje maida yaranne suba parent d’insu hakuri akan d’auko su da akayi, wannan tunanin da Najeeb yayi shine ya bashi daman cire komai a ranshi, shima daukar jakarshi yayi, yasa a mota driver yaja sukai hotel din da Gina take, baiko shiga ba ya kirata a waya tare da fad’in “come out, “yana fad’in haka ya kashe wayanshi .

Bata jima ba sai gata ta fito d’auke da k’aramin akwatin ta, kai tsaye motar ta shiga Bayan driver yasa mata akwatinta a booth, wani irin peck kiss tama Najeeb akan goshi tare da rungumo shi, tana fad’in oh baby I miss you so much 

Wani irin kallo ya watsa mata Mai kama da kin cika jaraba, yaushe muka rabu,. 

Ganin baice mata komai ba yasa ta k’ara manne shi, shidai driver tuki yake yana Allah wadai da irin wannan rayuwar 

Kai tsaye airport yakai su, inda suka sauka, driver ya d’auko musu akwatin yana ja musu.

Shiko Najeeb da Gina suna manne da juna, kai tsaye Najeeb ya wuce domin ansan pilot ne, ba’a tsaya wani duba kayanshi ba, suka shige cikin jirgi shida Gina, Bayan an gama shiga 11:20 dai dai jirgin ya d’aga zuwa k’asar America.

Su mum sun isa yola, inda suka sauka a wani babban hotel, Kafin gobe su shiga kauyen su Hanne, “koda Abban ibtisam yazo shima a nan ya samesu, ibtisam tasha ko harda ummi za’azo sai taga bada ita bane 

Washe gari da safe suka Kama hanyar kauyen su Hanne, inda sukai tafiyan awa biyu, Kafin suka k’arasa, “kauyen gidana irin na Fulani sai wajajan kiwon su.

Sauke su Granny sukayi a gidan y’an uwanta tare dasu ibtisam, su kuma Su Dad suka nufi wajan sarkin anguwan suka nufa, wanda shine sarkin fulanin gefen wajan, inda aka amshesu cikin mutunci da girmamawa, nan Dad ya fad’ama sarkin abunda ya kawo su,inda yayi na’am ya kuma bu’kaci a kira kawun Hanne. 

Hakan ko akayi aka kira kawunta, inda ya tubure akan Wlh bazai amince da wannan aure ba, domin an mata miji cikin dangi akwai wanda yace zai aureta saboda yaronta zai ri’ke mata shi, yace sarki yanzu Kaga ni gwara muba na gida akan muba na waje.

Sarkin Fulani yace wannan hakane, amma ai suma na gida ne, tunda suna jin fulatanci suda yaransu duk da ba’a nan suke da zama ba, Koba haka ba? Tare da kallon Dad 

Dad yace eh Toh gaskiya nan d’aya, yaron dai bayaji, sai dai mu muna ji 

Nan kawun Hanne yace Toh ku kad’o ne koh? 

Dad yace a’a mu Fulani ne mana, nan ya fad’a musu sunan mahaifinsu, kawun Hanne yace na sanshi mana, inda ban sanshi ba ai bazan bada Hanne a tafi da ita ba can bariki ba. Yace kenan baya jin fulatanci? Shuru yayi Kafin yaci gaba da fad’in. 

kawun Hanne “yace kenan ku rabi da rabi kad’o da Fillo, toh gaskiya bazan yarda ba inba kad’o auren Hanne ba, “Yaje ya kaita shan Bariki ya ajiye ba. 

Sarkin Fulani shima tunda yaji ance yaron baijin fulatanci yaji gaskiya wannan maganan bamai yihuwa bace, dan basa bama kad’o auren y’arsu cikin wannan kauyen, duk da sun San su Dad ba kad’o bane Amma ance yaron nasu baya jin Yaren fulatanci ,

Abban ibtisam yace Amma AI Ina ganin wannan ba matsala bane dan yaron baijin yare….

Sarkin Fulani yace matsala ne babba, mu muna mutunta yaranmu, ku kun tafi Bariki bakwa damuwa da nuna ma y’ay’anku yaransu, “Gaskiya kuyi hakuri bama Hanne ba kaf kauyen nan babu Mai baku auren y’arsu Indai sun San yaron bayajin yaren fulatanci, domin dashi da kad’o babu maraba. 

Babu yanda su Dad basuyi ba, amma suka kafe, tare da fad’in d’ansu kad’o ne, haka suka tashi suka koma inda suka sauke Granny, yaro suka tura akan a fad’a musu sun dawo, “Mum ce ta fito tana fad’in su shigo mana .

