GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVEL

“Shi..shikenan na rasaki Umaimah na roqeki kada ki manta dani a addu’ar ki idan bazan taba yafewa duk wanda ya rabani dakeba Umaimah nasani kema saboda babu yanda zakiyi ne zaki auri wani amma ki riqe kuma kisa a ranki watarana zaki dawo gareni Umaimah don Allah idan kinje kada ki bari ya tabamin ke idan na tuna abinnan zuciyata neman tarwatsewa take bansan meyasa naqi mutuwa ba….”

Rufe masa baki tayi tana girgiza masa kai tace “bazaka mutu ba Hameed zaka miqe kaci gaba da rayuwa kayi hqr haka Allah ya tsara mana…” ji tayi an janyeta tana juyowa taga Sulaiman ne suka shigo da mahaifinsa da Daddy kuka ta saka me sauti ta fada jikinsa ta qanqameshi tana kuka tace “kayi hqr dani a yanda nake D.S wlh inason sabawa zuciyata dakai amma na kas…” Rufe mata baki yayi yayi murmushi me ciwo yace “kiyi hqr ki daina kukannan banaso inasonki zanyi hqr dake a duk yanda kika zomin kuma zan riqeki amana da zuciya daya nayi alqawarin saina goge miki duk wani namiji dake zuciyarki nazama nikadai ne nake mulkinta”

Yana fadin haka yaja hanunta suka fice ya sata a motarsa Saudat Alfah da Sa’ud suka biyosu ya zage sai goge mata hawaye yakeyi duk da yanda yakejin kishinta a ransa amma ya kasa nuna Mata saboda yasan nunawar qarin shigarta damuwa ne Sa’ud ce ta leqo tace “ango kabamu aron amaryar taka yamma tayi kwalliya zamu” kallonta yayi yace “kuyi gaba zamu biyoku” hakan kuwa akayi shine yakaita har gurin kwalliyar Saida ya shigar da ita har ciki ya sumbaci hanunta yace “ki kulamin da kanki iya yau na baki amanar kanki daga gobene”

Qasa tayi da kanta tana murmushi yayi murmushi yace “yanzu hankalina ya kwanta matata tayimin murmushinta me tsada” juyawa yayi ya fita yana daga Mata hannu ta bishi da kallo tana masa murmushi shima yanayi mata kiss ya jefo mata ta kumayin dariya har haqoranta suka bayyana.

Hakanan akayi musu kwalliyar suka fito suka tafi gda suna zuwa gda motocin daukar amare sukazo 6:30pm suka isa gurin dinner ba tare suka taho ba amma tare suka shiga anatayi musu tafi da ihu suka isa gurin da aka tanada dominsu suka zauna daqyar yasata ta tashi suka shiga filin rawar lkcn da M.C din ya kirasu suka dan taka kadan kai ranar Umaimah taga rashin kunya a gure D.S ko kunyar mahaifiyarsa bayaji da Hajiya da suke gurin kamota yakeyi tako ina suna hotuna itadai hawaye kawai takeyi da ta rasa na meye farin ciki ko baqin ciki basu tashi ba sai sha biyu suna zuwa gda wanka kawai tayi ta kwanta tana kwanciya D.S ya kirata yana fada mata wai yau bazai iya bacci ba duk ta tayar masa da hankali ji yake kamar ya janyo gobe itadai murmushi kawai tayi masa sukaci gaba da hirarsu waishi ya matsu yaji abinda akeji.

Washe gari qarfe goma daidai na safe aka daura auran Dr Sulaiman kabir Yola da Umaimah Ahmad Hameed Shuwa farin ciki gurin Sulaiman baa cewa komai ita kuwa da aka sanar da ita an daura auran kamar yanda Hameed ya suma haka itama ta yanke jiki ta fadi hankalin gdan biki ba qaramin tashi yayi ba shidai Daddy baa gama bikin dashi ba ya dauki dansa suka wucce India ita kuwa amarya Umaimah lbr yana zuwarwa Sulaiman babu kunya ya shigo cikin gdan har dakinta ya shiga ya kuwa yi saa babu kowa ya mayar da qofar ya kulle ta bude idonta a hankali da suka kumbura saboda kuka zama yayi a kusa da ita ya dagota jikinsa yace “ni bantaba ganin aure irin namu ba sweet Ina cikin farin ciki ke kina baqin ciki yakamata ki yarda da qaddara ba duka abinda zuciya takeso take samu ba ki qaddara dama Hameed ba shine mijin da zaki qarasa rayuwa dashi ba wlh Umaimah inasonki kuma zanyi miki komai donki yarda da hakan babu saki a tsarin aurena dake aurene na mutu ka raba”