Dad yace a’ah basai Sun shiga ba, tace ma Mama ta fito su wuce kawai. 

Komawa Mum tayi ta kira Granny inda ta sami yaran nata a waje, tace lafiya badai har an d’aura auren ba? 

Abban ibtisam yace a’a mama.

Tace toh maiya faru? 

Yace…  Sai kuma yayi shuru 

Tace me inaji ku fad’amin mana? 

Abban ibtisam yace Wai baza suba kad’o auren y’arsu ba. 

Granny tace toh su Waye kad’on Toh? 

Abban ibtisam yace Wai Najeeb tunda baya jin Yaren fulatanci. 

Granny tace amma dai wannan ko yan wulakanci, akan wani dalili zasu kirashi da kad’o? Babu komai zan nema mishi Mata wacce tafi tanan Wlh, bari inyi musu sallama mu Kama hanya, ni naji zaman nan yama isan,”jikan nawa zasu kira da wani kad’o dan wulakanci tsaki taja tare da shiga cikin gidan inda tace su Zarah su taso su wuce tayi musu sallama Bayan ta basu kud’i. 

Mum kam taji dad’in haka Koba komai d’anta yanzu bazai auri wacce baya soba, kuma y’ar kauye ta bakin nashi, “yanzu Abu d’aya zata dage shine ya koma karatun addini tunda ba’a girma da neman ilimi, sai dai Anfi so mutum yayi tun yana yaro, domin lokacin kwakwalwanshi yana saurin d’auke Abu, ba kaman Idan mutum ya girma ba. 

Ibtisam kam ba’kin ciki kaman ya kasheta, “Wlh taso a d’aura ma Najeeb Hanne taga ta tsiya da miskilanci, da mugun hali tsaki taja. 

Granny tace ke dawa kuma wannan tsakin kaman wata tsaka? 

Ibtisam tace Kai granny miye na dangantani da tsaka kuma? “tare da sakin wani tsakin 

Granny tace aikin banza, naga koda tsaka tayi tsaki Allah tsine Mata yayi balle mutum 

Uhm kawai ibtisam tace tare da kawar dakai gefe guda 

Granny ta tsuke baki tace ai inaga keda Najeebu zan had’a Idan Kabiru bai turo ba, dan naga abun nashi wasa ne. 

Zarah tayi caraf tace Wlh kuwa Granny Nima haka nake Fata, kawai a had’asu, Kinga sun dace Sosai 

Ibtisam banza dasu tayi, amma kallo d’aya zaka mata kasan ta cika tayi fam, a kumbure take, domin haushin wannan maganan take har cikin ranta wlh, gashi Mum na cikin motar balle tayi wata magana, dole yasa tayi shuru suke ta fad’a mata magana akan a had’ata da Najeeb 

ita kam mum dariya kawai takeyi.

Tafiya suke har suka k’arasa hotel din da suka sauka, duk a gajiya, Zarah da ibtisam d’aki d’aya, Mum da Dad ma haka, sai Granny ita d’aki daya, sai Abban ibtisam shima d’aki d’aya.

Suna shiga ibtisam toilet tayi domin tayi wanka danta matukar gajiya Sosai, bayan ta fito wayarta ta Fara ruri “Zarah ta mi’ka mata wayan dan yana kusa da ita tace Kabiru na kira. 

Hararanta ibtisam tayi domin tana jin haushinta ita da Granny. 

Amsan wayar tayi tare da dannawa, “Zarah kam dariya tayi tana fad’in ikon Allah. 

Ibtisam na waya ita da kabir, aka fara musu nocking, bud’e kofar akayi inda Granny ta Kutso kai Tana fad’in tare daku zan kwana, bazan iya kwana ni d’aya ba a nan 

Zarah tace Mai yasa Granny? 

Granny tace haka kawai, “ni tsoran wajan nan nakeji “yama kuke cema wajan? 

Zarah tace hotel? 

Granny tace eh zatol.

Zarah dariya, ibtisam dake waya itama Katsewa tayi ta Fara dariya,wai zatol. 

Granny tace miye kuke dariya kaman kun zare? Ko kuma sabbin hauka?.. 

Ibtisam tace Granny miye wani zatol, hotel fa akace. 

Granny ta tsuke baki tana fad’in kunce zatol, Nima haka nace zatol, “Toh miye ba dai dai ba?.. 

Kiran kabir ne ya k’ara shigowa ibtisam ta d’auka. 