UMMUH HAIRAN CE… ✍????
[2/1, 1:44 PM] UMMUH HAIRAN CE…✍????: GU

Kuka takeyi sosai tana shigewa jikinsa shima yana qara matseta yanajin ninkin sonta da tausayinta ya yarda so halitta ne duk kyansa da kwarjininsa amma Umaimah kuka takeyi saboda an daura aurenta dashi wasu hawaye masu zaffi suka zubo masa suka diga a dokin wuyanta yace “kiyi hqr Sweet da zan iya halatta miki Hameed dana halatta miki shi saboda nasani shine burinki” saurin dago da kanta tayi tace “wlh ba hakanne yake sani kuka ba tunanin halin da yake ciki shine yafi dagamin hankali D.S aman jini fah yakeyi…”

Rufe mata baki yayi da nasa ya lumshe idonsa a hankali yanajin wani farin ciki na mamayar zuciyarsa yau da Umaimansa zai kwana a hankali ya janye bakinsa daga nata yace “zamu hadu anjima kiyi hqr ki cire komai a ranki ki barwa Allah ikonsa zan tayaki da addu’a Allah ya sassauta miki son mijin daba naki ba kiso mijinki me qaunarki” murmushi yayi mata ya daga Mata hannu yace “mu hadu a matakin qarshe” ya juya ya fice da sauri batasan sanda tayi murmushi ba sanyi Halin Sulaiman yana burgeta a hankali ta daga hanunta tace “Allah ka cusamin son mijina Allah kabani ikon yimasa biyayya Allah kada ka jarabceni da jarabta irin ta gdan Uncle Hameed”

Haka ta yini a kwance tana juyi Saudat Alfah da Sa’ud da Sarah sune suka zama amarorin bikin suna tausayin Umaimah suna tausayawa Sulaiman da irin rawar qafar da yakeyi akan Umaimah dashi aka zage akayi aikin shirya gdan bai iya barin masu decorations din su kadai ba abokansa sai tsiya sukeyi masa wai ba sabon ba wasu suna cewa dashi wai Allah yasa ba auran kisan wuta tayi dashi ba da haka har magrib tayi aunty Jameela Zarah da Hajiya da Hajiya Kaka sune suka sanyata a gaba suna yi mata nasiha akan ta riqe mijinta amana kada ta cutar dashi domin shi da zuciya daya yake sonta kuma ya yarda zai rayu da ita duk da kasancewarsa saurayi sannan yan’uwansa basu nuna mata wani hali na tur ba mahaifiyar mijinta kamar ta goyata tanata godewa Allah daya nuna mata lkcn auran dan nata sama da shekara talatin da uku amma ko zancen budurwa akayi masa sai ya kama fushi da mutane yau gashi shima yayi mata saidai fatan zaman lfy.

Sosai Hajiya tayi mata nasiha me shiga jiki tare da fitowa ta fada mata bazata taba yafe mataba idan tayi qoqarin kashe aurenta saboda Hameed ta sake fada Mata maganganun da mutane sukeyi akan cewa auren kisan wuta tayi amma D.S ya toshe kunnensa yace yaji ya gani.
Haka yan daukar amarya sukazo tana kuka mecin zuciya wai yau ita Umaimah zaa dauka akai gdan wani a sunan mata? Tana tuna haka ta sake rushewa da kuka hakanan uwar mijinta ta ruqota a jikinta tanata bata hqr da sanya mata albarka Hajiya Sa’adatu mahaifiyar Sulaiman cewa tayi dakanta zata daukowa danta amaryarsa aikuwa haka ta sanyata a mota ta kwantar da ita a jikinta tace “kiyi hqr Umaimatu wlh na tayaki murna kin samu miji saidai fatan dorewar zaman lfy bawai yabon kai ba bakuma dan Sulaiman dana bane nasani zakiyi hamdala kiyiwa Allah gdy yayi miki sauyi na alkhairi na jima Ina fadawa Allah yayiwa junior zabi na qwarai kuma na yarda yayi masa”

Da wadannan kalaman motocin sukayi parking sauran mutanen suka firfito suna ta guda gabanta ya sake faduwa Hajiya Sa’adatu ta kama hanunta Aunty Zarah ta kama dayan suka nufi gdan wata waqa me sanyin sauti yana tashi sunan Umaimah ne da Sulaiman yake tashi a cikin waqar haka suka ratsa har cikin parlourn saida Hajiya Sa’adatu tace “kiyi addu’a kafin ki zauna a bakin gadonki cikin aminci” saida tayi addu’ar sannan ta zauna Hajiya Sa’adatu tayi murmushi tace “alhmdllh yau ubana ya angwance Allah na gde maka Allah yasa bani na dauki jikoki na” murmushi Aunty Zarah da Aunty Jameelah sukayi suka amsa da “amin” sannan suka fara zamewa suna guduwa ya rage gdan daga ita sai Sa’ud da Sarah Saudat Alfah mijinta yazo sun tafi tashi sukayi suka fara gyara mata gdan saida suka gama tsaf sannan suka koma haushi da takaici ya cika Sa’ud tace.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button