Granny aka tabe baki ana fad’in sai waya amma ya’ki fitowa, “lokaci kad’an na baka, koka fito ko in bata wani, bazan iya wannan tsiyar ba, da kashe kasuwa ba, kai bada fitowa ba, ka tarema wasu waje. 

Gashi yanzu anje nema ma miskili aure anki bashi dan bayajin fulatanci, kai wannan rayuwa damai tayi Kama?”yau an nuna min iyakata koda yake suna da gaskiya, Sun nuna muku suna daraja harshen su, amma iyayenku Sun watsar dashi, sun koya muku Yaren aro, Yaren masu jajayen Fata, sai kuma Hausa daba yaranku ba, tsaki taja tana fad’in ai yanzu kwasan darajan yaran naku. 

ita kam Zarah cikin ranta cewa tayi Allah  yaga abunda ya gani sai yasa Najeeb baya ji, inda yana jin fulatanci dayau an d’aura mishi Hanne, “amma a fili sai tace Granny Suma sai basuyi niyan bashi matar bane inda sunyi niya Aida Sun aura mishi ko baya ji, ina ganin yare bashi bane matsala a aure, yanayin kamalan mutum da kuma addininsa. 

Granny taja tsaki tare da fad’in inko kamala za’a duba, babu maiba miskili auren y’arsa, “Yaron da kana fad’a yana fad’a, Allah ya rage ma Aya za’ki dabai iya Hausa ba, inda ya iya Hausa Allah kad’ai yasan irin tsiyar dazai shuka, farin banza da hofi 

Dariya Zarah ta saki tana fad’in Kai granny..

Granny tace eh mana “baki ga saboda ba’kin halinsa ba, har Hanne tace bata son auren, duk da harda ke aka had’a baki, amma ita ta nuna bata sonshi dagaske, miskilin banza dana hofi, “ki ganshi a fili kaman mutumin kirki amma inya tafka tsiya Kya rantse bashi bane, munafiki 

Zarah tace shine munafukin kuma? Masoyin naki? 

Granny tace ai Wlh bai gado mai sunan ba ko kad’an, domin ba haka yake ba, “ke inda Kinga Mai Sunan Aida kince Miskili ba halinsa ya gado ba, domin shi mutum ne mai saukin Kai da sanin darajan d’an Adam, baya raina kowa, “gashi ya iya soyayya kai zamanin mu munsha soyayya Allah yaji qanshi, kai sai kuma ta Fara share kwalla “alaman ta tuna da rayuwarsu tada 

Zarah tace wayyo Granny kiyi hakuri Kinji? Allah yaji qanshi yasa ya huta 

Granny cikin kuka tace Ameen. 

Ibtisam dake waya tace nifa Granny kin isheni gaskiya, ki tashi ki tafi d’akin ki. 

Granny ashar ta kunduma mata tare da fad’in kinci gidanku, y’ar banza. 

Ibtisam dariya ta Fara, “KABIR yace kina tare da Granny ne? 

Tace eh muna tare duk ta ishemu da surutu 

Jin haka yasa Granny Jan tsaki tare da fad’in zanyi maganinki, kanki zan dawo yanzu, “tunda miskili dai baida farin jini anki bashi mata, “Dan bai iya fulatanci ba 

Ibtisam sallama sukai da kabir suka zauna suna fira da Granny, inda Granny take basu shawara akan suyi aure, domin Sun tsufa a gida 

Granny tace Wlh Idan kuka je jami’a kallon y’an iska za’a dinga muku, “kuma a jami’a a nan yara ke lalacewa, baki ga yanda miskili ya koma ba ya fetsare ya koma mara mutunci ba? Ana fad’a yana fad’a, dan banza mara kunya 

Zarah tace Granny, shifa university ba haka yake ba, mutane ne suke mishi wani irin kallo, duk da akwai wanda suke lalacewa a can, amma mu Granny kiyi mana kyakyawan zato. 

Uhmm Granny tace tare da fad’in nidai Ina baku shawara Wlh ku fito da maza kuyi aure tun Kafin lokaci ya k’ure muku ,”domin matan da sukai karatu basu cika samun mijin aure ba 

Ibtisam tace injiwa? Mata nawa sukai aure Bayan sun kammala karatu? Kai Granny waike wake fad’a miki wannan labarin kanzon kurege dinnan ne?.. 

Granny tace uwaki ke fad’amin, “ke bakya ganin abunda ke faruwa ne a duniya? Ai nasan Kun San komai dake wakana, “yarinya zata tai karatu saita gama babu mijin aure, daka wannan yazo ya dauketa sai wancan yazo, in tayi Sa’a ta samu miji Toh sai kuga tsoho ne komai mata.. 

Dariya Zarah ta saki tana fad’in Kai granny wannan sharri haka? “Wanda ya fad’a miki wannan maganan ba gaskiya ya fad’a ba.. 

Ibtisam tace fad’a mata dai.

Tsaki Granny tayi tare da fad’in abunda yake a zahiri, maza yanzu basa son auren y’ar jami’a, domin suna ganin kaman idonta a Waye yake Sosai, kuma haka dinne “yara an turasu wani gari karatu babu Mai kwaba a can AI dole suyi ta tsula tsiya, iya son ransu 

Ibtisam tace Granny ko ina akwai y’an banza akwai na Allah, “karki manta karatun y’a mace yana da matukar muhimmanci,” Kema da kinyi karatu da yanzu tayu kina da ma’kami a gwamnati. 

Dariya Zarah ta saki tace aikuwa, da yanzu hala kina office d’inki zaune, kina sanye da glass kina zuba turanci 

Tsaki Granny taja tana fad’in AI gwara da Banyi ba, “Wlh nidai na fad’a muku ku fito da mazajan aure tun lokaci bai k’ure muku ba, “domin indai kuka tafi jami’a babu aure toh samun mazan aure sai kunji jiki, Inba so kuke ku auri tsoho ba sa’ana ko kuma mai mata biyu ko uku 

Dariya ibtisam tayi tace ai gwara in zauna banyi aure ba, da in auri tsoho ko Mai mata ba, “Kut nifa ban son kishiya Wlh.

Granny tace in bakya so fito da miji tun kan ki tafi jami’a, inko kikai wannan kuskuren damai mata zaki k’are in kinyi Sa’a kenan, in kuma bakiyi ba ki k’are da tsoho Sa’a na, ko wanda ya girmeni mara hakori 

Ibtisam da zarah dariya suke Sosai suna fad’in lallai kam wa yaga mara hakori, “zarah tace Tashin hankali 

Granny tace kuna d’auka wasa nake koh? Shikenan ai 


(function loadPageAds() { return afriPageAds({ ‘pid’: 8612, ‘uid’: 9740, ‘t’: ‘300 by 250’, ‘url’: ‘https://2gnblog.blogspot.com/’ }); }());


Karan wayar zarah yasa ta d’auka tana dariya domin taga Sunan Najeeb ne, tace Bros har ka tafi ne?

Mai yakon ya bata amsa sai yace Maiya kaiku yola? 

Tashi tayi ta fita Tana fad’in Wlh munje akan maganan aurenka ne 

Yace what? 

Tace kwantar da hankalinka bros ba’a d’aura ba. 

Yace what happen? 

Labari ta Fara bashi yanda akayi 

Yace better domin inda an d’aura nan take zan saketa saki uku

Zarah tace uhm 

Kashe wayarshi yayi gaba d’aya danya samu ya kwanta ya huta koda ya kwanta kasa bacci yayi domin ya gaji gashi ya kora Gina data mishi massaging, tunani yai tayi Kala Kala 

Lallai shida ya k’ara zuwa Nigeria saiya dad’e tunda Idan yazo har Dad na biyema wannan old woman din , wai shi za’a d’aura ma widow kuma Mai yaro yar kauye, “murmushi yayi tare da fad’in god forbid, “bazan iya shiga ramin da wani ya shiga ba, kai never, inda wacce zanyi wani abu da itane da sauk’i, amma aure kam never in auri bazawara, ido Ya lumshe lokaci d’aya yana Mai jin zafin abunda akaso mishi, “taya zai auri bazawara wacce ta tabayin aure? 

Murmushi ya saki lokaci d’aya tare da fad’in, I think inna tashi aure bazan fad’a musu ba sai dai suga mata, koda zanyi aure secret marriage zanyi, Danni inna auri mace bazan saketa ba, domin inna rabu da people will say my ex wife, I won’t let that happen, ina da kishin abunda nake so, gwara ace ta mutu akan ace na saketa har a kirata da ex wife d’ina, tsaki yaja tare da fad’in ni bama auren bane a gabana, Indai Mata ne gasu nan like Recharge card everywhere you go, murmushi yayi tare da fad’in na them they rush us, so why will I marry? In ajiye abunda zai daman no bazanyi wani aure ba, ban son takura…..

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button